KOWA YA GA ZABUWA...

By Gureenjo6763

13.9K 1K 46

Rayuwa wani abu ne da kan zo mana da kalubale iri iri, wani muna iya fin karfinshi da taimakon Allah wani ko... More

Page 1
Page 2
Page 3
Page 4
Page 5
Page 6
Page 7
Page 8
Page 9
Page 10
Page 11
Page 12
Page 13
Page 14
Page 15
Page 16
Page 17
Page 19
Page 20
Page 21
Part 22
Part 23
Page 24
Page 25
Page 26
Page 27
Page 28
Page 29
Page 30
Page 31
Page 32
Page 33
Page 34
Page 35
Page 36
Page 37
Page 38
Page 39
Page 40
Page 41
Page 42
Page 43
Page 44
Page 45
Page 46
Page 47

Page 18

255 19 2
By Gureenjo6763

KOWA YA GA ZABUWA...
(DA ZANEN TA YA GANTA)

بسم لله الرحمن الرحيم

FATIMA MUHAMMAD GURIN.
(Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
And Now
*Kowa Ya ga zabuwa..*

*PAGE 18*

*FREE BOOK*

**Assalamu Alaikum warahmatullah gaisuwa irin ta addinin musulunci, fatan duk kuna cikin koshin lafiya? Kuyi haƙurin jina shiru jiyan kaman yadda Zaku sake jina shiru daga wannan se ranar Friday in Allah ya kai rai.... Bautar ƙasa nake gamawa jibi Thursday kenan, tunda Monday ya shigo bamu da zama yini muke wurin abubuwan gamawan da ciwon kai, bacci da gajiya nake dawowa bani da natsuwar typing Sam, fatan Zaku min uzurin hakan. Na gode***

Da sallama ta tura kofan ta shiga, yana lulluɓe cikin bargo daga kafafunshi har kanshi a natse ta karasa gefen bed side ɗin ta ajiye tray ɗin, bata bi bugun zuciyarta ba ta gyara murya kaɗan tace

"Sir ur tea is ready"

Be motsa ba seda ta sake maimaitawa ya kai zara zaran yatsunshi ya janye bargon fuskanshi ya bayyana, gajiyayyun idanunshi ya buɗe a kanta hakan ya sakata saurin rausayar da nata don bazata iya jurar kallon cikin idanunshin ba..

Mikewa yayi ya zauna tare da jingina bayanshi da jikin gadon yana sake kallon fuskanta dake nuna taradaddin rashin lafiyan nashi.

Ganin ya zauna yasa ta ɗauko ta mika mishi karamin tumbler ɗin ya sa hannu garin karɓa hannunsa ya ɗan gogi nata kaman wacce ta sa hannu a cikin wuta ta wani zare da hanzari tare da saurin zaro idanunta kuma tana kallon tea ɗin da ya kusa barewa jikinshi.

Da sauri ya riƙe da kyau yana kallonta itama idanun nata ta ɗago ta kalli fuskanshi se ta duburce, wani malalacin murmushi ya saki yana janye idanunshi ba karamin dariya ta bashi ba, ita kuwa mutuwar tsaye tayi tana kallon kyaun halittar da Allah ya mishi, ba karamin kyau murmushin ya mishi ba.
Ganin ze kara kallonta yasa ta ja baya ta fice da sauri, tean shi ya cigaba da sha yana murmushi lokaci lokaci bayan ya gama ya koma ya kwanta yana me sake rufe jikinshi, cike da Tunanin dalilin ciwon shi yana da wani abu guda idan har abu ya dameshi to se fa ya kwanta ciwo wadda kaman ya zame mishi jiki a daaa chan sede yanzu da ya mance menene damuwa hakan ya zama wani sabon abu a gareshi, so yake ya tantance wasu wasin da zuciyarshi ke yi ya tsayar da ita a matsaya ɗaya sede kwakwalwarshi ta kasa yardar mishi da amsa guda ɗaya tak dake amsa kuwwa daga cikin kanshi har zuciyarshi..

Tana komawa ɗaki ta samu Hamza na kiranta, ɗauka tayi sbd ya kusa yankewa suka fara waya yana mitar bata neme shi ba, daga karshe Aisha ya nema ta Haɗa su suka yi ta surutu, har junior ta makalawa yana ta kiran Daddy suna ta dariya ita dae idanu kawai ta zuba musu, hamza na matukar kaunar yaran nata Dukda be kai Raed ba sede she appreciate..

