KOWA YA GA ZABUWA...

By Gureenjo6763

13.8K 1K 46

Rayuwa wani abu ne da kan zo mana da kalubale iri iri, wani muna iya fin karfinshi da taimakon Allah wani ko... More

Page 1
Page 2
Page 3
Page 4
Page 5
Page 6
Page 7
Page 8
Page 9
Page 10
Page 11
Page 12
Page 13
Page 14
Page 15
Page 16
Page 17
Page 18
Page 19
Page 20
Page 21
Part 22
Part 23
Page 24
Page 25
Page 26
Page 27
Page 28
Page 29
Page 30
Page 31
Page 32
Page 33
Page 34
Page 35
Page 36
Page 37
Page 38
Page 39
Page 40
Page 42
Page 43
Page 44
Page 45
Page 46
Page 47

Page 41

303 22 0
By Gureenjo6763

KOWA YA GA ZABUWA...
   (DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.            
         (Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

FOLLOW ME ON Wattpad @Gureenjoh6763

AND ON AREWA BOOKS @gureenjo

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
And Now
*Kowa Ya ga zabuwa..*

                      *PAGE 41*

*FREE BOOK*

*Sorry! Jiya bamu da wuta wayana ya mutu kan wuta ya dawo kuma na wuce Garinmu a bacci! Yauwa I want to talk about ghost readers, kun ganku? Babu na gode, babu comments se an kwana biyu ba'a ganka ba se kaga ana cewa "wacce kam shiru!" "Yau babu kowa yaga zabuwa" ko kuma masu cewa "continue" Abeg ku duba wahalar da mutum yake sha wurin wasa kwakwalwa, data, hannu da idanu wurin faranta muku ku faranta mishi kuma... Typing is not a joke I repeat ba wasa bane wlh! Allah yasa mu dace***

Wuta sossai ya tashi a gidan ba tare da na sani ba saboda baccina ba na lafiya ba, wata ce ta zo ta tada ni karfi da yaji ta Jani muka hau gudu muka fita daga gidan kaman yadda sauran jama'ar gidan kowa yayi ta kanshi yayinda wasu daga ciki suka ƙone kurmus ciki harda magajiya, dab asuba kowa ya kama gabanshi haka nima na nausa nayi ta tafiya ban damu da dubun dare ba banda jakana da nake rungume dashi ba dare ba rana ko takalmi babu kafafuna.

Karnuka sede su min haushi su gaji su wuce amma ko ta kansu bana bi bare in tuna wani abu wai shi tsoro, jikin wani gida na samu na zube a wurin saboda gajiya da nayi ga bacci ina ji, pillow nayi da jakana na hau bacci a wurin Dukda uban sauro dake yawo a unguwar.

"Baiwar Allah! Baiwar Allah!!"
Wata murya ke ta ambaton hakan har Seda na fara buɗe idanuna ina lumshewa, ganin garin yayi shaaaa Dukda be zama haske tangararam ba hakan yasa nake iya kallon kamilalliyar fuskanshi yace.

"Me kike yi anan haka da tsohon ciki? Na fita zan je masallaci na ganki har kuma na dawo baki tashi ba! Baki tsoron sauro ya illatar dake da abunda ke cikinki?"
Ban amsa ba se Kallonshi kawai da nake, chan na iya buɗe baki kaman an fusgo maganan nace
"ru....wa"

Yace
"tashi! Tashi mu shiga gida se in baki kisha"

Da kyar na iya mikewa sbd nauyin jiki da ciwon kafafu, haka muka shiga gidan nashi tun fitowa ta shine mutum na farko da ya tausayamin har ya taimake ni ba tare da ya san ko ni wacece ko daga ina nake ba!

Mutum ne me matsakaicin karfi don baza'a kirashi me kuɗi ba, gida ne daidai na rufin asiri, sallama yayi cikin babban sashen.

Wata mata ta fito tana kallonmu ɗaya bayan daya, yace
"Umman khausar ga bakuwa nan don Allah kaita extra room ɗin nan ki bata ruwa in akwai wani abu a gidan ki bata kan a gama abin kari!"

Kallon tara saura kwata take mana daga ni har shi seda ta gama kare mana kallo kan tace
"amma Abban Yusuf ka ma raina min wayau, haka kawai ka shigo min da mace da tsohon ciki rimi rimi ka wani ce in bata extra ɗaki da abinci? Ina ka samo ta da sassafen nan?"

