KOWA YA GA ZABUWA...

By Gureenjo6763

13.9K 1K 46

Rayuwa wani abu ne da kan zo mana da kalubale iri iri, wani muna iya fin karfinshi da taimakon Allah wani ko... More

Page 1
Page 2
Page 3
Page 4
Page 5
Page 6
Page 7
Page 8
Page 9
Page 10
Page 11
Page 12
Page 13
Page 14
Page 15
Page 16
Page 17
Page 18
Page 19
Page 20
Page 21
Part 23
Page 24
Page 25
Page 26
Page 27
Page 28
Page 29
Page 30
Page 31
Page 32
Page 33
Page 34
Page 35
Page 36
Page 37
Page 38
Page 39
Page 40
Page 41
Page 42
Page 43
Page 44
Page 45
Page 46
Page 47

Part 22

286 22 0
By Gureenjo6763

KOWA YA GA ZABUWA...
(DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.
(Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
And Now
*Kowa Ya ga zabuwa..*

*PAGE 22*

*FREE BOOK*

"ASSalamu Alaikum pls can I sit here?"
Ta faɗa tana kallon Hidayat.

Murmushi tayi mata tace
"Wa'alaikumussalam warahmatullah, bismillah..!"

Zama kyakyawar matashiyar black beauty tayi tace
"thank u, am rashida from Nigeria and you?"
Tayi murmushi tace
"masha Allah, nima sunana hidayat daga Nigeria"

Wani irin zaro Idanu Rashida tayi tace
"kaiii wai dama ke ƴar Nijeria ce? Wow kin san Allah kullum ina kallonki na ɗauka irin Larabawa lebenon ɗin nan ce, masha Allah sister u r so beautiful"
Tayi magana tana kallon orange gyale da Hidayat ɗin tayi wrapping ya fito da fuskanta dake nan smooth gwanin kyau.

Dariya ta ba hidayat wadda seda ta dara, tace
"haihuwar Nijeriya girman Nigeria kuwa!"
Ita dae Rashida na ta mamaki ga hausa radau bakin hidayat kam, tace

"Ina karanta MBBS second semester 100lvl ke fa?"

Tace
"law, nima second semester 100lvl, ashe tare muka shiga"

Rashida tace
"ai ko na samu ƙawa dama tunda na zo ni kaɗai nake yawo kaman aljana"

Hira suka cigaba da yi, rashida buduruwa ce kuma wayayyiya daga ganin ta kuma ƴar gidan manya ce gata da surutu, nan take suka saba da Hidayat, kan a tashi har sun shaku tare suka fito daidai lokacin da taji saƙo a wayanta..

Dubawa tayi taga an
"at the entrance of ur school just passing-by nd I guess it's ur closing time, can I pick u up?"
Duba sunan ta sake yi
"Sir Raed"

Tana shirin dauke idanu kenan kuma wayan ya fara ringing
"ya hamza!"

Ɗagawa tayi ta gaida shi ya amsa yace
"Ina gate ɗin ku kin tashi ne?"

Rikicewa tayi tace
"am uhmm ai.. ai na wuce tuntuni"

Shiru yayi kan yace
"is ok, zamu haɗu anjima ko?"

Kai ta gyaɗa tace
"in Shaa Allah by the way it's Friday half day ne ai"

Yace
"ok see u later"

"thanks" ta faɗi tana kashe wayan.

Seda ta tsayar da Rashida na mintuna taga tafiyar hamza kan suka fito sallama suka yi da Rashida ta tafi ita kuma ta nufi motan cikin tafiyan ta na natsuwa, in ka ganta bazaka ce ta haihu har uku ba, yarinya ce wacce ko 25 bata rufa ba amma kaddara da rabo ya zaɓa mata wahalar rayuwa.

A jikinta take ji kaman ana kallonta sede batayi kuskuren ɗaga kai ba har ta isa motar ta buɗe gaba ta shiga, sanyi da kamshin motar na dukanta.

