DAN ISKAN NAMIJI

By feedynbash

47.8K 1.5K 174

Labarine me taba zuciya yadda maza suke zaluntar matansu da yadda iyaye ke lalata rayuwar yaransu sboda abun... More

page 1-2 & 2-3
5-6&7-8
page 9-10&11-12
page 13-14&15-16
page17-18&19-20
25-26
25-26&27-28&29-39
31-40
41-50
50-70
Book 2 part 1
part 2
Part 3
part 4
part 5
part 6
page 7
part 8
part 9
part 10
part 11
part 12
part 13
part 14
part 15
part 16
part 17
part 18
part 19
part 20
TALLAH! TALLAH! TALLAH!

21-22&23-24

1.2K 42 0
By feedynbash

[10/3, 4:59 PM] 👯🏻Ummu Subai'a🎭: *👨🏻‍🎤DAN ISKAN NAMIJI👨🏻‍🎤*

               *NA*

*FAREEDA ABDULLAHI*


*_🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION_*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*Wannan page din Sadaukarwane ga latest novellas by samee Ina fatan Allah ya temaki wannan group me albarka inajin dadin kulawarku da comment dinku nagode sosai Allah ya Kara Mana Amana da zaman tare*



*BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM DA SUNAN ALLAH ME RAHMA ME JIN KAI GODIYA TA TABBATA GA ALLAH UBANGIJIN TALIKAI TSIRARA DA AMINCI SU TABBATA GA ANNABI MUHAMMAD SAW*


            21-22



Nafeesat ce ta Fara dawowa ta kawo Masa wayar ta zauna sai ta hango na arfan yafi nata yawa dabara ta fado Mata la Yaya kaga wani news Yana juyawa ta dauke nasa ta maida Masa da nata ta kyalkyale da dariya tsokanarka nake shima dariyar yai nafeesa bakya rabo da zolaya Wai Ina Maryam ne na aiketa kitchen ta yankon kayan fruit be gama rufe Baki ba sai gata Yana cin abinci cin da kyar ganin Maryam Taki sha Amma nafeesat ta shanye sai da tagama ta shanye tasa sannan hankalinsa ya kwanta har wata ajiyar zuciya ya saki lafiya ko dear ba komai sweety ya saki murmushi ya Kama cin abincin haikan ka'in da na'in sai da yaci ya koshi yadda zeji dadin aikin tukun ya daga lemon ya kwankwade


Yana lasar Baki cike da farinciki muntinsa biyar da Gama ci sun koma parlour suna kallo maryam ta shige daki Arfan yafara doka hamma bacci me nauyi ya Kama shi tuni ya Fara gyangyadi ganin haka nafeesat ta Kama shi da kyar Dan har yafara tangadi bacci yake sosai lafiya Wai dear nafeesat bacci kwantar Dani da kyar taja shi dakinsa na kasa ta kwantar da shi tafita taiwa maryama sai da safe Dan itama bacci take ji dama ita gwanar bacci ce suka wuce ta kulle dakin ta kwanta jikinsa Amma Ina kamar gawa kawai bacci yake bema San metake ba ta tabashi taga kawai sakin munshari yake to shi wnn lafiya wnn bacci haka Tai kwanciyar ta


Ita ko maryama ta shiga tashin hankali bala'in Sha'awa ce ta taso Mata gashi Bata San yaza Tai ba kawai namiji take bukata haka tadinga murkususu tana ciwon Mara tana matse cinya Bata saka hannunta ba Sam Dan tasan haramun ne duk tsananin Sha'awar datake ji haka ta daure gumi kawai take ko Ina jikin ta rawa yake take tayiwo alwala ta tada sallah a haka akan daddumar bacci me nauyi ya dauke ta gaba daya ta gama jikewa da gumi jagab Tai ta wasu irin mafarkai gashi Nan arfan Yana binta da gudu sunata gudu chan sai kawai taganshi a gabanta Yana wata dariya bazaki taba tseremun ba ke tawace hhhhhhh haka Tai ta mafarkai sai bayan magriba ta farka duk ta jike da gumi Tai salati ta sanar da ubangiji


