KWANTAN ƁAUNA

By Nana_haleema

3.3K 145 17

Izza, mulki, k'asaita sun tattara a gare ta ita kad'ai. Y'ar sarki ce, jikar sarki, matar sarki. Bata k'aunar... More

001
002
003
004
005
006
007
008
009
010
11
012
013
014
015
016
017
018
019
020
021
022
023
024
Trailer
KWANTAN ƁAUNA Book2

025

144 11 3
By Nana_haleema

*KWANTAN ƁAUNA*
Fitattubiyar 2023

©️ *Nana Haleema.*

*Book 1*
*025.*

Yaya Ummi tayi shiru alamun tunani kafin ta sauke numfashi ta kalli Rauda tace, "Tabbas Anas ba abin yarwa bane ba, in muka watsar da Anas bamuyi adalci ba." Rauda rausayar da kai tace, "Abinda na gani nima kenan, zan iya auren Anas na zauna dashi duk da bana jin sonsa a zuciya ta har gobe, amma halayyar sa da yadda yake nuna tsantsar so a gare ni zata saka naso shi nan gaba."

Yaya Ummi tace, "Haka ne Rauda, ki cigaba da addu'a kedai kawai duk abinda ya zama alkhairi Allah ya zab'a maki."
"Ina yi sosai." Yaya Ummi zatayi magana kenan aka bud'e k'ofar aka shigo Baba ne da kuma maza guda biyu a bayan sa ganin su waye ya saka Yaya Ummi tashi tsaye tana fad'in, "Sannun ku da zuwa."

D'aya daga cikin su yace, "Yauwa Ummi, ya mai gidan naki?." Yaya Ummi tace, "Alhamdulillah." Gaisawa sukayi har Rauda kana d'aya daga cikin su yace, "Jiya nazo wucewa ta k'ofar gidan ku na tarar an baje gidan gabad'aya ya koma fili ana sabon gini na bulo, daman kuma ina ta ji a gari ban tabbatar ba sai dana gani da ido na; sai yanzu mahaifin ku yake shaida min abinda yake faruwa."

Kawu Badamasi yace, "Ke daman kin san shi ne tun a baya har ya furta yana sonki?." Rauda ta girgiza kai tace, "A'a Kawu bansan shi ba." Ya girgiza kai yace, "ikon Allah kenan, abinda baka tsammaci faruwar sa ba sai kaga ya faru." Kawu Lawan yace, "To ke meye a ranki kenan?." Rauda tayi shiru bata amsa ba Baba yace, "ita bata yanke hukunci ba har yanzu; akwai wani yaro Anas da yake sonta yana hidima da ita sosai ina tunanin shine a ranta."

Kawu lawan yace, "ba d'an gidan Alhaji Tasi'u mai farin gida ba?." Baba yace, "Shi." Kawu lawan yace, "to ai ni Alhaji Tasi'un ya aika min da mutane guda biyu na d'auka ma ko neman auren ta suka zo wajena sai suke shaida min shine ya turo su yace a sanar damu ya yiwa d'ansa mata kar a jishi shiru kwana biyu zai masa aure ne. Sun shaida min bazasu iya had'a ido da kai ba sabida kunya shiyasa suka je wajena kai tsaye." Baba yace, "ikon Allah! Amma baka sanar dani ba."
"Na d'auka shi yaron ai ya sanar dakai ko ya sanar da ita."

Baba ya girgiza kai ransa fari karr har hakan ya bayyana a kan fuskar sa yace, "basu zo inda nake bama shiyasa kwana biyu shiru babu motsin yaron, Allah sarki ni shaida ne yana son Rauda amma da alama iyayen sa basa son alaqar su tare shiyasa suka yanke wannan hukuncin, Allah ya zab'a mafi alkhairi." Kawu Badamasi yace, "Amin. Baza muyi saurin cewa iyayen ne basa son alaqar ba wataƙila alqawarin aure ne sukayi zasu had'a shi yaron bai san dashi ba shiyasa yake neman Rauds. Rauda karki yiwa kanki dole dan ganin kud'i ko dukiya ko kuma sarauta, yanzu maganar Anas ta k'are kinji duk abinda yake faruwa da kunnen ki, kar kice tunda babu batun Anas yanzu bara na amince da d'an sarkin kar kiyi haka kiyi addu'a ki kuma bi zab'in zuciyar ki."