Sanye yake da kayan kwallo har takalmi da alama shima tun safe se yanzu yake shirin komawa gida, cikin muryarta me sanyi tace
"Good Afternoon sir"

Ba tare da ya kalleta ba Yace
"Afternoon how's studies"

Tace
"Alhamdulillah!"

Babu wanda ya sake magana a cikinsu banda qira'ar minshawi dake tashi se take jin wani sanyi sanyi na shiganta ga tausayinshi na rufe ta don da gaske yake shirin koyon Addininshi dole ya tsani Mahaifinshi yanzu ma Allah ne kaɗai ya san da irin damuwar da yake kwana.

Ya gyara parking bayan sun shiga gidan zata sauka yayi gyaran murya hakan ya sakata dakatawa, dashboard ya buɗe ya fiddo wasu Fararen takarda ya miƙa mata

"5 tickets ne to Merseille, taking off in 2hours we're going for our Islamic shoppings"

Da sauri ta kalleshi se suka Haɗa idanu kawar da nata tayi fuskanta na nuna rashin jin daaɗin tafiyan saboda ta tabbatar hamza ba ze taɓa jin daaɗi ya tako kafa da kafa daga Nijeriya ya zo wurinta ita kuma ta kara gaba ba.

A hankali tace
"school fa? I nd the kids!"

Yace
"we r coming back on Sunday and today is Friday I guess"

Ajiyar zuciya ta sauke ba ta yadda zata kaucewa tafiyan, sede bata san yadda zata yi da hamza ba.
Da ma ta bari ya ganta yanzu amma kuma Raed ogan ta ne bazata iya ƙin karɓar taimako da yake son mata na rage mata hanya ta bi hamza ba by the way it's her pleasure, mata nawa a duniya suke da Burin ganin su kusa da wannan celebrityn..

Sauka yayi ba tare da ya ce mata komai ba ya shige cikin gidan, itama saukowa tayi rungume da jakan ta ta shige, tana shiga yana karasa haurawa stairs da Junior da ya ɗauka a parlorn a kafadanshi.

Itama haurawa tayi ta shige ɗakin ta se taji text ta duba shine yace kar su ɗauki kaya ko guda.

Kitchen ta shiga ta sama ma yaran abunda zasu ci bata da cikakken kuzari don bata san me zata cewa hamza ba, kan ta gama suka shigo Norah ta saka tayiwa Farrah wanka ita kuma tayiwa Aisha, take suka fito gwanin kyau kowacce ta rufe gashinta Dukda ba Atampha bane ko jallabiya ba.

A dining suka zauna, daidai lokacin ya fito shima shirye cikin wasu designers Versace riga da wando da ya amshe shi sossai, ya chanza ɗan kunne daga wadda ta gani ɗazu a kunnenshi kafafunshi sanye da rufaffun takalma na kamfanin Fendi, hannunshi sanye da diamond Rolex watch kamshinshi duk ya cika wurin kaman babu wani kamshi se nashi, yana rungume da Junior.

Shima dining ɗin ya zauna yana amsa gaisuwar yaran fuskanshi ɗauke da fara'a, kau da kanta tayi daga Kallonshi shima tayi serving ɗinshi ta kai gabanshi ta saka hannu ta karɓi junior cikin taka tsantsan idanunta akan gashin kanshi da ya sauko ta gefe har ƙasan idon shi na hagu ƙasan black saman ba ja ba ba kuma fari ba an kwashe gefe da gefe zuwa kan ɗan kunnen da yake ta kyalli.

Ajiyar zuciya ta sauke ta ja baya rike da Junior, a hankali zasu zo kan waennan abubuwan dole ya san haramcinsu.

Juyawa tayi ta bar su yana musu surprise na tafiyan su kuwa suna ta ihun murna, murmushi tayi kawai tana jin yadda Aisha take turanci yanzu masha Allah, yarinyar ta samu kyakyawar rayuwar da take musu fata Allah sarki Usman, tuna hakan kaɗai ya saka hawaye cika idanunta.