Ta shiga Tai wankanta ta dauro alwala tana ta addu'oi Allah ya tsareta daga sharrin arfan Dan Wallahi masifar tsoransa take ita Wallahi tana tausayin yayarta da Allah ya hadata da Dan iskan namiji nafeesat saliha ce itako zata tambayeta garin Yaya suka hadu da wannan mijin nata duk da tana tunanin rabo ne inba haka ba Ina ita Ina shi a haka tafito parlour tana ta tunane tanane taga wayam basa Nan take ta Fara gyara ko Ina na gidan ta kunna turaren wuta wani Ni'imtaccen kamshine ya ziyarci hancinsa Yana tsaka da bacci a hankali ya bude idonsa meya faru dashi a sukwane ya mike


Yaga nafeesat na bacci itama dama ita mayyar bacci ce ta shinta yai nafeesat ya akai na kwanta bacci me nauyi haka ta mutstsike cike da magana irin ta masu bacci wallahi baccine ya dauke ka daga Shan lemo kadinga bacci da kyar na shigo dakai dakin Nan saboda bacci jikinsa har rawa yake garin Yaya Haka tafaru ya furta a ransa biki Sha lemon ki bane na Sha Mana wayo naima nasanja maka da nawa naka yafi yawa na dauke naka sanda nace ka juya dinnan sannan na dauke gyara kwanciyar ta Tai ta cigaba da baccin ta mtsww wani masifar tsaki yaja ya fada bandaki yai wankansa yafito yasha kana Nan Kaya sun Masa kyau ko kallonta beba ya fice Dan ya tsaneta ita ta janyo Masa tafka wannan asara


Yana fita falo sukai ido hudu da Maryam tana kallon wani American film a fox series Banda tabe tabe ba abunda ake itako sai matse matse take ido hudu sukai shibe sauke ba ita Bata janyeba bala'in burgeta yai Dan ba karamin Sha'awa takeba daya akesawa shi hudu yasa Mata Kuma ita bazata taba sabawa mahaliccin taba wannan ma Dan film ne da hanzari ta mike cike da kunya yadda take kallonsa ta kashe tv din ta nufi daki Maryam ya kirata da wani whisky voice sumane kawai batai ba dawo ki kallonki fita zanyi


Ko motsi ta kasa yi Dan yagama kashe Mata jiki da muryarsa ganin Haka ya karasa ta jawota jikinsa ya hadesu gu daya ta kasa ture shi ta kasa Hana shi jikinta ya mutu kawai so take tajita ajikin namiji (hattara iyaye da yammata wallahi akwai wannan kawayar a gaske Wanda da ita ake amfani ake karbewa yammata budurci musamman masu kwadayin cin abun hannun saurayi yakamat iyaye mu hankalta da yammata)ya matseta a jikinsa ya hada bakinsu gu guda yadinga kissing dinta tuni ta sakar Masa jikinta gaba daya duk sunfita daga hayyacinsu motsi yaji alamar nafeesat ta tashi ya tureta ya fice da sauri zubewa tayi a wajen ta saki wani uban Kuka tana ihu baba ka cuceni aure nakeso wallahi da gudu nafeesat ta fito


Guri ya cika an taro yayi taro andaura auren lawan da Laila Amma amarya na gadon asibiti ango Baki kamar gobar auduga abokansa mamaki suke sunzo gulamane kawai bawai daurin aure ba ko a mafarki basiyi tunanin za'a aura Masa Laila ba sai gashi a gabansu aure ya dauru bayan komai ya natsa babanta ya Kira lawan da yake tsaye Yana jiran amarya ta fito shiga kwallon Dan iska ya tsuguna baba gani baba ya Soma bayani kamar Haka alhamdulillah Allah nagodema na sauke nauyin daka doramun na aurar da Laila nauyi dayane ban sauke ba ban zaba Mata mijin da ya Dace da itaba Wanda addini ya tanada