Yace
"tsaya tukuna Amina gidanki ne nan kam ko gidana? Taya zan ce ga abunda za kiyi kice ba haka ba matar nan tana tsaye tana jin jiki?"

Dariya tayi ta tafa hannu tace
"Aaaa lallai ni dayake ba ciki ne jikina ba a kwance nake ina jin daaɗi, taya zaka fara fifita wata kaina? Kab zuri'arku ban san me kama da aljannu ba bare in ce daga dangi take.."

Juyawa yayi ya kalleni yace
"zo mu je baiwar Allah"

Juyawa muka yi zamu bar wurin tayi wani tsalle ta sha gabanmu ko damuwa da cikinta da ya ɗan fara fitowa bata yi ba tace
"Ina Zaku je? Wai me kake nufi ne?"

Hannu ya sa ya matsar da ita yace
"wuce baiwar Allah"

Na wuce ya biyo ni zuwa karamin sashen dake daga gaban wannan ɗin, da sauri ta kuma shan gabanmu tace
"ɗakin ka zaka kai ta?"

Yace
"eh tunda nan kam ba naki bane baki da hurumin hanani ko yi mini iko"

Bori sossai tayi tayi wadda wasu ba zan iya tunawa ba akan kilan cikin ma nashi ne dangina suka koro ni na dawo mishi da abunshi in ba haka ba ina ze sameni da sassafen nan, babban damuwarta kankantar shekaru da kyau na Dukda sossai ya ɓuya sbd wahala.

Daga karshe ganin da gaske sashen shi ze ajiyeni tace ta hakura in zauna sashen ta, haka muka koma ta bani extra room, be barni ba seda ya tabbatar na ci abinci nayi sallah, ina gabamawa nayi pillow da jakana as usual na hau bacci.

Dukda kasancewar Amina mace ƴar uwata sede ko sau ɗaya bata taɓa jin tausayina ba a zamana da ita Dukda taga banda cikakken lafiya da hankali, bayin ta babu pampo se wurin wanke wanke, da safe zata saka ni diban ruwa in cika mata randunan bayi, in yi wanke wanke kan ta bani abin karyawa, abincin rana wani lokacin se yamma idan Alhj ya dawo mutum me tsananin mutumci da karamci ze ɗauki nashi ya bani Dukda barazana da matarshi ke mishi a kaina iri iri.

Na zauna na tsawon sati uku a gidan bana yiwa Kowa magana tun ruwa da nace ina so ban sake cewa kowa tak ba, da dare Alhj ya kan zauna ya tambayi suna na, mijina, garin da na fito ko wasu en uwana amma babu abunda nake iya ce mishi ko nake tunawa.

Wata rana na tashi da nakuda bayan na ɗibi ruwa ina a na karshe cikina da bayana suka riƙe sossai, ban iya karasawa ba bokitin ya faɗi nan tsakiyar parlor ya jike Mata ɗaki, wani irin bangaza tayi mini ta hau zagi na babu irin sunan cin mutuncin da bata kirani ba har marina Seda tayi akan se na gayamata gaskiya mijinta ne uban ciki na?

Ina fama da wahalar nakuda hakan yasa duk abunda take yi ɗin ban ma san tana yi ba, ta saka ni na share mata ruwan da na zubar ina cije baki da komai a tsugune na yi aikin ban iya komawa ɗaki ba nan tsakar ranan na faɗi ina shan azaba, matar nan bata fito ba bare ta kulani na fi awa uku a wurin har jini da ruwa suka fara bin kafafuna ga rana ana yi na jike sharkaf da zufa, da taimakon Allah Allah ya turo Alhj Dukda yaranta na nan suna kai kawo sede kallo babu wacce tayi min.

Hankali tashe ya kirata ta zo ta taimaka min mu tafi asibiti tace ba da ita ba, lokacin da aka yi abunda aka yi ba'a gayyace ta ba se yanzu, haka ya taimaka min sbd babu yadda ze yi muka je mota ya kaini asibiti, da kyar suka karɓe ni seda suka yi faɗa sossai akan rashin kulawa da sakaci da aka yi gashi ba wurinsu nake zuwa awo ba.

Bayan baƙar wuyan da nasha na haifo yarinya mace, ina haifanta kuma na fara wani kalar bacci kaman wacce ta bugu, su suka mata komai har nono suka bata ba tare da na sani ba.