Kai ta girgiza alamun gamsuwa Baba yace, "Ai ana ta addu'a duk inda na bayar ayi mana istikhara sai kaji ance auren sa da ita alkhairi ne ba kad'an ba. Daman Anas d'in nan nake ji tunda abin yazo da haka wallahi nafi kowa farin ciki ya auri zab'in iyayen sa itama ta auri Asad d'in shikenan an huta." Kawu Badamasi yace, "A'a, ka barta ta zab'i abinda take so dan Allah kar abin duniya ya rufe mana idanu mu kaita inda zamu zo muna dama mun sani bamu kaita ba, dan ni Allah ya sani wani lokacin bana yi mata sha'awar shi yaron mai martaba sabida abinda zata tarar ba abu kad'a bane. Na farko da ga babar sa, na biyu ga sauran jama'ar gidan, na uku har abada gidan sarauta bazasu tab'a girmama ta ba k'ask'ance zata rayu dan su gidan sarauta indai ba y'ar gidan sarauta ka d'auko ba talaka sunan ka balle kuma Rauda."

Umma da take zaune tace, "tun a yanzu ya fara bayyana kansa dan mahaifiyar yaron bata jima da fita daga gidan nan ba tayi b'adda kama ta shigo tana yi mata gargad'! akan auren d'anta, har da ikirarin in ta aure shi sai ta b'atar da ita daga duniya, ina dalili d'an sarki ai ba d'an wani annabin bane da za'a so a aure shi. Kuma shi yaron ita dashi bai ma ce yana son ta balle yace zai aure ta, haka zasuyi zaman auren?." Kawu Lawan yace, "sai a bar maganar in mai martaban ya nemi jin ra'ayin ta ace bata amince ba ai ba dukan mu za'ayi ba."

Baba yace, "A'a bafa za'ayi haka ba zata amince ma in sha Allah, meyasa kuke haka ne ku? Alkhairi ya biyo mu kuna k'okarin saka mu guje masa?. Ni ina goyan bayan auren d'ari bisa d'ari kuma in sha Allah sai ta aure shi." Umma tayi murmushi tace, "Daman Malam ai baza ka k'i ba kai." Kawu Badamasi yace, "Muma bamu k'i ba muna fatan abinda yafi alkhairi Allah ya zab'a, in shine alkhairin Allah ya tabbatar da arzuk'i a gidan wasu ai gwara a gidan ku, kuma kowa yana so yaga nasa cikin jin dad'i da kwanciyar hankali, abin alfaharin mu ne gabad'aya ace Rauda ta auri d'an sarki dan kaf dangin mu ba'a tab'a ba sai a kanta. In kuma babu alkhairi Allah ya watsa lamarin waje duk kud'i ko mulki bazai saka mu kaita inda zamu zo muna dana sani ba."

Baba yace, "Da alkhairi ma in Allah ya amince." Shiru sukayi dukkan su kafin suyi sallama su wuce. Baya fitar su Yaya Ummi ta kalli Rauda tace, "to kinji yanzu babu batun maganar Anas sai ki dawo da hankalin ki kan Asad." Rauda ta murmusa tace, "Wallahi Yaya sai nake jin zuciyata tayi min nauyi da akace ya fasa aurena, ashe shiyasa ya kasa nema na a waya."

Umma tace, "Ni kaina zuciyata babu dad'i Rauda balle ke, Anas ya cancanci aso shi kodan soyayyar da ya nuna miki ashe Allah bai rubuta zai mallake ki matsayin matar sa ba, Allah sarki! Allah ya zab'a masa abinda yafi alkhairi ya basu zaman lafiya shida wacce aka zab'a masa." Rauda tayi shiru tana jin babu dad'i a zuciyar ta.

*☆☆*

Gudu yake sosai a motar yadda Mama ta kira shi a wayar tana kuka ta d'aga masa hankali sosai hakan ya saka yake gudu kamar zai tashi sama burin sa yaje yaji kiran da take masa. Ko gama faka motar baiyi ba ya fita da sauri zuwa wajan ta yana shiga falon farko bata nan ya shiga ciki ya tarar da ita ita da Mum a zaune sunyi jugum-jugum kamar an musu rasuwa. Hankalin sa tashe yace, "Mama lafiya?." Kallon sa tayi da jajayen idanun sa ta yafito shi da hannu ya k'arasa kusa da ita ya zauna ta rik'e hannun sa tace, "Asad dan Allah ka janye batun maganar auren yarinyar nan, bata da tarbiyya ko kad'an bata da kirki."

