Kai ya d'aga masa kawai baice komai ba ganin hakan shima sai ya share ya kalli Aliyu da yake wuce yace, "Ya dai bro?." Ji yayi kamar ya make Hydar ganin rainin hankalin da yayi masa, a gaban idanun sa ya kira Asad sarkin su sannan shi kuma ya kalle shi ya ce masa wai bro, k'wafa yayi yana jijjiga kansa dai-dai nan mahaifiyar su ta fito.

"Ya dai triples" ta fad'a tana kallon su ganin haka duk suka mik'e tsaye ta k'araso ta zauna a kan kujera suka zauna a kan carpet ta kalli Aliyu dashi bai zauna ba tace, "Aliyu wai me yake damun ka haka ne?."
"Ranki ya dad'e Asad shine yake damuna, har yana da ikon da zan kira ma'aikata zan saka su aiki ya ce su tafi?, me yake tak'ama dashi wanda bana tak'ama dashi?, ki ja masa kunne har ya harzuk'a ni nayi masa abinda bazai manta ba"

Kallon Asad tayi tace, "Ina ruwan ka da ma'aikatan sa? Asad Aliyu fa yayan kane why zaka dinga masa halaye irin wad'annan kamar ba jini ka ba?, meyasa bakwa shiri ne?." Asad ya kalli Mama yace, "wulak'anta su yake Mama, bana jure ganin ana wulaƙanta na k'asa dani."
"To ina ruwan ka dan na wulak'anta su?, kai na wulak'anta ko wani naka?, kai lallai mai zuciyar tausayi da Imani wa  kafi a cikin mu!?" Aliyu ya fad'a da ihu yana kallon sa.

           Yatsine fuska Asad yake yi ya mayar da idanun sa ya kulle Mama tace, "Aliyu bana son shirme zauna ka daina min shouting a kai na. Wannan halayen naka suna bani mamaki kamar ba jinin sarauta ba." Ba musu ya zauna yana jijjiga kai Mama ta kalli Asad tace, "Ina ruwan ka in ma dafa naman su kazo ka samu yana yi? Ba bayin sa bane?, yana da ikon yi musu duk abinda yake so babu abinda ya shafe ka a ciki, bana son shishshigi Asad dalilin da ya saka bakwa shiri kenan kai da shi."

Asad bai ce komai ba daman kuma itama tasan bazai ce ba tace, "Ku had'a kan ku dan Allah bana son wananan tashin hankalin a tsakanin ku, yadda kuke zaune lafiya da Hydar shima da Aliyun ku zauna lafiya."

Aliyu ya girgiza kai yace, "ki gafarce ni Mama, Ba'a nemi zaman lafiya ba matuk'ar aka bawa Asad mulkin garin nan, Ba'a nemi kwanciyar hankali ba ko kad'an." Mama ta kalle shi a gajiye da magana irin ta tace, "Wai kai Aliyu waye zai baka mulki ne?, baka kwana a gida sai sanda kaga dama, koda yaushe cikin yawon banza kake da shaye-shaye na banza da wofi, a haka za'a baka mulkin ragamar al'uma?. Ka ajjiye wannan tunanin a ranka ka taya d'an uwan ka neman sarauta domin indai yana raye kai baza kayi mulki ba sai shi."

Kallon mahaifiyar tasa yayi da jajayen idanun sa yace, "indai yana raye mahaifiyata tace?."
"Eh indai yana raye baza ka mulki garin nan ba, da ace babu shi ne babu kuma Hydar zan shiga na fita wajan ganin ka zama sarkin garin nan kodan cikar burina, amma kash! Asad ya fika duk wani 'karko da ake nema a wajan wanda za'a bawa mulki dalilin da ya saka mahaifin ku ya furta zai bar masa karagar kenan. Hydar ya fila qualities d'in mulkar garin nan tunda shi rashin lafiya ce kawai kuma sai lokaci zuwa lokaci take tashi kai fa?."

"In kin min izini zanje na kwanta" ya fad'a muryar sa har sark'ewa take sabida bak'in ciki.
"Mu tashi lafiya" ta furta bata kalle shi ba yace, "Godiya nake." Mik'ewa tsaye yayi yana kallon Asad da ba shi yake kallo ba ya lumshe idanun sa kalaman mahaifiyar sa na dawo masa cikin kansa a zuciyar sa sak'a yadda zaiyi da Asad tunda ta furta da dai baya raye ne sai ta san yadda zatayi tabbas zai zama baya rayen kuwa nan kusa, baice komai ba ya girgiza kai ya fita.

Asad ya kalli Maman nasu yace, "in anyi min izini zan tafi na kwanta nima." Da kai tayi masa alama da an bashi ya mik'e sannan ya duk'a yace, "Sai da safe" abinda yace kenan ya mik'e Hydar ma haka suka fita tare.

       Tare suke tafiya Hydar yace, "Deaf bana son mulkin nan ya sub'uce daga hannun ka ya koma hannun Aliyu, babu abinda bro bazai iya ba indai a kan sarautar nan ne." Asad ya sauke numfashi kawai baice komai ya kalli Hydar har zaiyi magana sai kuma ya fasa cewa komai ya d'auke kansa.

Murmushi Hydar yayi yace, "ka koyi magana deaf domin nan da wasu kwanaki kad'an zaka zama shugaban wannan gari ba kuma za'ayi shugaba wanda baya magana ba."
"Hydar ya zanyi?!" Ya furta da wata irin murya da ya sanya Hydar kallon sa har lokacin tafiya suke yi yace,

KWANTAN ƁAUNAWhere stories live. Discover now