***

Juyi kawai yake yi from this side of the bed zuwa other side, numfashi da karfi yake ja sede kaman wadda aka shake mishi wuya numfashin baya wucewa zuwa cikin cikinshi hakan yasa yake ta kokawa da numfashin kaman me tashin asthma, zuciyarshi wani irin kuna take kaman an aje garwashin wuta, be saba ambaton Allah ba bare ya ambata yaji sauki, gashi dakakkiyar zuciyarshi bazata bari yayi kuka ba..

Cikin tsanani haka yayi ta juyi se daga baya Allah ya taimake shi ya janyo numfashin da karfi yana mikewa zaune lokaci ɗaya, saitin kirjinshi ya dafe yana haki kan daga karshe ya Haɗa kanshi da gwiwa idanunshi sun rine sun yi jajazir, ya jima be samu attack na panic ɗin nan ba se yau, ya kuma haɗu da wani mummunan mafarki da yayi..

Da sauri ya sauka daga gadon ya nufi frigde ɗinshi na ɗaki ya buɗe cike da son shan ruwa sede babu, haka ya juya ya nufi parlor da sauri..

Daidai lokacin ta fito don daukowa junior ruwan da ta manta bata dauko ba, karo suka ci da hanzari ta koma baya tana ambaton Allah, hannunta dake rawa ta laluba ta kunna switch..

Hard broad chest ɗinshi da ba riga ta ci karo da kan ta kai idanunta kan fuskarsa, wani irin zufa yake Haɗawa kaman ma a firgice yake, zata yi magana ta ga ya sulale ya zauna tare da haɗe kanshi da gwiwa kaman me tsoron mutane kaman kuma me tsoron ta ganshi a halin da yake ciki, da sauri itama ta durkusa tace

"Sir! Me kake bukata? Jikin ne?"

Cikin rawar murya yace
"waaa...ter"

Da gudu taje fridge ta ɗauko ruwan ta dawo ta buɗe murfin ta mika mishi ya karɓa ya kurbi kaɗan ya watsa sauran a fuskanshi zuwa kanshi yana karkada gashin shi wadda feshin ruwan har fuskanta lumshe idanunta tayi, Seda ruwan ya kare tsab kan ya jefar da goran ya sake maida kanshi cikin kafafunshi yana sauke numfashi..

"Mugun mafarki kayi?"

Kaman yaro ya tsinci kanshi da gyaɗa mata kai..

Tace cikin sassanyar muryarta
"ka ja numfashi a hankali sir, mafarki ne ba zahiri ba. Ana so idan mutum yayi mummunan mafarki a duk sadda ya farka ze ce 'Auzu bi kalimatillahi tammat min qablihi wa iqabihi wa sharri ibadihi wa min hamazaatis shayadini wa an yahduruun' Adu'ar na nan cikin hisnul Muslim"

Gajiyayyun idanunshi ya ɗago ya zuba mata yana so ya ce ta sake don be sani ba se yanzu kuma ba ze iya maimaitawa ba, kanta ta mayar kasa ta sake farawa yana bi har suka kai karshe..

Seda ya ɗan natsu kan ya miƙe cikin kasalalliyar murya yace
"thank you"

Jurewa kallon idanunshi dake gigitata tayi cikin natsuwar murya tace
"u welcome, kayi Adu'a karka sake yin irin mafarkin kuma"

Har ya juya ya sake juyowa yace
"ban iya ba"

Runtse idanunta tayi sbd hawayen dake son zubo mata, shi kuwa wani irin rayuwa ne wannan da yayi!

Tace
"baka yin ko wani irin Adu'a?"

Kallonta kawai yake, se taji kaman maganan yayi mishi rashin daaɗi zata ce yayi hakuri se taji ya ce
"me zan roka?"

A tsorace ta kalleshi tace
"Subhanallah! Sir ai Adu'a dole ce ga dukkanin musulmi ko ka samu duniya ba shine ze sa ka kasa neman lahirarka ba, mahaifiyarka dake kwance cikin kabari itama tana bukatar Adu'ar ka don Adu'an ƴaƴa na daga cikin manyan sadakatul jariya  zaka nemi tsari da azabar kabari da na wuta, kuma ka nemi gamawa da duniya lafiya.."

Bakinta dake ta motsi kawai yake kallo idanunshi sun sake rinewa don ambatar sunan mahaifiyar shi kaɗai ya Tono mishi wani miki da ya jima da binnewa, me ke faruwa ne? Meyasa bayan ya manta komai nightmere ɗin Mahaifinshi ke dawo mishi kaman yanzu?