Wanka tayiwa junior ta shirya shi kan itama tayi ta shirya cikin Jallabiya peach ta saka wani karamin baby hijab me stones baya da gaba ya ɗan fi tsawo akan gefe da gefe shima peach amma ya ɗan turu saɓanin Rigan, kwalli kawai ta saka a idanunta tare da lip gloss ta fito.

Duk a parlor ta same su suna ganinta suka miƙe suka sauka, itama ta bi bayansu Seda yayi magana da su Miss Mary kan ya shiga bayan motan da Paul ya buɗe mai, mota biyu suka yi zuwa Train station sarai zasu iya tafiya a jirgi su isa cikin mintuna sede haka kawai yaji ya fi son su tafi a train ɗin which will take them 3hours da wasu mintuna.

VVIP aka yi musu reserving, be sauka ba seda ya saka face mask da glasses saboda mutane, in ka gansu se ka sake kallo zaka ɗauka wani big happy family ne yana rike da Junior yayinda Hidayat ke rike da hannun Farrah, Norah Da Aisha suna tsakiyar su.

Ita kam bata taɓa shiga train ba, ta dauka yadda ake kallon na India ɗin nan me cunkoso da mutane dayawa zata gani se taga sun shiga wani hadaddiyar room wadda bazaka ɗauka a cikin train yake ba in kana ciki.

Lufas ne manya masu faɗi kuma zagaye da ɗakin harda fararen labule center table da TV, akwai kuma toilet.

Zama suka yiyyi ta zauna daura dashi tare da ɗan yaye labule tana kallon waje, daidai jirgin ya tashi wayanta ya fara ringing..

Dubawa tayi taga Hamza, a sanyaye ta ɗaga suka gaisa ya tambaye ta meeting point, ƙasa tayi da murya sossai yadda baze ji ba Dukda tana jin idanunshi a kanta ta fara yiwa Hamza karya a zuciyar ta tana tuba, akan an basu wani group assignment wadda zasu yi a Mersellei ita bata san ma da tafiyar yau bane kawai kiranta aka yi aka bata ticket.

Daga muryanshi ta san be ji daaɗi ba, for the first time ta mishi en kalamai masu kwantar da hankali har Seda yayi dariya cikin jin daaɗi yace kuma ze jirata, tace
"matarka fa? And aikin ka fa?"

Yace
"duk zasu yi hakuri don ko na koma baza su gane min ba don hankalina da ruhina Duka zan bari a Paris"

Dariya tayi har haƙorinta ya bayyana tace
"shikenan we talk later"

Yace
"take good care of your self"

Daga nan suka yi sallama, ɗaga idanu tayi ta kalleshi bayan ta sauke wayan se taga yana jingine idanunshi a lumshe.

Yaran tuni sun fara bacci kuma duk wurin ya ishe su su kwanta har da blanket ɗin rufuwa, itama jingina tayi ta kunna wayanta ta hau temple run, ta jima a haka kan ta sake ɗaga kai ta kalleshi se taga shima ita yake kallo da idanunshi da suka ɗan birkice, kanta ta mayar ƙasa daidai Wayanshi yayi kara dubawa yayi bayan ya kusa tsinkewa ganin Daadida ne yasa be ɗaga ba seda ta ya katse ya kirata back.

Gaisawa suka yi, ta tambayeshi lafiyan yara yace
"Alhamdulillah"

"Raed har yanzu dae akan maganan mahaifinka ne ko yaya yake uba ne, ina jiye maka fushin ubangiji..." Cikin sanyin murya yace

"wanni fushin ubangiji ɗaya bayan wadda ya sa ni a ciki? Daadida he abandoned me ko kaina ban sani ba, you also left me after na fara just koyon some verses na Alqur'ani wadda da su nake salla, sallar ma na ganin dama without knowing me nake jefa kaina, ban koya ba bare in koyar da yarana suma gashi sanadiyar baƙin hali da zuciya irin na ubana suma na cutar dasu especially Norah wacce ta girma bata san wani mahalicci ba... I've made it clear to you Kaman yadda baya so na I don't fucking care and I also don't like him as well.."

