DAN ISKAN NAMIJI

By feedynbash

47.8K 1.5K 174

Labarine me taba zuciya yadda maza suke zaluntar matansu da yadda iyaye ke lalata rayuwar yaransu sboda abun... More

page 1-2 & 2-3
5-6&7-8
page 9-10&11-12
page 13-14&15-16
page17-18&19-20
21-22&23-24
25-26
25-26&27-28&29-39
31-40
41-50
50-70
Book 2 part 1
part 2
Part 3
part 4
part 5
part 6
page 7
part 8
part 9
part 10
part 11
part 12
part 13
part 14
part 15
part 16
part 18
part 19
part 20
TALLAH! TALLAH! TALLAH!

part 17

839 42 0
By feedynbash

_*👨🏻‍🎤DAN ISKAN NAMIJI👨🏻‍🎤*_

               _*NA*_

_*FAREEDA ABDULLAHI*_
     
       _*(Feedyn Bash)*_

_*BOOK  2*_

_*Faceebook Fareeda Abdullahi Ibrahim*_

_*Whattpad @FeedynBash*_

_*Instragtam Feedyn Bash*_

_*Snapchat Feedyn Bash6660*_

_*E-mail  faridaabdullahiibrahim6660@gmail.com*_

*_🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION_*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation


                   *80-85*

Daddy ya ce "subhahanallah zaka je ka kashe kan ka a baza a wofi akan abun da  ka san gaibu nai ba samu zakai ba, idan ban da baka da hankali tayaya kana auren ya zaka auri kanwa shashasha kawai."

Momy ce ta shigo da sauri ta tallafe shi ta dinga masa fifita har ya samu sa'ida sai da ya lafa yana haki, ya kalli Daddy ya fashe da kuka "tabbas Daddy baka kaunata baka kaunar ganin farin cikina a duniya."

Mikewa yai ya fice daga dakin bai ce komai ba dan gaba daya abun ya gama fice masa arai, mugun tausayin yaransa yakeji a yanzu kawai daurewa yake dan ya nuna masa kuskurensa da abun da ya aikata saboda ya hankalta a gaba.

Hankalinta ya tashi ganin Daddy yai masa banza yama fice, cigaba da rarrashinsa tai tana kwantar masa da hankali a haka bacci ya fara daukarsa ta kamashi ta kai shi dakinsa.

Watan ta biyar a kwance a asibiti duk wani mai imani sai yaiwa Nafeesat kuka ta rame ta jeme sai uban ciki, baci ba sha sai ruwa da ake sa mata masu magunguna alhamdulillah jikin nata yai sauki sosai zuciyarta ce ta kumbura sosai.

Amma ta dan sabe a yau aka mai da ita ainihin dakin da aka kwantar da ita dan bazasu sallameta ba sai lokacinta yayi Edd din ta ya cika sannan zasi mata operations su ciro jaririn saboda bazata iya haihuwa ba a yadda ta ke.

Cikin watan sa bakwai cif a yanzu Maryam ko cikin ta ya kai wata biyar dan tana gidan kanwar Umma saboda mutane sun fara zargin wani abu akanta jikin nata dai alhamdulillah yau tana magana sosai ba laifi.

Bayan ya farka daga baccin ya mike ya dakko takarda da biro ya rubuta mata saki daidai har guda uku saboda sai ya sake ta tabbas zai samu damar auren kanwarta da ta kasance rayuwarsa a halin yanzu, dan wanda yai tunanin rabashi da ita tabbas ya raba shi da duniya nai.

Ya ninke ta ya fito ga bawa driver "ungo ka kai asibitin da matata Nafeesat ta ke ka ce a bata wannan in jini" shi kuma bai kawo komai ba ya hau mota ya tafi yana zuwa su kai kicibus da Abba ya rarrafo ya taho yau saboda yanaso ya duba jikin Nafeesat duk da shi ma sai a hankali.

Suka gaisa ya gaya masa aiken da Arfan yai masa da takkadar gabansa sai da ya yanke ya fadi saboda tashin hankalin ganin takadda, to mai ta kunsa amma ya dake ya amsa yace "bari na shiga na dubata duk da dazu muka dawo da Hajiya jikin nata da sauki ba kamar da ba."

