“Waira baki taba jin marmarin wani abu da kika rasa ba?”

Da manyan idanuwanta ta kalleshi tana kokarin fahimta tambayarsa, sai ya saka yatsansa ya daki hancinta.

“Taya mutum zai yi marmarin wani abu da da be san da wanzuwarsa ba?”

Ya kallonta yake wannan karon kallon tausayi yake mata, ta tashi babu iyaye kuma tana rayuwa ita kadai kuma tace bata jin marmarin wani da ta rasa ba.

“Baki marmarin zama da iyaye?”

Ta kyalkyale da dariya irin dariyar nan ta yaran da ba su gama sanin ciwon kansu ba.

“Mi zai saka na yi marmarinsu? Bayan ban rayu da su ba? Abun da ka taba kasancewa da shi shi kake marmari ai”

“Zaman da kike ke kadai be taba sakawa kin ji marmarin iyaye da yan'uwa a kusa da ke ba?”

“Ina da yan'uwa ai”

“Su waye?”

Ta saka hannunta cikin gashin kanta ta ciro karamin beranta ta dora a hannu ta nuna masa.

“Gashi tare da zakaru, ina jindadin rayuwata ni”

Ya kawar da kansa.

“Wannan ba jindadin rayuwa ba ne, Waira kin tashi babu iyaye kin ware kanki dabam kina rayuwa tare da abubuwan da ake kebewa, a haka kuma jiran ake ki shekara ashirin a baki sarautar da idan kika haihu zaki mutu ki bar abun da kika haifa, to ina jindadin rayuwa a nan?”

Hannu ta saka ta raba gashin kanta biyu ta saka beran a tsakiya sannan ta mike tsaye ta doshin gurin iccen abaya, Eid na kallonta har ta haye sama tana tsinko ayabar tana jefowa kasa sai da ta gama sannan ta kwanta a saman itacen tana cin wata. Eid na ganin haka ya tashi ya karasa gurin ya daga kansa sama yana kallonta.

“Zo mu tafi gida”

Ta girgiza masa kai alamar aa, yana jin haka ya san ba yanzu zata tafi gidan ba, sai ya juya yayi tafiyarsa, tashi ta yi zaune sai da ta daina hangoshi sannan ta share hawayen da suka cika mata ido. A yau kam Eid ya saka ta marmarin da tunanin abun da bata taba ba, su waye iyayenta wace kalar kulawa za su bata duk bata sani ba, ta ware kanta daga yan'uwanta saboda ta fi jindadin rayuwarta a inda take rayuwa a yanzu. Saukowa ta yi daga kan itacen ta nufi gabar da ruwa ke gudana ta rika bi tana kallon ruwan har ta isa inda mahadarsu take, sai ta taka wani tsauni ta tsaya akai tana hango wani gari da ba ta taba sanin akwai a gurin ba, domin yawonta be tana kawo ta a nan ba, hangaga ta hangame baki tana dariya domin yanayin iskar gurin ma a dabam take.

‘Wannan ba jindadin rayuwa ba ne, Waira kin tashi babu iyaye kin ware kanki dabam kina rayuwa tare da abubuwan da ake kebewa, a haka kuma jiran ake ki shekara ashirin a baki sarautar da idan kika haihu zaki mutu ki bar abun da kika haifa, to ina jindadin rayuwa a nan?’

Maganar Eid ta dawo mata, a ciki babu abun da ya fi tsorata kamar cewar zata haihu ta mutu, kamar yadda mahaifiyarta ta mutu bayan haihuwarta, a duniya babu abun da take tsoro kamar mutuwa, ta zauna a gurin ta sako kafafuwanta kasa tana kallon yadda dacin ya wadatu da ni'imar Allah da albarkarsa.

AMEER POV.

Ya dago yana yi ma sakatarensa wani mugun kallo irin na kaskantaccin mutane.

“Ga file din”

Ya aje masa file din akan Table cike da Ladabi.

“Waya baka inzinin shigo min office?”

With confused sakataren yake kallonsa.

“Na yi knocked kamin na shigo”

“Amman ban maka izinin shigowa ba ai, ko kuma rainin wayo ne ya saka ka fara yim yadda kake so a office dina?”

WANI GARIWhere stories live. Discover now