Se washegari da yamma bayan sun gama bincikensu suka bani sallama, tunda na farka kuma se hauka na muraran ya bayyana, ba zan ce na riƙe yarinyar ba sbd Alhj tsoron bani ita yake kar na yarda ta.

Muna dawowa Amina ta sake tada sabon bore, Seda suka kai ruwa rana kan na shiga ɗakin da suka saukeni, da farkon dare ya kawo min yarinyar yace
"Baiwar Allah ya kamata kiyi magana ko sunanki ne mu sani! Babu daaɗi yadda Amina take adressing naki da sunaye marar kyau"

Kallonshi nayi kaman zan ce wani abu se nace
"Aisha! Aisha!!"
Ina ta maimaitawa Seda ya gaji yace
"sunanki Aisha?"

Kai na gyaɗa yace
"daga ina?"

Ban yi magana ba se jaka na buɗe na fiddo box na miƙa mai nayi murmushi, karɓa yayi yana Juyawa kan ya ɗago nayi bacci fita da yarinyar da ko kukanta ni ba zan ce ga yadda yake ba yayi, madara ya sa aka sayo mai ya bata a tare suka kwana.

Karfe Taran dare naji ana tashina, ɗago kai nayi na kalli Amina ta zaro min idanu tace
"tashi tsohuwar munafuka ki fitar min daga gida.. Ai nayi kokari tunda kika yi sama da sati uku"

Mikewa nayi a tsorace na rarumo jakana na rungume, fisgewa tayi tana cewa
"uwar menene ciki da kike mammaƙeta haka?"

Zazzagewa tayi zobuna na suka zubo waenda suke gwal ne masu kuɗi a lokacin guda biyu, ɗauka tayi tana Juyawa ta kalleni tace
"kam bala'i!! Wato Alhj ya iya saya miki gwal kina karuwarsa ni matar gida be sayawa ba?"

Girgiza kai nake ba tare da nace komai ba, mari ta sauke min tace in zo in fitar mata daga gida kan ta kulle idanu ta buɗe zobunan kuma wlh bazata bani ba tunda da kuɗin mijinta aka saya.

Kuka nake son yi ta fincikoni tare da toshe min baki ta ja ni har wajen gate ta cilla ni na faɗi har Seda goshina ya fashe da dutse, raina ne ya ɓaci ban sani ba ko aljannun da aka Haɗa ni dasu ne ko yaya kawai ina mikewa na dau hanya ba tare da ko waiwaye ba.

Seda nayi tafiyar da ban san na awa nawa ba gari dae yayi shiru kan na iso wani rumfa inda buzaye suke zube sun hura wuta, anan na shiga cikinsu na kwanta basu ganni ba seda safe, sun tsorata macen ta tashe ni, ina farkawa mijin yace kar kowa ya min magana, wasu Adu'a ya dinga yi min kan yace
"Baiwar Allah!"

Na kalleshi sede ban yi magana ba, yace
"hoo innalillahi wainna ilahi rajiun duniya ina zaki damu jama'a? Laure wannan mata na shikin masifa tana matukar bukatar taimako"

Matar tace
"to me gida ba se ayi wani abu ba?"

Yace
"yo ai ba ze yiwu anan ba duk abubuwan suna chan gida gashi kudu muka nufa"

Tana kallona cikin tausayawa tace
"kayi hakuri mu koma Nijar me gida! Wannan baiwar Allah duk inda danginta suke na tabbatar suna shikin tashin hankali"

Haka gamji da matarshi Laure suka fasa wannan tafiya suka tafi dani Nijar, na sha wahala sossai wurin adapting rayuwarsu, nayi jinya me yawa wadda har na kan yi wata ba tare da na san inda kaina yake ba, abun ya zo ya fi karfin Gamji Seda ya Haɗa da neman taimako a wasu nahiyar na Nijar.

Tsawon shekarun ashirin ina fama da jinya don se haukan yayi kaman yayi sauƙi se kuma ya taso, na samu lafiya shekaru uku baya inda komai ban manta ba, na basu labarina gabaɗaya saboda sun zama kaman yayyina sun riƙe ni da amana matuka, basu taɓa saka lomar wani abu a bakinsu ba tare da na saka ba, ko da suka ji labarina wadda ina zuwa wurin barin jinjirata da ba zan iya tuna fuskanta ba se kuka da firgici su rufe ni, ta ina zan fara neman ta? Kuma ta yaya? Wlh ko sunan Wannan bawan Allah da ya taimakeni ban sani ba bare unguwar da yake a birnin Kano.