Juya idanun sa yayi ya rik'e hannun ta da yake cikin nasa yace, "meya faru?." Mum da take gefe tace, "zuwa gidan su yarinyar mukayi da niyar ta rok'e ta kar ta amince maka; yarinyar ta dinga zazzaga masa rashin kunya har da k'okarin dukan mahaifiyar ka tana fad'in bata ga wanda ya isa ya raba ku ba. Bata da tarbiyya gabad'aya yarinyar in kaji cin mutuncin da tayi mata baza ka d'auka tana da hankali bama."

Asad da yake jinsu yayi shiru kawai baice komai ba jin yayi shiru ya saka Mama tace, "Asad dan Allah ka fasa auren ta, ka aure ta zan iya mutuwa dan zuciya ta zata iya fashewa ko wanne lokaci." Asad sanyaye yace, "Mamana bazata mutu ba, Allah ya wuci zuciyar ki, I'm sorry" ya furta a hankali yana kallon ta.

"Ka fasa d'in?" Ta tambaya tana kallon idanun sa. Kasa magana yayi dan bai san me zaice mata ba hakan ya saka shi yin shiru kana yace, "zan fad'a sanar da mamana in anjima, ina zuwa yanzu" ya fad'a yana tashi ya fita daga falon zuciyar sa duk babu dad'i.

Mum ta kalli Mama tace, "bafa zai amince ba an riga an juyar masa da tunani daga kanki, in badan haka ba Asad ne kike rok'on abu a wajan sa amma yake cewa ki jira ya dawo anjima, yaron da kince zo kayi yake cewa to in ba asiri ba meye?." Mama sabida abinda take ji bata ce komai ba amma ta amince da asiri aka yi masa dan ga zahiri ta gani.

Mum tace, "Ai hanya ta biyu dole zamu bi, ko a kashe yarinyar, ko a haukata ta. Cikin biyu zamuyi guda d'aya." Mama tace, "Kisan yafi haukan, ta b'ace bat daga duniyar yafi ace tana cikin duniyar hankali ne babu. Kije ayi duk abinda za'ayi aga bayan ta tsakanin yau zuwa gobe kin san bana son b'ata lokaci, sai dai bana so a samu matsala, bana so sunana na ya fito, bana so ayi mata kisan da za'a fahimci kashe ta akayi." Mum ta tashi tsaye tace, "Baki da matsala Fulani wannan ki d'auka an gama." Ta d'auki jakar ta da makullin mota kana tace, "Sai kin jini" tana fad'a ta fice daga cikin falon.

Asad da ya fita daga wajan Mama daga gidan ya fice gabad'aya dan bazai iya jure abinda yake ji ba ya hau mota ya tafi gidan da ya saba keb'e kansa, yana zaune a falon gidan ya zubawa waje d'aya ido yana kallo zuciyar sa na bugawa da gudu ko ya ya kulle idanun sa Rauda yake gani. 'Ina sonta sosai, amma nafi son Mama da ita bazan iya ganin Mama cikin wani hali sabida ita ba, zan cire komai a raina.' Abinda yake fad'a a zuciyar sa kenan gabad'aya ransa a jagule yake.

Motsi yaji a bayan sa ya juya suka had'a ido da Hydar ya k'araso kusa dashi ya zauna yana kallon sa kana yace, "Deaf indai zaka biyewa Mama baza ka tab'a samun farin ciki ba." Da sauri Asad ya kalle shi Hydar yace, "yeah sabida duk hanyar da ka biyo ta neman farin cikin ka sai Mama ta toshe ta, ka bar abubuwa da yawa sabida ita ya kamata zuwa yanzu kaima ka samu abinda kake so a karona farko, farin cikin ta kawai ta sani banda naka."
"She's my mother tana da ikon zab'a min duk abinda take so, bana son rasa ta a cikin rayuwata" Asad ya fad'a a raunace yana kallon k'asa.

"Even me i love her because itace ta haife mu bamu da wata kamar ta a kaf dunitar nan, but tana son kanta da yawa ne Asad musamman akan abinda ya shafe ka, tana tauye maka hakki ka always abinda take so kake yi meyasa wannan baza ta baka dama ba?."
"I can leave anythings because of her" ya sake furtawa yana lumshe idanun sa.

