_*👨🏻🎤DAN ISKAN NAMIJI👨🏻🎤*_
_*NA*_
_*FAREEDA ABDULLAHI*_
_*(Feedyn Bash)*_
_*BOOK 2*_
_*Faceebook Fareeda Abdullahi Ibrahim*_
_*Whattpad @FeedynBash*_
_*Instragtam Feedyn Bash*_
_*Snapchat Feedyn Bash6660*_
_*E-mail faridaabdullahiibrahim6660@gmail.com*_
*_🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION_*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*Dedicated to: Mrs Ameenullah ina godiya sis Allah yabar zumunci ina jin dadin yadda kike mun comment nagode Allah yabar kauna*
*Nagaya muku so biyu zan dinga posting a sati dan Allah kuyi hakuri kudena yawan damuna private ina wasu books din guda biyu so dan Allah kuyi hakuri fans dana gama daya daga ciki zan dinga yi akan kari*
*Wallahi banjin dadi banyi editing ba idan kunga error kuyi hakuri*
*5-10*
Ummi na shiga gidan ta fara ball da kayan da ta gani a tsakar gida na Laila tadinga zage zage tana kiran Laila ta fito su raba raini
Ta jika wanki ta daga kayan ta shekar a rijiya kayane masu tsada nata dana Lawan zata wanke ta dinga danne dannen ashar
Yaran ma korasu tai makota dan tasha alawa shin sai ta balla Laila yau a gidan gwara su zama saura su biyu a gidan
Jin shiru yasa ta haye sama dakin Laila ba sallama ba komai ta banka kanta dakin
Laila ce kwance a kasa laulayi take me mugun wahalarwa wanki ta jika amma ta kasa
Ko aiki bata jeba yau saboda wahala da cikin ke bata
Kawai ganin ummi tai tsaye akanta sai da hanjin cikin ta ya kada kamar cikin jikinta ze bare
Wuyanta ta damka ta shaketa a kwance ta haye kanta wallahi yau sai na kashe ki akan ki cigaba da zama da lawan
Ke nifa wallahi da kishiyar gida gwara ta waje nan ta fara dukanta ganin haka ta rarumo wata kwalba ta buga mata akanta wani mugun ihu ta saka ta dage wajen
Jini ne yake ta shatata ta kanta da gudu ta fice daga dakin itama ta rarrafa ta rufe kofar tana maida numfashi
Kuka ta rushe da shi wannan wane irin masifa ne wace irin rayuwace miji ba kwanciyar hankali kishiya babu ta kara rushewa da kuka
Lawan ne kwance dai dai a hotel shi da wata beb daya samu ana ce mata Yar gwal yarinyar ta gama tafiya da Lawan dan duk wata lugga ta bariki ta kware akanta
Lawan jiyai sam baze iya barin Yar gwal ba sai da yai sati biyu cif a wajen ta be leka gidan ba saboda gaba daya ya samu dai-dai dashi
Kwana suke suna diban juna bata gajiya itama gashi ta iya maganganun batsa yadda Lawan ke bukata
Gashi tana shan giya sosai shiyasa ta janye hankalinsa kwata kwata wayoyinsa ma a kashe suke yana dai lekawo office shima ba kullum ba kuma a makare ya kuma gudo da wuri ya tare rankata kaf a sabon gari gun karuwa Yar gwal
Laila kuma tana rasan ransa yanaso yasan halin data ciki musamman saboda cikin jikinta baya ganin ta a office anata tambayarsa yana bata da lafiya
Yau ta kama juma'at yau za'a daura auren Lawan da doctor Saudat auren da ba wanda ya sani ko matansa basu sani ba
An daura auren Lawan da saudat auren sirri sukai ba wanda yasan da wannan auren saboda saudat tace bata bukatar zama gidansa hakan ba karamin dadi yai masa ba
Momy kawar Saudat ce tazo tayata murna saboda ita kadai ta yarda tasan tayi aure sai kawarta data rakata gun malamin data kai ta ita ki bama ta kasar gaba daya
Yanzu Saudat kina ganin auren da kikai na sirri ze kai ki tudun muntsira kuwa wace irin rayuwace wannan kika daukarwa kanki
Dakata Momy bansan shishshigi saboda naga baki da surutu kinada amana na bari kika san maganar aurena
Aurena nayi shi ne da zuciya biyu na farko inasan nadau fansar wani cin mutunci da Lawan yai mun a asibiti na biyu kuma inasansa
Saboda haka dole Lawan yabi abunda nakeso saboda dorewar auren mu dashi wallahi sai na gasawa Lawan gyada a hannunsa badai shi Dan iskan namiji ba zan nuna masa shu'uman cin mu na yaya mata
Hmmm baki da wayo wannan ba hanyar daukar fansa bace kibar mutum kawai da halinsa musamman Lawan din nan da kinfi kowa sanin ainihin iskancin sa
Mtsww mubar wannan maganar kinsan har dinki nai masa yau ze fara zuwa yanzu ma me kunshi zata zo da kitso tai min kinsan amarya nake ayau