Suka shi ga tare ya dubata tana murmushi ya fito ransa duk a jagule saboda yadda duk ta kare abun tausayi, ba abun da kake gani sai kashi Abba ya zauna suka gaishe shi sannan ya mikawa Mama takardar "karanta mana muji."

Ta karba ta fara warwarewa ta soma karantawa kamar haka.

_Ni Arfan hakika ina tsananin san kanwarki Maryam wadda ta sanadinta na bar duk wasu halayena saboda tsananin san da nake mata wanda rasata daidai ya ke da rasa tawa rayuwar gaba daya a doron duniya, kuma tabbas Nafeesat idan ina auran ki bazan samu damar mallakar muradin raina ba duk da Maryam ta kasance masifa ga rayuwata, ina santa mahaifina na Santa amma tabbas ni zan mallaketa saboda haka na yanke..._

Kasa karasawa tai ta fashe da kuka wanda gaba dayansu jikinsu ya fara rawa, Nafeesat ko jikin ta nai ya fara rawa dan ko bata karasa ba tasan mai takardar ta kunsa cikin kidima ta ce .

"Mama ki sanar dani saki nawa yai mun dan Allah Mama ki sanar dani? innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un! tabbas na san Mama Arfan ya rabu dani bai tsaya a abun da yai mun ba nida kanwata daku iyayena sai ya sakeni.

Ya barni na mutu cikin sittira mana, ya bar ni na mutu da hijabin aure mana, amma ya gaza yimun wannan alafarmar" sai kuma ta shide gaba daya ta fita daga hayyacinta abun da ya daga hankalinsu ke nan.

Cikin kidima aka kirawo likita nan da nan aka shi ga da ita emergency dan dubata, ina haihuwa tazo gadan gadan nan da nan aka ce sai dai ai mata cs bazata iya haihuwa da kan ta ba gaba daya kuka suke dukansu.

Abba kuka yake kamar ransa zai fita yayi nadama mara amfani ta yadda ya fifita kudi akan yaransa, ga shi yanzu abun da san kudin nasa ya haifar masa shi ya sa hannu aka shi ga da ita, anyi nasarar ciro mata diyarta mace mai kama da ita sak amma karama ce dole sai an sata a kwalba.

Amma kuma Allah yai ikonsa akan mahaifiyar inda kafin ma agama ta cika, tashin hankali wanda ba'a sa masa rana wannan ahali suka tsinci kansu a ciki.

Inda Abba ya yanke jiki ya fadi Mama tayi tawakalli hawaye kawai ta ke ita ta koma tana rarrashin Umma, ta ke ta kira Daddy ta sanar masa da abun da ke faruwa a gigice ya sanarwa Momy suka taho asibitin kota kan Arfan basu bi ba.

Suna shi ga asibitin suka kara rikicewa ganin ta akwance sambal kamar kai mata magana ta amsa, Daddy nai ya tsaya yai duk wasu cike cike da suka da ce aka basu gawar saboda ta dade tana jinya a asibitin ya bukaci su wuce da ita gidanta ai mata suttura a can.

Mama ce cikin fushi ta ce "me zata koma tayi a gidan wanda bai san kara ba ko yakanah, wallahi dan ku yayi asara bata da hurumi da wannan gidan tun da ya aiko mata da takaddarta saki uku rigis, wanda yai sanadiyyar rasa rayuwarta ai ya huta ko kuma mun bar shi da Allah."

Jikin Daddy har rawa ya ke saboda tashin hankali "haba Hajiya wasa kike Arfan din da duka yaushe ya fito daga asibitin yana gida ma fa shi ba lafiya" murmushi kawai tai ta mika masa takardar ya karanta fashewa yai da kuka duk dakiya irin ta namiji.

Ya din ga kuka duk sai da jikinsu yai sanyi "tabbas ka haifi da baka haifi halinsa ba, amma dan Allah kuyi mun alfarma idan har mun zama daya a sallaceta a gidana" Umma ce ta ce ba komai su tafi.

Yana kwance a daki yana ta tunani anya ko yaiwa Nafeesat adalci bai kamata ba sam abun da ya aikata, dan yana san kanwarta bai kamata ya rabu da ita ba tun da tana masa tsananin biyayya, bai mata adalci ba tabbas kafin dan aiken ya risketa gwara ya janye dan tabbas yana san Nafeesat amma Maryam fa?