"I know Asad but ka aikata hakan zaka cutar da kanka ne fiye da lokacin baya, Sabida you loves Rauda so much itace ta farko da ka fara yiwa wannan son, lokaci d'aya Allah ya d'ora maka k'aunar ta a zuciyar ka cire ta ba abu bane mai sauk'i. Try to understand soyayya ba irin aiki da mukaman da ta saka ka bari a baya bane, wannan rayuwar kace domin soyayyar ta ta riga ta kama ka barin ta illa ce a gare ka." Asad ya furzar da iska ya kalli Hydar da idanun sa yace, "Meye mafita?."
"Addu'a. Nasan kana yi but ka k'ara a kan wacce kake yi, in Rauda alkhairi ce a rayuwar ka Allah ya baka ita in ba alkhairi bace ya fitar da ita daga ranka."

Asad ya girgiza kai alamun gamsuwa da maganar Hydar kafin Hydar ya kuma cewa, "then yana da kyau ko number yarinyar ne ka nema sabida ku dinga gaisawa, hakan zai rage maka wani abun a zuciyar ka." Asad ya girgiza kai alamun a'a kafin yace, "I can't."
"U can" ya bashi amsa shima yana kallon sa. Murmushi Asad yayi har hak'oran sa suka bayyana fuskar sa ta washe sosai annurin ta ya fito kyau da zatin da Allah yayi mata ya fito k'arara ba tare da ya shirya ba. Ganin hakan ya saka Hydar yayi murmushin shima yace, "Kayi murmushi mana nasan zaka iya sabida kana sonta."

Baice komai ba Hydar daman yasan bazai ce ba sai yace, "Deaf nifa ina ganin rashin gaskiya a tare da Aliyu cikin kwanakin nan, bana amincewa da yanayin sa gabad'aya." Tab'e baki Asad yayi kawai baice komai ba dan shima ya fahimta musamman ma halayya da shiga da ya canja ya koma sak irin nasa kafin ya d'auki wayar sa ya fara dannawa. Haka suka zauna shiru babu mai magana a cikin su sai daga baya suka tafi suka bar gidan.

*☆☆*

Mum ce a zaune a gaban wani malamin daban ba wanda suka je wajan sa da Mama ba yana ta dube-duben sa kafin ya d'ago ya kalle ta yace, "Auren nasu yana da wahalar rabuwa amma za'a raba shi." Mum ta girgiza kai tace, "haka nake so naji Malam, so nake a raba auren a saka masa tsanar yarinyar itama a saka mata tsanar sa ta har abada." Malam yace, "wannan baki da matsala Hajiya Sadiya, sai dai za'a kashe kud'i."
"Kud'i ba matsala ta bane ba Malam ayi kawai."

Malam yace, "Zaki ga aiki kuwa nan bada jimawa ba." Gyara zama tayi tace, "Aiki na biyu so nake a saka masa k'aunar Jidda a ransa fiye da yadda yake k'aunar ita gurguwar, ya manta da kowa da komai Jidda kawai yake gani. Hatta uwar sa Rabi'atu ya manta da ita gabad'aya ya zama Jidda ce zata juya shi yadda take so duk abinda tace shi zaiyi." Girgiza kai tare da yin dariya kad'an yace, "Za'ayi hakan tabbas. Amma yana da wahala kasancewar sa mai ibada da zama cikin alwala muna buk'atar lokacin da ya kasance babu tsarki a jikin sa a sannan aikin mu zai tafi yadda muke so. Dan aikin da zamuyi masa akan Jidda ba k'arami bane ba gaskiya."

Mum tace, "ta yaya zamu san bashi da tsarki?." Malam yace, "Wannan ba abin damuwa bane ba zamu gano hakan da kanmu." Mum tace, "to ma sha Allah haka nake so naji. Batun auren sa da Jiddan yana nan dai ko?." Malam yace, "yana nan kawai dai akwai sauran lokaci amma akwai maganar auren su kamar yadda nake shaida miki, kuma dole sai ita gurguwar bata tare dashi sannan zai kalli Jidda."

Mum tace, "Za'ayi maganin ta ai. Ina maganin da mukayi zaka bani?." Malam ya juya gefen sa ya d'auko wani turare a k'aramar kwalba ya mik'a mata yace, "Wannan turaren zaki shafa in zaki je wajan ta ko in zaki had'u da ita a ko wanne lokaci, ina tabbatar miki tana shak'ar sa a lokacin babu wani sirrin ta da zata b'oye miki komai sai kinji sai kuma abinda kika ce mata shi zatayi."

Mum ta karb'a ta saka a jaka ta fito da kud'i masu yawa ta ajjiye masa kafin tace, "Na gode Malam, a cigaba da aiki in komai yazo mana yadda muke so duka tare zamu ji dad'i, sauri nake mayi waya" ta fad'a tana mik'ewa ta fita da sauri.