Muryarshi na ɗan rawa yace
"ban san hakan ba..!"

Hawayen tausayin shi ne ya zubo mata ta sa hannu ta share tare da Kallonshi tace
"ai ka iya ayatul kursiyu, qulhuwa, Falaq da nasi?"

Kai ya gyaɗa mata tace
"ka karantasu kafa uku uku se ka shafa in Shaa Allah bazaka sake mafarkin ba"

Kaman ze yi magana se kuma ya fasa ya juya ya wuce, da kallo ta bishi har ya shige room ɗinshi se ta samu kujera ta zauna hawaye na sake silalo mata, Matukar tausayin rayuwarshi na lulluɓe ta.

Ta jima a wurin kan ta ɗauki ruwan ta koma ɗaki zuciyarta fal sake sake..

Washegari Seda likita ya sake dawowa ya sa mishi drip sbd jikin dae ba daaɗi, ba jikin kaɗai ba har zuciyarshi likitan ya tsorata ganin ciwon da suka samu suka raba shi dashi karfi da yaji ne ke shirin sake dawowa, idan kuwa hakan ta kasance har career ɗinshi se yayi affecting..

Yana fita ya kira Father ya sanar dashi, a rikice yace ze bi available flight yau ya zo Paris ɗin.

Norah da Farrah jikinsu duk yayi sanyi kaman sune ba lafiyan har Aisha da kyar ta lallaɓa su suka tafi school, ita ta girka mishi abu marar nauyi da kanta ta kai mishi..

Cikin karfin hali ya mike yayi brush da ta ɗauko mishi har nan ta ajiye mishi abincin, kaɗan yaci yace ya koshi, maganin shi ta ballo ta bashi ya sha da coffee ɗin da ta hada mishi.

Tattare wurin tayi ta fice, da kallo ya bi ta har ta rufo kofan ya koma ya kwanta.

Da rana ma haka ta sake kawo mishi cikin muryarshi yace
"baki je school ba?"

Kanta kasa tace
"eh, idan na tafi babu me kulawa da kai"

Motsi me karfi yaji zuciyarshi tayi da Seda ya runtse idanu, a hankali ya buɗe yace
"thanks"

Kai ta gyaɗa, tace
"ko zaka yi wanka sir?"

Kai ya gyaɗa mata kawai, ta shiga toilet ta hada mishi ruwa me dumi ita dae taga turarukan wanka kala kala a bayin sede bata san wanne yake anfani dashi ba hakan yasa bata saka ba ta fito, ya miƙe yana dafe gini ya wuce nan ma jarumta kawai yake da karfin hali amma shi kaɗai ya san me yake ji..

Yana shiga ta hau gyara ɗakin, fes ta gyare cikin lokaci kankani, bata bari ya fito ya sameta ba ta fice daga ɗakin..

Abincin ƴan makaranta ta hau yi bata gama ba taji motsin shigowa, kuma bata ji hayaniyar yaran ba..

Da sauri ta ajiye abun hannunta ta leƙa se suka Haɗa idanu da kakkarfar mutumin sanye da wando da riga me yanayi da dogon riga baƙi da fari, se wani abu kaman mayafi da ya ɗaura saman rigar igiyar har wurin gwiwar shi, katuwar sarkar cross sanye a wuyan shi se Bible rungume a hannunshi na dama Ɗayan hannun kuma brief case.

Fitowa tayi a ladabce don bata san wanene ba tace
"u r welcome sir"

Kallonta yayi sama da kasa wannan ce kenan da Raed ke faɗa itace sabon nannyn yaran, aiko se ta bar gidan daga gani ma itace sanadiyar ciwon shi da ya tashi tunda a farkon barowansu Nigeria a duk sadda ya ga baƙin fata se ya shiga panic attack, ya zo da wata baturiya daga Amsterdam na Kasar Netherland da dama yawancin zaman shi a chan ne don hakan sallamar wannan dole.

Ba tare da ya amsa ta ba ya wuce zuwa room ɗin Raed, Seda yayi knocking kan ya buɗe yana shiga idanunshi suka faɗa bisa kanshi, da sauri ya karasa yana cewa
"Son!"

Tare da riƙe hannayenshi yana zama bakin gadon, 3 quarter ne a jikinshi da ya zazzage daga sama ya fitar da boxers ɗinshi fari Kal jikinshi ba riga yana jingine da gado yana duba phone ɗin shi ɗakin banda sassanyar kamshinshi me cike da wani ni'ima da sanyaya zuciya na musamman babu abunda yake ga sanyin Ac.