Yana kai nan ya sauke wayan, tare da cillata ta daki jikin train ɗin wannan haɗin kan da Daadida ke so ba ze taɓa wanzuwa ba, da zafin zuciya da kuma ƙuna yake kwana yake tashi tun daga sadda ya fara fayyace laifukan shi a wurin ubangiji, me za'a yi da uba irin nashi tabbas da ana chanzawa suna da ya jima da chanzawa..

A hankali ta miƙe ta dawo gefen shi da ɗan rata tsakaninsu ta sa hannu ta ɗauki Wayanshi ta maida mishi kusa dashi, da wayanta tayi anfani tasa qira'ar Maher cikin Suratul Isra'i, shiru duk suka yi banda bugun zuciyoyinsu da ƙaran karafunan jirgin ƙasan se sautin karatun dake tashi babu abunda kake ji, kamshinsu ya haɗu ya bada wani yanayi me wuyar fassara a temperature ɗin jirgin.

Itama jingina tayi tare da lumshe idanu tana sauraran bugun zuciyarta cikin mamakin sauyawarshi, sun jima sossai a haka se ajiyar zuciya yake saukewa da shi kaɗai ne hawaye ze zubar har ya samu zuciyarshi tayi sanyi amma yanzu ba ze iya ba kuma karatun ya taimaka mishi..

Bayan ya ƙare se wurin yayi tsit, a hankali ya buɗe idanunshi ya zube su bisa fuskanta yana ƙare mata kallo.

Tana da kyau ya ayyana a ranshi daga kan gashin dake kwance lublub daga gaban goshinta zuwa idanunta masu fusgan hankali, karan hancinta da ɗan karamin bakinta ya karewa kallo kan yace cikin ƙasa da murya

"Malama!"

Da sauri ta buɗe idanun ta zube su cikin nashi wadda seda ya ɗauke nashi saboda dokawar zuciya da ta riskeshi har yana ji kaman zata iya jin ƙaran bugun daga inda take.

"Uhm"

Yace
"Ki kara min karatun"

Tace
"tohm amma zaka bani wadda na baka ko? Don in san ko ya zauna"

Ya gyaɗa kai kan yayi bismillah ya fara karantowa lumshe idanunta tayi muryarshi akwai daaɗi haka kawai ma bare yana rero karatu me ratsa zuciya bayan ya gama ta kara mishi da next surah, abunda ya ɗauke hankalinsu kenan har suka isa.

Motoci biyu na train ɗin yayi hiring ya kaisu best hotel na garin "hotel sofitel" wadda yake tsakiyar ruwa, garin shima ya ƙawatu iya ƙawatuwa don shine second biggest city na France kuma akwai Arabs France dayawa a garin don tana ganin masu hijabs gasu nan birjik..

Suits biyu yayi reserving manya tsararru, sauran yinin a hutawa suka karasa washegari Asabar suka fita around 10, wani tsararriyar shopping mall suka je babu abunda babu a wurin sayayya har Seda ta tsorata ganin irin uban abubuwan da ya saya ba Qur'anai da littatafai ba a'a har da Abayoyi tsararru qirar ƙasashe daban daban su huɗu ya kwasar musu kusan hamsin, shima ya sayi jallabiyoyi masu kyau da tsada.

Changing room ya shiga ya cire Rigan jikinshi ya saka wata ox blood jallabiya qirar ƙasar Qatar an yi mata ado da surfani ta gefen kirjinshi ta hagu ba karamin kyau jallabiya tayi mishi ba barin ma da bata je ƙasa chan ba tana bayyana wandon jikinshi wadda designer ne.