*☆☆*

"Me kike so kice mana kenan master planer? Asad zaiyi aure?" Waziri ya fad'a a bayyane cike da mamaki da kuma al'ajabi. Daga cikin wayar Hajiya tace, "Nima dai jin abun nayi wani iri, kika ce kuma gurguwa zai aura?."

Dariyar tayi tace, "tabbas Asad zaiyi aure nan bada jimawa ba zai bar k'asar Nigeria zai tafi can wata k'asar yaje kula da matar sa, a wannan lokacin muke da damar sake nisanta shi da k'asar gabad'aya."

Waziri yace, "To ya maganar Aliyu kuma? Ya amince min amma har yanzu bai sake tuntub'a ta ba nima kuma haka."
"Ya fika wayo wannan yaron raba k'afa yayi yana nasa aikin yana kuma naku aikin, duk maganar auren nan shine assasata badan komai ba sai don cikar burin sa. Zai mana amfani a tafiyar mu sosai domin kansa yana ja fiye da tunanin ku zai kawo mana mafita lokacin da abubuwa suka yi mana yawa."

Hajiya tace, "Sai nake ganin kamar yaudara ce amma baya tare damu." Master tace, "yana cikin mu yana kuma saka idanu akan ku gabad'aya duk motsin ku ya sani, tafiya dashi zata yi mana amfani sosai amma sai nan gaba zaku fahimci inda na dosa. Tsarin da ya saka muka jawo shi cikin mu yanzu babu batun sa tunda shi Asad d'in zai bar k'asar nan da wasu kwanaki ba buk'atar mu canja shi da Aliyu."

Waziri yace, "kuma kina ganin tsarin zai tafi yadda muke so kuwa?."
"Sosai ma kuwa fiye da hakan ma ku dai ku shirya ta kusa fashewa mu samu abinda muke so, boom!" Ta fad'a tana yanke wayar compress call d'in ya rage daga shi sai Hajiya a kai. "kana ganin abinda tace haka ne kuwa? Nifa ban ji maganar aure a cikin gidan nan ba ta ya akayi ita ta san da ita?."
"Tunda tace haka tofa haka d'in ne, zan bincika yanzun nan naji gaskiyar lamarin koma meye ai bazai b'uya ba, in da gaske akwai maganar auren ai sai munfi kowa farin ciki da hakan. Ki saurare ni zan sanar dake abinda na binciko" ya fad'a yana yanke wayar shima.

*☆☆*

Rauda haka ta wuni sukuku bata son Anas amma bata jin dad'in raba su d'in da akayi lokaci d'aya ba gabad'aya sai taji tana jin zafi a zuciyar ta hakan ya haifar da sanyin jiki a gangar jikin ta. Tana zaune a d'akin da suke kwana ita da Ummulkhairi tana juya wayar da ya bata gabad'aya wani iri take jin ta kamar ba ita ba zuciyar ta a jagule kamar ta zubar da hawaye. Shigowar sak'o taji wayar ta tayi kamar bata ta duba ba sai kuma ta duba ta bud'e tana karantawa.

_Assalamu Alaikum Rauda ina fatan kin wuni lafiya ya jikin ki da jikin Umma?. Nasan kin ji labarin abinda yake faruwa wata k'ila zaki ji babu dad'i duk da ba sona kike yi ba amma nasan zaki tausaya min tunda kin san ke kad'ai ce a zuciyata ke kad'ai kuma nake k'auna. Wallahil azim ke nake so Rauda har gobe har jibi har na mutu amma iyayena sun nuna min wacce suke so na aura babu yadda zanyi na amince musu sabida matsayin su gare ni. Bazan ce ki jira ni nayi aure na dawo na aure ki ba nasan abu ne mai wahala shiyasa na saka a raina na rasa ki har abada, wallahi ina rubuta miki message d'in nan ina hawaye Rauda domin na tabbatar na rasa abinda nake so wanda bazan mayar da kamar sa ba har abada. Ina sonki Rauda, ina k'aunar ki har gobe, naso ace zan rayu dake har abada amma hakan bai yu ba duk da har yanzu ban cire rai dake ba amma ni kaina ina ganin wahalar hakan. Ki yafe min wallahi ba'a son raina ba banyi kuma dan na yaudare ki ba, kunyar ki nake ji shiyasa na kasa ko kiran ki a waya dan ban san me zance miki ba in na kira ki, ina fatan zaki yafe min za kuma ki dinga min addu'ar Allah ya bani ikon yiwa wacce za'a aura min adalci domin matuk'ar ba ke ba bana tunanin akwai wacce zan zauna da ita da zuciya d'aya. Ina miki fatan alkhairi Allah ya baki miji na gari ya baki lafiya Amin. ANAS._