Mun kara delay na shekara uku kan mu zo ne sbd tsananin rayuwa da gamji yake ciki ya sayar da duk dabobbin shi wasu yayi asarar su duk ta hanyar neman min lafiya don aljannun sun sha kashe mishi garke gabaɗaya sbd ni akan ana mishi gargadi ya Rabu da ni da rayuwata babu ruwanshi.

Da muka samu kuɗin suka taru kuma fita ƙasar Nijar ya gagareni seda muka yi ta biyan wasu kudade kan muka iya fitowa, mun kwana Kano kan muka nausa Gembu seda muka samu kab labarin abunda yake faruwa gidan Buba kan muka nemi layin mama, matarshi Badi'ah ta bamu shine muka kira, ko da muka iso Kano da neman taimako muka samu me adaidaitan da ya ɗauko mu zuwa wannan gida don ko biyar bamu tsira dashi ba kuma..."

Shiru tayi tana share hawayen fuskanta, tana me cigaba da shafa kan Hidayat da take ta kuka har da majina, Abbanta da ya hamza ma kuka suke yi duk dauriya irin ta maza, sossai jikkunansu yayi sanyi babu wadda ya iya magana se muryar Hajiya Balaraba suka ji ta fara cewa

"Hahahahahhaha ba kin dawo ba! Dama ya faɗa kina dawowa se na haukace ai kaikayi koma kan mashekiya ne! Aisha ke azzaluma ce, ina zaman zamana da mijina tun kan yayi kuɗi har yayi arziki shine ya tsallake ya auro ƴar gembu waenda ba inda labarin kyaunsu be je ba! Yana so ni balaraba in zama bora ya sa kyakkyawa gaban mota Hahahahahhaha"

Ta sosa kai ta sake gyara zama kan tace
"ni ce nan na je wurin neman taimako aka taimaka min ake sakar miki da ciwon ciki me tsanani da kuma zuban jini duk kwananki...! Hahahahahhaha kin ɗauka ban sani bane har da bani labari.... Ai wannan malamin ma ba malami bane ruwan asiri na yayi ta baki as magani ke kuma wawuyar kika yi ta amfani dasu har asirin warin jaɓa ya shige ki..."

Kallon maman Rashida tayi tana kwalalo idanu tace
"ke Adama ke munafuka ce! Har abada a matsayin hoto na so Aisha ta zauna gaban Usman se kika min zamba cikin aminci kika karya mun magani ba tare da na ankare ba.... Boka na yace min tunda har wannan ya karye babu yadda na iya sede in fara Haɗawa da kissa irin ta mata su zasu na aiki har gunki ya basu nasara..."

Hararan Aisha tayi kan ta kwashe da dariya se ta fara kuka tace
"Munafuka! Algunguma kwai na guda ɗaya jal na gani gidan Usman amma ke! ke seda na zubar miki da ciki har bakwai na karshe da ya fara girma na baiwa Boka suka shanye mai jini suka musanya shi da kadangare sbd duk maza ne"

Hahahahahhaha tayi dariya kan ta cigaba
"kuka maida ni shahasha kuka koma inda ban isa in taɓa ku ba baku dawo min ba seda ciki, na harzuka naje wurin Boka me taimako na, maji roko na! Yace tabbas cikin nan haifaffe ne be kuma san mace bane ko namiji don basa iya gani...! Na ji haushi raina yayi baƙi nace ya kashe ki Aisha ko ya ɓatar min dake in dena ganinki a rayuwata"

Sosa jikinta da ya fiddo wasu manyan kuraje tayi tace
"kin san me yace min? Munafukar bazata mutu ba sede a ɓatar da ita, amma duk shekara za'a dinga zubdawa aljannu jini sbd su kasance cikin gaskiya a aikinta, million biyu"