Nata mai sauki nai gwara su rabu da Nafeesat cikin salama, yadda zai Dora mata lefi yadda iyayensu bazasi jayayya wajen bashi auren Maryam ba, da wannan shawarar ya samu karfin gwiywar mikewa ya fice.

Haka ya mike yana layi ya nufi gate ya tarar driver ya dawo ya ke tambayarsa yaya ya kai ya ce eh, cikin tashin hankali ya koma dakin sai kuma yaji fitar su Daddy, yana nan kwance yana karanta wasikar jaki ya kira Maryam missed call bakwai yai mata sannan ta daga.

Fashewa tai da kuka "Arfan ka cuceni ka gama da rayuwata ciki wata biyar na shege ni Maryam? Wallahi ka gama zaluntata saboda wannan abun yar uwata ta ke halin mutuwa da rayuwa, tun ranar data samu labari bata kuma rayuwa mai dadi ba a duniya.

Zabura yai kina nufin dama ba rainon ciki Nafeesat ke ba lalura ce tasa har yanzu bata dawo ba, kina nufin kice ciki ne da ke? alhamdulillah! naji dadi amma zan je duba Nafeesat, nasan kodan cikin jikin ki zan mallake ki cikin ruwan sanyi" "bansani ba munafiki kana nufin bama kasan halin da iyalinka ke ciki ba ke nan, to karka kuma nai ma na dan ni yanzu uwace a gareka dan mahaifinka zan aura" tana kuka ta kashe wayar.

What! ya furta da karfi ta kashe wayar gaba daya ta fashe da kuka duk duniya bata da makiyi kamar Arfan ta tsaneshi tsana mai yawa, tabbas sai ta rama bakin cikin da ya tusa mata ita da iyayenta kodan yaji dacin da suke ji, ba abun da zai hanata auren mahaifinsa sai mutuwa koda ko shi ne aikin da za tai na karshe a duniya.

Shi ko mikewa yai jikinsa na rawa ko gani bayayi sosai yana fita yaga motoci na shigowa har da ambulance, yai mamaki da aka shi go kowa kuka ya ke nan aka dakko gawarta hannunta nai ya leko zoben hannunta ya gani tabbas ita ce ba sai an fada masa ba ta mutu.

Ni ne? ni na kashe ta wallahi! wayyo Allah na! innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un! ya Allah! wani gigitaccen mari Daddy yai masa "kukan me kake? ka kashe ta ka huta sai ka zuba ruwa a kasa kasha, amma inaso ka sani ko mutuwa zakai wallahi bazaka auri Maryam ba ko bayan raina ka aureta ban yafeba.

Gaba daya ya susuce wasu surutai ya ke abun tausayi yana bin gawar har aka shi ga da ita aka ajiye a tsakar gidan dan ai mata sittira, jikin ta ya tafi gadan gadan ana rikishi amma ina rukunkumeta yai, jini sai zuba ya ke da kyar aka bambare shi ji kake yif ya fadi.



*******************


Amarya ta lakadawa Zubaida uban duka da kyar Malam Mato ya kwace ta a hannunta, gaba daya ta hada mata jini da majina Zubaida ta daku shi ya sa yana kwatar ta tai hanyar waje ko mayafi bata dauka ba gidan Kulu ta fada tana haki.

Kuka tasa sai da tai mai isarta sannan ta fara zagin Kulu tana tsine mata, "wallahi Kulu kin cuceni dan duk ke ce kike kara tunzura ni, ga shi yanzu kun mana sanadin mutuwar aurena, wallahi sai naga bayan Haule ko zan yawo tsirara har gida taje ta kashen aure."

Hhhhh! ta sheke da dariya "kin ga shi ke nan dan ni ko ta kyauta mun munyi ragas gaba dayan mu duk mu zauna a haka ba kare bin damo ke babu ni babu ita babu kin ga babun badilahu ke nan."

Cikin tsananin fushi Zubaida ta mike "lallai baki da mutunci dole ki furta haka tun da ke dama ba mijin gareki ba sai yawon na dandi dole mu da mukasan muhimmancin mazajen namu dole hankalinmu ya tashi."