Koda yake kaddara ta Riga fata Allah yayi rabonkace matar mutum kabarinsa Amma lawan ga Amana Nan banine mahaifin Laila ba hhhhhh Aina sani bava cewar lawan Kai yayan babantane to ai kakarta ma data haifi babarta ba'asan ubanta ba ita kanta babarta sai da ta Dan eh ta zazzaga sannan ta auri Dan uwanka aka haifi Laila da kannen ta Dan Haka Banga abun daga hankali ba baba nine daidai da Laila duk Dana San wannan Sirrin Amman na rufa Mata asiri na aureta baba karka manta duk yawon Nan Laila ma nadan zagawa Kuma Yar giyar Nan tadan Sha saboda masifar Sona da kishina Dan Haka baba kabasar kawai nida Laila mutu ka rabane auren zobe mukai baya mutuwa matsalar daga itane fa kishi Ni kima zuciya Dan haka aja mata kunne ta gidama hakuri take Dani


Baba yagama mutuwar zaune Dan baze iya cewa komai ba game da wannan tantirin tunda beji kunyar tarar sa da wannan maganar ba ya tsaya ma bashi amsa shima yazama mahaukacin maganganunsa ba karya Amma a Ina yaji ko Laila tagaya Masa Kai Ina itama batasan da wannan ba Amma wannan yaro Dan iskane yasan da Haka Amma ya dage sai ya aureta gashi an daura itama ta dage baba kadena tunani nibanwa yarku asiri ba hakanake da shiga Rai shiyasa Mata suke mutuwa akaina ya Mike zan koma baba to lawan Ina Laila tana asibiti yai Masa kwatance ya fice shiko mutuwat zaune yai be Kara magana ba


Yana fita sukai asibitin shida abokansa tana kwance fuska yai zindim nad da bandage yadanji tausayinta besan Haka yai mata ba ya rungumeta yadinga lailayata abokan suka tafi suka barsu sai murna take Yan gidansu ko sai sha'awa suke Basu ba Wanda yasan meya wakana sai baba shiko tausayin Laila yakeji tanada biyayya ga kyauta Allah ya jarabceta da Dan iskan namiji sai yamma ya tafi zeje gida ya dawo a asibitin ze kwana da ita Dan soyayyace ake yinta a ranar Bata wasaba saika rantse da Allah lawan ki tsawa baze iyayiwa Laila ba tsabar kulawa(Allah karabamu da Dan iskan namiji me Hali irin na lawan zulwajihaini wallahi akwaisu life irinsu)


Ya ja motarsa sai gida ba kowa a gidan kowa ya tafi sai yaransa sai ummi data gama cika Tai Dan ta hada kayanta komai a gefe shi kawai take jira Taji dirin motarsa sai gashi ya shigo Yana zukar sigarinsa Yana dariya mezan gani ummi yaji Zaki sai kin jirani ai Naga inza ai yaji ba'a sallama da Miji ranta ya gama baci eh dama saboda danka bansan nabarshi yai ta garari shi kadai a waje hehehehe Ashe Ana Sona tunda anasan jinina mtswww Allah sittiri bukwi mezan da Dan giya manemun Mata Dan iska irinka ransa ya baci nikike gayawa Haka Dan Kinga Ina kyaleki agidannan darajar yayanmu nafada banza Dan iska gadan gadan ya nufeta itama da zafin zuciya Taki gudu ya shaketa



*To my fans inje ruwan comment kawai kuji ruwan typing nice taku akoda yaushe uwargida a gidan bash*

  

          *Feedyn bash*
[10/3, 4:59 PM] 👯🏻Ummu Subai'a🎭: *👨🏻‍🎤DAN ISKAN NAMIJI👨🏻‍🎤*

               *NA*

*FAREEDA ABDULLAHI*


*_🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION_*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''

https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*ASSALAMUALAIKUM WANNAN PAGE DIN SADAUKARWANE AGAREKI MUMMY ILHAM YADDA KIKE KAUNAR WANNAN BOOK DIN DAMA DUKA BOOK DINA NAGODE ALLAH YABAR ZUMAUNCI YA BARA KAUNA KIYI YADDA KIKESO DASHI NAKINE KE KADAI INKISO KIHANA KOWA KARANTAWA😉😉😉😉*


*BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM DA SUNAN ALLAH ME RAHMA ME JIN KAI GODIYA TA TABBATA GA ALLAH UBANGIJIN TALIKAI*


         23-24


Dan ubanki nine Dan iska ya shaketa dakyar take fitar da numfashi yayan sai kuka suke suna ture uban daga jikin ta sai dayaga tadena numfashi ya saketa a kufule ya shige dakinsa ya kunna sigari ya dinga dankarawa cikinsa Amma batai Masa ba tuni yafara Mirza wiwi da hanzari ya Fara zuka cikin gwanan cewa sai sannan ya Fara jinsa ya koma normal wallahi bazan dau iskanci ba data fada rijiyar ubanwa ya cirota mtsww yaja tsaki


Ummi ko tuni idonta ya firfito waje numfashinta ya dauke Dan ba karamar Shaka yai Mata ba cikin ikon Allah babbar me suna Zahra tayi dabarar debo ruwa sunata zuba Mata Banda kuka ba abunda ragowar sukeyi cikin ikon Allah ta farfado dakyar ta mike ta rungume yaran tana kuka suma suna ta kuka tabbas tayi kuskure sone taja Mata aikata wannan kuskuren shiyasa annabi yace kunemawa Yaya yenku uba nagari ita yanzu mezata dorar a rayuwarta da lawan najin Dadi sai dai soyayya kawai


Haka ta wuni kuka ta Debi kayansu ta maida daki dama kawai barazana Tai Masa ashe rabon taci dukane bayan rijiyar data fada akansa Amma ko akikinsa itama Kuma aranta batajin zata sauke wannan kishin datasawa kanta andai daura aure sai tariya taga shegiyar dazata shigo Mata gida wallahi ba wadda zata shigo gidannan a matsayin kishiya gidan tane ita kadai Dan ita lawan yai wannan gidan


Ita fa wallahi da kishiyar gida gwara ta waje tunda Bata ganiba batasan da zamanta ba Amma wallahi zata nuna Masa ta fishi hauka wallahi sai ta bargidan Bata Isa tazauna Mata a gida ba tana Nan tana zuba idon ganin ranar daza a shigo Mata da amarya haka ta dinga saka da warwara a kwance Dan zazzabi ne me zafin gaske ya rufeta tanajin sanda lawan ya fito ya fice koya lekasu kuka ta saki me ciwo


An kawo kudin auren nauwara million 1 an kawo lefe akwati ashirin da hudu da mukullin dankareriyar mota kawunta zaucewa ya kusayi Shiba siyar musu da ya zeyi ba sukayi dariya ai su burinsu alhaji ghali yai aure Kuma wnn ba komai bane cikin dukiyar alhaji ghali matar daze aurace kome yai Mata Basu Fadi ba Nan suka ishe shi da dadin Baki aka tsaida Rana sati biyu dama kayan lefen suna cikin motar tata sun Gama tsara komai da nauwara da alhaji ghali komai na gida yace baya bukata akwai komai


Suna tafiya kawu yasa aka kirawo Masa dansa ya shiga gaba yaja motar bayan da boot din shake da akwatuna wasu kan wasu sai kofar mazugal gidansu nauwara sunayin parking yasa aka Kira masa Yara suka dinga jidar lefen suna kaiwa gidan tun suna mamaki har suka tsaya suka zubawa sarautar Allah ido kawune ya shigo ya Mika musu mukullin motar da zunzurutun kudi naira million guda kudin auren nauwara Wanda tunda suke a duniya Basu taba ganin kudi irin haka ba


A take umman ta ta sume itako kuka tasa na farinciki da tsoro Anya ko bataiwa kanta zari ba Bata Kai kanta inda zata halaka ba kuka take wiwi ta debo ruwa ta zubawa umman tata malam ya fito ya kalli kayan gabansa Banda faduwa ba abunda yakeyi wannan tsabar dukiya a gidansa sunan kayan auren diyarsa da wane ido ze kalli mutane ta tabbata ya seda yarsa kawu ne yace to malam ga kayan auren diyarmu da kudin auren ta million guda da mukullin mota har laude since ingaya ma Ba'a bukatar komai na kayan daki Dan haka sun yafe