Ta Nuna da hannunta tace
"ko wani farkon shekara se na kaiwa Boka million biyu ya zubarwa aljannu jini... Ni ban ma san ko na mutum bane ko na dabba Hahahahahhaha..... Sharadin shine duk ranar da kika dawo ko jininki ya dawo har yayi ido biyu da Alhaji kaikayi ze koma kan mashekiya, ya ce min baze bari ku haɗu ba sbd barbushe ya bashi sa'a...! Yace har ku mutu bazaku sake arba da Usman ba! Munafukar ɗiyarki ta fara dawowa... A fujajan na tafi Kwara wurin Boka sede na samu dajin da yake ya ƙone kurmus babu abunda ya saura shi karan kanshi ko ƙashinshi ba'a samu ba! Shikenan na haukace Aisha ta haukatani... Kaikayi fa ya koma kan mashekiya, wallahi ya koma hahahahaaaaaa"

Cikin tsananin kuka hamza yace
"Hajiya why????? Meyasa hajiya? Hajiya kin cuceni kin cutatar min da rayuwa innalillahi wainna ilahi rajiun.... Menene ribarki? Me yasa kika zama uwata a duniya????"

Kuka yake sosai wadda seda zuciyar kowa ya tabu Dukda kowa na cikin shock da jimamin jin wannan mummunar labarin daga hajiya... Alhj Usman yana zub da hawaye yace

"Allah a gode maka! Allah na gode maka da ka jarabceni da samun irin wannan mace a matsayin mata! Balaraba kin cucemu, kin cuci mata ta da ɗiyata da ni karan kaina sede na gode Allah da ya nuna miki iyakar ki ya maidani Hoto a gabanki ni da kike son mallakewar, me ribar ki??? Kin raba Aisha da ni don in zama naki ni kaɗai, a ranar da Aisha ta tafi a ranar na bi hanyar gembu cikin tashin hankali da talatainin dare na faɗi cikin tsaunuka wadda na shekara ashirin ban anfane ki da komai ba! Ban farka ba kuma Seda ana gab da dawowar Aisha da Hidayat gareni, kin ga ikon Allah ko? Wallahi wallahi ba zan taɓa yafe miki wannan zalunci ba Balaraba, Allah ya isa wahalar Aisha..."

Kuka ne ya kubce mai kaman ba babban mutum ba, Daadida na zub da hawayen tausayi tace
"Hidayat!"

Idanunta da suka kumbura suntum ta ɗago ta kalli Daadida, Daadida tace
"Aisha ta barki hannun Amina, A labarin Aisha Amina bata da mutunci bata san shi ba, shin ya rayuwa ya zame miki hannun ta da iyalinta?"

Raed da idanunshi suka sauya ne sbd damuwa yace
"A'a Daadida don Allah! Ku ji tausayinta mana, kukan nan ya isa haka zuciyata na gab da samun matsala in ta cigaba... I cannot take it anymore!"

Da gaske zuciyarshi na beating fiye da yadda ya kamata ya buga, har daci yake ji a makogoronshi.... Kallonshi hidayat tayi tace
"I'm fine..! It's OK"

Yayi saurin cewa
"no you are not fine, it's not ok please die hard not now, not today"

Abban Rashida yace
"Raed kayi Hakuri ka barta ta bayar ɗin sbd iyayenta na so su ji irin rayuwar da tayi! Ina Alhjn da ya taimaka ma mahaifiyarta yake a yanzu da take a matsayin matar ka bayan ta aureka ne as me aikin gidanka! Ba tare da dangi ko zuri'a ba..."

Runtse jajayen idanunshi yayi ba tare da yace komai ba.

A hankali hidayat ta fara bada labarinta....

#Vote
#share
#comment



                🖤Gureenjo🖤

Continue Reading

You'll Also Like

419K 25.4K 20
𝐒𝐡𝐢𝐯𝐚𝐧𝐲𝐚 𝐑𝐚𝐣𝐩𝐮𝐭 𝐱 𝐑𝐮𝐝𝐫𝐚𝐤𝐬𝐡 𝐑𝐚𝐣𝐩𝐮𝐭 ~By 𝐊𝐚𝐣𝐮ꨄ︎...
6.2K 234 25
labarin soyayya mai ciki da darussa iri iri mai masu tsayawa a zuci..masoyane suke nuna ma juna tsana marar adadi rana d'aya lokaci d'aya kiyaiyar ta...
57.5K 6.4K 37
Rashi ba shi kaɗai yake samar da giɓi a rayuwa ba. Wani yana doron ƙasa amma dalilai kan sa wanzuwarsa ta kasa amfanar da makusantansa. Me zai faru d...
261K 10.7K 37
Complete story of a young girl Ummy.