Habawa tuni suka kaure da fada kamar kaji suka din ga tone tone, "ni sai dai ki ce mun uwar tuggu Zubaida amma waya kai ki bin malamai kaf lokon nan ke kika koya mana bin Malamai, kuma dandi ai ba karya bane tun da tsohuwa ma tayi a haka a samo mutum, saboda haka karshen ki nai yazo yanzu."

Habawa kukan kura tayi tai kan ta ta fara jibga ta huce fushin dukan da ta sha akan ta nan suka din ga fada sai da makota suka shi go jin ihu suka rabasu.

Haule ko tana fitowa asibiti ta nufa ta sha wahala kafin a kai ta gunsu yana ganin ta ya hade fuska tamau jikin ta a matukar sanyaye ta shi ga dakin daga shi sai ita yana bare mata ayaba yana bata.

Wani kallo yai mata da wata muguwar harara "nan ma kin biyomu  nai ki karasa kashe ta da abun da ke cikin nata ko yaya? to maza tun kafin na bude idanuwana ki fice daga dakin nan kafin raina ya baci na yanke miki mummunan hukunci dan ko ganin ki bana san yi."

"Haba Malam kayi hakuri mana ko gaisawa ka bari muyi kaji me ya kawota kasan fa tana da hakki ita ma akan ka, yadda nake matarka haka ta ke matarka itama, saboda haka bai kamata kai mata haka ba kayi hakuri ka saurareta kaji uzurinta."

"Wacece matata? ki ma daina wannan maganar kawai gaya miki nai banba amma ai mun dade da rabuwa shi ya sa duk san da kika ce na koma gidanta na kiya, na bar mata gidan nai saboda in rufa mata asiri saboda lalurar data samu, amma yanzu ta warke bana bukatar sake ganin ta kafin mu dawo ki tattara kayan ki koma kauye."

Kuka ta rushe da shi ta durkushe a wajen "dan girman Allah kayi hakuri ka mun rai ka tausayamun wallahi bazan iya komawa kauye ba, kasan ban da kowa ban da komai sai kai ka temakeni ka maida ni dakina dan girman Allah na tuba wallahi, ki sa baki Indo dan Allah ki yafemun kice ya yafemun."

Indo ta din ga lallabashi da kyar ya ce "shi ke nan wallahi kinci darajar farar mace mai farar zuciya baiwar Allah, wallahi da nagama zama da ke" murna ta din ga yi tana ta godiya ga Indo dan ita yanzu taga rayuwa wanda ka yarda da shi dan yaci amanarka ba wani abun wahala ba ne.

Nan ta saki zancen Nauwara amma ya dakatar da ita yama fice tasa kuka ta sanarwa da Indo komai dan dama can ita ce mai bata shawara ta gari kuka tasa saboda tausayin Nauwara hankalinsu ya tashi sosai da sosai.

Bayan wata uku indo ta warke ciki ya kai wata bakwai tuni an sallamesu, kullum cikin bashi hakuri ta ke kan lamarin Nauwara duk da abun na damunsa amma ya da ke, amma yau mummunan mafarkin da yai ne yasa ya mike ya wuce police station dan ya jarraba zuwa gidan basu sani ba, an hana shi shi ga wai ba kowa kuma yana yawan ganin maza ma shi ga gidan, Alhaji Ghali ko har a kasuwa yana ganinsa bayan ganin da ya ke yana fitowa.

Ba bata lokaci suka bashi yan sanda ya debi Malamai yan uwansa suka dau hanyar gidan ta dan tabbas mafarkin da yai Allah zai iya kamashi zuwa yanzu tayi nadama mai matukar yawa.


*To fans mu hadu a next page insha Allah kuma na karshe a wannan chakakiyar,nice taku a kullum a yaushe.*


           *Feedyn Bash*


Pls
Share
Comment
Vote

Continue Reading

You'll Also Like

548K 18.7K 80
Child of the Eldest Gods from the East, Heiress of Earth and Legacy of Stars and Magic, Has the Affinity to Balance the Peace of Nature, Fated Love i...
19.9K 797 12
In the starlit festivities of Penacony, she meets Caelus, a figure shrouded in mystery who shines as a beacon into her enduring night. He was her lig...
170K 5.1K 98
After the death of Gwen Stacy, Peter hadn't had the courage to become a hero again. Meanwhile, the Justice League were looking for a more experience...