Ta risinar da kanta kamar yadda ta san na amsawa Shugaba idan yana magana.

“Na gode”

Hannun sarki ya daga mata, sannan ya kalli Eid ya ce.

“Wannan ya zama karo na karshe da zaka rike hannunta a gaban idona”

Shi ma ya amsawa sarki da kai.

“Za'a kiyaye”

Sannan ya saki hannun nata ya juyo ya fito sai ta biyo bayansa, a yanzu kuma fushi take da shi saboda shi ya kawo ta gaban Sarkin, har aka mata gargadi abun da ba a taba yi mata ba, suna fitowa ta sauya hanya ta nufi inda dakinsu yake, tana shiga ta shige dakinta ta kwanta daga bakin kofa tana kallon waje, fuska murtuk babu annuri, zakarun da suke gidan suka taso suka tare a bakin kofar suna kallonta, tana ganin haka ta san abun da suke bukata, sai ta tashi ta bude inda take aje musu abunci ta dauko ta zuba musu su ka ci, ta bude wani karamin rame ta dauko beranta ta dawo bakin kofar ta zauna tana shafa shi, a gurin ta yi ta zama har hudu yayi sannan ta tashi ta koma kan shimfidarta ta kwanta ba tare da ta kunna fitilar aci balbal da ta saba kunnawa ba.
Kamar wata gawa tun da ta kwanta bata farka ba sai da hasken rana ya keto dakin, sannan ta tashi zaune tana murza ido, ta dade a zaune sannan ta tashi ta fita ta yi fitsari, ba musulma bace balle ta san wanke fuska da yin alwala ayi sallah, ba mai tsabta ba ce balle ta san wanke baki da hannu kamin aci wani abu, tana dawowa dakin ta nufi inda ta saba aje ayabar ta sai ta samu an huda ta kasa an ci ayabar an ja wata a zubar, a fusace ta juyo ta kalli beranta dake kwance akan gado yana sharbar bachi ta watsa masa wata uwar harara. Gurin da ta saba aje bulala ta dukan beran da zakarun da suka mata laifi ta nufa ta dauko ta labta masa daya, da gudu ya shige cikin katifar ta kada yana tsuwa kamar wani karamin tsuntsun, haka take a duk lokacin da suka mata laifi sai ta zanesu da bulala haka kuma baya hana anjima ko gobe su sake yin barna. Zaunawa ta yi a gurin ta fara kuka domin fushin da take na jiya ta farka da shi a yau wannan ya saka na ayyana a ranta ba zata fita ko'ina ba balle ace ta yi laifi, gashi bera ya cinye ayabar data aje, ya lalata sauran.

MALEEK POV.

Yana jin lokacin da aka kwankwasa kofar dakin, amman ya kasa amsawa sai juyi yake akan gado gaba daya yau ya farka jikinsa babu dadi kamar wani mai laulayi.
Ya kusan minti talatin saman gadon yana ta juyi sannan ya sauko ya shiga bathroom yayi wanka da ruwan zafi mai zafi sosai wai ko zai jidadin jikinsa ya fito ya shirya kansa sannan ya bude kofar dakin ya fita, kamin ya karasa saukowa ya aikawa mahaifiyarsa da gaisuwa domin baya son karasawa kusa da dinning dinta ma saboda kanensa da suke gurin, a ko wace safiya idan za a karya a tare da juna to ana rabawa ne ita ta yi breakfast dinta tare da yan matanta Twins Nimra da Namra shi da kanensa Mahmood su karya a dinning din Babansu. Can kasan makoshinta ta amsa masa ta kawarda kai daga barin kallonsa ta cigaba da cin abincinta, a yanzu kokari take ta sabawa kanta da sabuwar dabi'ar yaye Maleek a zuciyarta, so take ta saba da halayensa da dabi'unsa so that ta samu peace of mind, ta samu natsuwa ta cire shi da damuwarsa a ranta. Sai da ya fice daga falon ya shiga bangaren mahaifinsa sannnan Nimra ta tashi tsaye ta dauki jakarta dake gefenta.

“Ummi na tafi kar nayi latti”

“To a dawo lafiya”

Hajiya Zahra ta fada ba tare da ta kalleta ba, fuskarta da muryarta suka kasa boye damuwarta, Nimra ta zagaya ta dayan side din mahaifiyarta take ta yi hugging dinta ta sumbanci gefen fuskarta.

“Ummi we love you dan Allah ki daina damuwa”

Ummi ta dago ta kalleshi da murmushi a fuskarka, sai ta ji abun da ke tsaye a tsakanin kirjinta da zuciyarta yana sauka kasa kamar suncewar tayar motar.

“Na gode Allah daya ba ni ku, Allah muku albarka ya ba ku mazaje na gari”

A tare suka hada baki suka amsa da Ameen, sannan Nimra ta fice daga falon tana ta sauri kar ta yi latti.

WANI GARIWhere stories live. Discover now