Ko da ya fito kasa ɗauke idanunta tayi a kanshi shi kuwa murmushi ya sakar mata tare da dage gira alamun ya ne? tayi saurin kau da kai tana murmushi Masha Allah, ya fita kaman irin Larabawa masu ɗan duhu duhun fatan nan, barin ma jajayen lips ɗinshi da ya ɗan saka a baki yana tsotsa.

Yaran se complementing ɗinshi suke yace ai ko barin kayanshi ze yi, duk zaɓar musu yayi suka sauya, wani Emerald green Abaya me stones na asalin Larabawa ya ɗauko ya miƙa mata.

Ta kalli Rigan kan ta sa hannu ta karɓa ta mike ta shiga change room.

Ko da ta sauya ta juya ta kalli kanta seda ta sake kallo, ba karamin kyau tayi ba murmushi ta saki tana shafa kayan kan ta yafa gyalen da kyau, ta fito cike da jin kunya sbd adon Rigan yayi yawa dole ya fisgi hankali.

Idanu kawai ya zuba mata tana tsaye tana wasa da fingers ɗinta, ihun yaran ne ya dawo dasu daga duniyar da suka tafi suka tattara yayi payment suka fita.

Yawo sossai suka yi a garin suna buɗe ido, wani wurin har yabon su ake da nice family sede yayi murmushi, se chan dare suka dawo.

Washegari ma haka suka tafi yawon se biyar suka yi airport da loggage da basu zo dashi ba.

Karfe shidda na yamma a Orley Airport yayi musu su Paul suka zo suka dauke su zuwa gida, 2days ɗin a wurin su duka was among the best days of there life, duk sun tsinci wani farin ciki da har yanzu sun kasa fayyace ma menene.

A parlorn sama suka yi turus suna kallo gabaɗaya an sauya tsarin parlorn an chanza kujeru an yi shelf me girma da katon wurin sallah da ya ƙawatu ga kyakyawar darduma milk da ash dake shimfiɗe wurin kuma hasken shi me duhu ne se ya bada wani kyaun burgewa.

Bayan sun yi isha suka zo suka shirya Qur'anai da kananun hadisan da suka sassayo a shelf ɗin se ya karasa kawata parlorn.

Se murmushi yake yana ji yanzu za'a iya kiranshi cikakken musulmi, Kallonshi tayi tace
"thanks"

Yace
"for?" Yana narka idanunshi cikin nata.

Ta fusge a sanyaye tace
"the shoppings"

Yace
"ko duka kuɗaɗen da na tara a duniya zan baki ban biya ki ba, u r an angel in human form..."

Sautin kiran wayanta ne yasa yayi shiru tare da Juyawa kawai ya wuce ɗakin shi.

Duba wayan tayi se taga number, bata san waye ba kuma ba Rashida ba picking tayi cikin mamakin yadda wani ya samu layinta....

#like
#share
#comment

                    🖤Gureenjo🖤

Continue Reading

You'll Also Like

2.3K 100 16
wannan sanyin illa zaiyi miki acancikin ki, ai ita mace da ɗumi aka santa, ai ballagaza ita ke illata ƙanta da ƙanta sai sanyi ya kamaki kizo kisani...
45.1K 2.2K 51
"Don ubanki wanki dana barmiki kimin shine kika kiyimin Kika zauna kika rungume wannan shegiyar d'iyar taki wallahi koki aje ta ko kuma yanzu jikin k...
1.6M 98.1K 39
"You all must have heard that a ray of light is definitely visible in the darkness which takes us towards light. But what if instead of light the dev...
616K 64.1K 25
في وسط دهليز معتم يولد شخصًا قاتم قوي جبارً بارد يوجد بداخل قلبهُ شرارةًُ مُنيرة هل ستصبح الشرارة نارًا تحرق الجميع أم ستبرد وتنطفئ ماذا لو تلون الأ...