Bakin ciki kamar ze kashe Momy saboda haushin yadda Saudat tai auren sirri tana ganin abun ze bata matsala a gaba amma ita sam bata tunanin hakan
**************
Buduri ake a gidan Alhaji Ghali na tashin hankali idan kaga yadda maza ke turuwar abun ze baka mamaki musamman yadda ya kasance manyan mutane ne wayanda ake mugun ganin girmansu a garin nan
Nauwara ce ta fito daga bandaki taga mutum a cikin dakinta fuskarsa a rufe ba abunda kake iya gani sai idonsa hannunsa wata sharbebiyar wuka ce
Ihu ta saka ta razana ta juya da gudu zata koma yasa kafa ya hardota jikake dam ta fadi a kan tiles ba karamar faduwa tai ba dan hakoran ta guda biyu sai da suka fita
Jini ya fara ambaliya ta hancin ta ta baki habu na labe sakon wadrobe ya rasa abunda ze dauka ya temaka mata dashi daga gefe ya hango butar jona ruwa dai dai kafarsa
A hankali yadauka shiko ya bita kasan ya haye kanta ya shaketa yana neman hallakata ya daga wukar ze daba mata habu yai kukan kura ya doka masa kettle a kansa
Tuni ya fadi warwas a kasa nan da nan jini ya fara ambaliya ta kunnensa amma saboda karfin hali ya daga wukar da niyyar sokawa Nauwara habu ya kara buga masa kettle akansa shike nan ya mutu a wajen
Nauwara tayi plat a kasa hakora biyu a waje kuka take me sauti tana nadamar auren me kudi datai da talaka ne da tuni tana rayuwarta hankali kwance
Hankalin Habu yai masifar tashi ganin yadda wannan me mask din baya numfashi yana daga mask din abun ya firgita shi saboda babban yaron Baby Chakwai ne yana mugun ji dashi
Duk wani ta'addanci shi yake sawa ha aikata kuma tabbas kashe shin da yai ba karamin barazana bane ga rayuwarsa
Zama yai dabas zaman Yan bori shima ya fashe da kuka saboda tsananin tausayawa rayuwarsa da yake yasan yanzu shi dai sai ta Allah ba abunda ze hana baby Chakwai besa an kashe shi b akan wannan tantirin
Shi kuka Nauwara a hankali ta mike zaune bakin ta na zubar da jini ta kalleshi waye kai meyasa ka temake ni daka bari ya kashe ni na huta
Tayaya zan bari ya kashe ki Nauwara bayan Allah ya jarabceni da kaunar ki tun kallon farko danai miku naji ina masifar kaunar ki ya matso kusa da ita
Yanzu yazami da gawarsa Nauwara meye shawarar ki akan gawar nan kigaya min dan Allah
Ajiyar zuciya ta sauke banda wata shawara banda ita taunani na ya tsaya ta fashe da kuka
Baby Chakwai shagali kawai ake sha burinsa ya cika ze rayu shi kadai da Alhaji Ghali dama burinsu duniya tasan yayi aure tunda har an sheda yayi auren komai ya kare meye amfanin zaman yarinyar a gidan
Yasha giyarsa yayi tatul ya kalli Alhaji Ghali ya sheke da dariya my sweetheart kaje ka fito da waccen jakar ta gyara ragowar dakunan munada bakin kwana tunda munada wadatar waje base sunje ko ina ba
Jikinsa na rawa ya mike ya shiga gidan Dan cika umarnin Babyn sa saboda bayasan abunda ze bata ran baby Chakwai musamman yadda suke kara samun kyautuka daga kasashen duniya na kungiyarsu
Dole ya rike baby Chakwai yarinya Yar yayi wadda kowa keso shi yayi dace duk da ya fara tausayawa kwadayayyiyar yarinyar data nane masa
Alhaji Ghali ne ya shiga babban parlour din a hankali ya karasa bakin dakin nata saboda jin tashin kuka da magana kasa kasa
Ya kasa kunne yaji Habu na fadin yazama dole na kashe idan ban kashe shi ba tabbas keze kashe kiyi hakuri mu nemo mafita kawai
Kofar ya shiga bugawa iya karfinsa fitsari ne ya subucewa Nauwara jikin ta yanata rawa kamar mazari
Ki bude duk abunda kuke fada naji ku bude kashe ni kike son yi ko to wallahi ta Allah ba taki ba kaf danginku dan ubanki yau zaki san nizaki kashe
Tayaya wani ya shigo mun gida wallahi sai na kashe ku dukanku gaba daya Nauwara ta gama firgita ta fice hayyacinta
Ganin haka Habu yai shahada ya mike ya bude kofar shidewa tai ganin ze bude ga gawa yashe a kasa yana zuwa ya murza key daya biyu
Gam kake ji Alhaji ya turo kofar ya damki wuyan Habu shaka bata wasa ba abunda ya gani ne ya sashi sakin Habu ya fadi yaraf shima ya zube wajen
*Kuyi manage da wannan wallahi banida lafiya ne sosai gaskiya bakwa comment rashin comment dinku shine ze hana ni yin dogon typing*