Murmushi ya saki yace
"father finally ciwona ya sa ka zo, Princesses will be happy today"

Yace
"drop that son! Me ya faru? What brings this illness back? Na tabbatar wannan baƙar fatar ce da ka ɗauko"

Kai ya girgiza yana tuna damuwarta da ciwon nashi wadda a rayuwarshi baze ce ya taba ganin makamancin tausayinshi a fuskan wani ba bayan nata, ya karanci ba karamin jimami take ba shi kuwa be san tsoronta na in ya mutu a tsukukin nan yana cikin babban hatsari bane, taimakonta da yayi kuma wadda bazata taɓa mancewa ba yasa ta ci alwashi me girma a kanshi..

"She is not father, I just had a dream abt my past!"

Yace
"then seeing her is the essence, na yi hiring nanny from Amsterdam a well reserved person ita zata cigaba da kula min da jikokina u should fire this one, and that's final.."

Da sauri ya ɗago ya kalleshi..

***

Ita kuwa ganin ya wuce kai tsaye yasa ta saka a ranta maybe dan uwansu ne, komawa kitchen ɗin tayi ta karasa duk wasu ayyukanta kan ta fito ta koma ɗaki.

Kasa bacci tayi a jiya da Tunanin wani irin rayuwa Raed yayi. Shi kuwa menene tarihin rayuwarshi haka? Wanene shi?

Kasa hakura tayi ta lalubi inda ta rubuta landline number ɗin Daadida ta saka kira..

Ringing na karshe aka ɗaga
"Assalamu Alaikum jikata..!"

Ɗan murmushi hidayat tayi tace
"Wa'alaikumussalam warahmatullah ina yini daadida?"

Daadida tace
"mu a wurin mu har yanzu kwana ne, Awa ɗaya da ƴan mintuna ya rage mu shiga yinin"

Murmushi hidayat ta sake tsohuwar akwai barkwanci tace
"to ina kwana"

Tace
"lafiya ƙalau Alhamdulillah ya kuke duka? Ya wannan sarkin miskilancin? Wai fushi yake dani, in kira in kira ya ƙi dauka ja'iri kuma wallahi ba zan fasa gayamai gaskiya ba ko mutuwa ze yi"

Hidayat ta ɗan yi murmushi tace
"yana kwance bashi da lafiya"

Daadida tayi salati ta sallame tace
"Allah sarki, Allah ubangiji ya bashi lafiya ya sa kaffara ne"

Hidayat ta amsa da
"Ameen"

Se ta ɗan yi shiru cikin shirya kalaman da zata yi akan tsari tace
"Daadida kin roke ni a kan tallafar rayuwar uban gidana kuma na ɗau alkawari, sede duk inda na duba babu wata mafita har se in na san wanene Muhammad Raed, yaya rayuwar shi take wani giɓi ne ya samu yake buƙatar plaster se na san ta inda kuskuren ya faro kan in yi tunanin hanyar bi wurin gyara"

Daadida ta sauke numfashi me nauyi tace
"Hidayat shi ba giɓi bane a rayuwarshi, tubali ne bashi dashi kinga toshewa da plaster ba ze taɓa yiwuwa ba in har ana so yayi karƙo se an rushe an sake sabon dakakkiyar tubali, ina nan ina muku Adu'a, ina sadaka ina saukar Alqur'ani da yardar Allah mafarkin da na jima ina yi a kanki nake saka ran tabbatarsa don haka zan faɗa miki wanene Muhammad Raed...."

#Vote
#share
#comment



                 🖤Gureenjoh🖤

Continue Reading

You'll Also Like

11.5K 1.5K 61
Kaddara! Mece ce ita? Yaya rayuwar yarinya mai karancin shekaru za ta kasance a lokacin da ta tsinci kanta cikin mummunar kaddara, irin kaddarar da b...
67.4K 7.4K 58
Murmushi tayi mishi wanda ya tafi da imanin sa yayin da ta juya kallonta ga duɓɓin mutanen wajen. Dogayen yatsunta biyu wanda suka sha jan lalle ta b...
83K 4.4K 59
labarine da ya kunshi rikitacciyar soyayya da ramuwa,Wanda masoyan suna son juna Amman sun kasa gasganta haka Wanda har suka kusa su rasa juna hmmmm...
20.6K 1.5K 40
labari ne akan Najma, wacce hasada, kyashi da yayu nata ya sanya a suka mata auren dole , inda zata fuskanta k'alub'e iri-iri a rayuwa. ku biyoni don...