Malam ransa ya gama baci jijiyoyin kansa sun tashi sunyi rada rada kawu wallahi bazanyi kaffara ba ba hannuna a wannan auren suyi duk yadda sukeso Amma duk abunda ya biyo baya wallahi ba ruwana tunda yata tagaza yimun biyayya Yana matsar kwalla su kwashe kayansu su fice mun daga gida ke Kuma bakin cikin da Kika sani a bakin da hanzari kawu ya toshe Masa Baki haba bansanka da irin Haka ba kafa sawa abun albarka wallahi na janye banyi tunanin abun ya Kai Haka ba yaya dama Kai ka karbi auren Nan duk abunda ya biyo baya su nemeka


Kawu ya rike hannunsa suka fita yanata rarrashin sa yace ya janye sakin dama be furtaba su zauna a gidan Amma baruwan shi da sabgar auren su shima yanada tasa sabgar shikansa habu Dan gidan malam ya girgiza da ganin dukiyar shikansa yaso nauwara Amma yasan tafi karfinsa Haka suka fito suna maida yadda akayi umma ta Basu dubu dari da kyar kawu ya karba Yana fitowa yabawa malam Dan Yana tausaya Masa shi yanada Yaya maza manya suna wahalta Masa duk abunda ya samu na Dan uwansane dama ya bashi ungo wannan Nina baka ka Kara


Da kyar ya karba yaji dadin kudin ya rakasu suka hau adaidaita sahu ya dawo gida Kai tsaye ya tura a kira Masa maimuna ya zauna a soron gidansu mahaifinta dama ya rasu da hanzari tazo ta bude masa dakin zaure na mahaifinta bayan ta gaisheshi ta kawo Masa ruwa me sanyi a kwanan Sha na randa gabanta sai faduwa yake tana mamakin meya kawo malam bayan betaba zuwa gidan ba da sunan yanso yaganta sai dai ya aiko musu da kayan bukatun yau da kullum kamar yadda Saba baya gajiya a Koda yaushe bayan yasha ruwa yai gyaran murya


Maimunatu ba komai bane yasa nace Inasan ganinki sai wata alfarma danake nema a wajenki nasan kindauke Ni tamkar mahaifinki Dan Haka nakeso ki temakeni ki rufan asiri kicika mun burina Wanda Yar Dana Haifa ta kasa cikamun tabi rudin duniya da zugar uwarta gabanta sai faduwa yake malam ya sharce kwallar idonsa ya Bata Labarin duk abunda yake faruwa na auren nauwara da alhaji ghali gabantane ya yanke Fadi lallai nauwara Maci amanace kamar saukar aradu taji malam Yana cewa kitemakeni ki yarda na daura aurenki da Bello ranar daurin auren nauwara a hada gaba daya wani zaro ido tayi



Wash hannu na ya gaji da typing fans Kuyi manage yanzu Labarin ya Soma labarine me cike da tarun darussa nice taku a kullum a Koda yaushe yawan comment yawan typing


              *Feedyn bash*

Continue Reading

You'll Also Like

43K 2.1K 75
What if it wasn't Japan that teleported to another world, but the superpower country on Earth, America's Cold War rival that in our OTL is collapsed...
535K 13.3K 42
Psycho brothers and a little angel sister sounds not so good together right? so what happens when an sweet angel comes live with her lovesick pyscho...
506K 15K 38
MALE WEDNESDAY X READER "I love you...Wednesday Addams" The girl cried while hugging him as tight as she could. "I love you too....Amore mio. Please...
26.7K 655 114
النوع: شونين اي ، مأنها ، كوميديا ، دراما ، الحياه المدرسيه العمل: مستمر -القصه- "يوما يحكى قصه مرحه عن الحياة...