Babu tsammani taji hawaye yana bin fuskar ta wanda batayi tunanin zasu zuba ba a wannan lokacin ba, ta ajjiye wayar tana kuka mara sauti tana fad'in, "Allah ya baka juriyar rashi na Anas, ni kaina zanyi rashin wanda yake sona da zuciya d'aya, ko bana son ka zan iya zama dakai Anas sabida kai me k'auna tane na tabbata bazan yi dana sanin zab'ar ka ba, Allah bai amince zan zama matar ka ba, Allah ya baka hak'urin rashi na" ta fad'a tana goge idanun ta jikin ta duk ya mutu murus.

Asad ne ya fad'o mata a rai nan take gaban ta ya fad'i ta dafe k'irjin ta tana jin yadda yake bugawa tayi shiru ta nutsu tana sauraron bugun zuciyar tata a hankali, ta rasa meyasa in ta tuna shi take jin bugun zuciya ta rasa dalilin hakan. kawar da tunanin tayi ta d'auki wayar ta ta shiga mayarwa da Anas amsa da kalamai masu sanyaya zuciya da taushi had'i da tausasawa har ta kammala ta ajjiye wayar a gefe tana tunani.

'Matuk'ar bai bayyana min yana k'auna ta ba bazan amince da auren sa ba, a soyayya ba'a nuna mulki da izza shi na lura abinda yafi mayar da hankali kenan a kai, zan nuna masa ba'a samun ko wacce mace da k'asaita ko izza.' Abinda take fad'a a zuciyar ta kenan a bayyane tace, "to ma in ya furta zan amince kenan? Anya na dace da rayuwar sa na kuma yiwa kaina adalci..? ga abinda mahaifiyar sa take fad'a ban kai kaina inda za'a kashe ni ba kuwa?. To wai duk da nake wannan tunanin sonsa nake kome..?" Ta fad'a tana jan dogom tsaki tana kallon sama abubuwa sun mata yawa a kanta duk sun cushe mata zuciya.

K'arar wayar ta taji duk a tunanin ta a Anas ne ta jawo ta ta d'auka bata duba waye ba ta d'aga wayar ta kara a kunnen ta tana jiran taji maganar Anas sai taji sab'anin hakan, nan take zuciyar ta ta sake bugawa ta cigaba da bugu kamar ana doka ganga tunanin ta ya tsaya cak lokacin da taji ance, "Ina sonki, na fara sonki lokacin da ban shirya ba........!."

*End of Book1*🤗⛹‍♀️

_Waye ya kira Rauda wannan lokacin..? Asad ne ko kuma Hydar ne ya kira a madadin sa...?. Rauda zata amince da Asad tunda babu maganar Anas a halin da ake ciki ko a'a..? In ta amince dashi tayi ya da Mama wacce take shirin kashe ta? Anya auren su zai kasance Mama tana raye...?. In ya kasance kuma ta yaya ta wacce hanya hakan zata faru...?. Ina matsayin Jidda da kuma Mum da suke son ganin bayan Mama? Asad zai amince da Jidda kuwa har ya aure ta? In ya aure ta kuma ya kenan in suka raba shi da Maman sa?. Aliyu fa? Anya shima zai bar Asad zaman lafiya duba ds yadda ya koma acting like Asad..? Anya babu abinda yake shiryawa a kan hakan tunda dukkan mu mun shaida yana son ganin bayan Asad?. Wacece master planer? A ina take da zama da take sanin sirran cikin gida tun kafin na gidan su sani?. Ina makomar su Waziri zasuyi nasara ko a'a? Shin Asad zai mulki katagum ne ko a'a? Shin Rauda zata zata aure shi ko a'a? Shin Jidda zata aure shi ko a'a?. Akwai rikici, akwai makirci, akwai tashin hankali, akwai dana sani, akwai soyayya, akwai akasin ta duk a cikin book2._

1000 for complete document via 09030398006 only on WhatsApp.

Sai na jiku mutanen amana🥰

#Vote
#Share
#like
#Comments
#gidan sarauta
#makarci
#fuska biyu
#Soyayya
#Nana haleema.🥳

Continue Reading

You'll Also Like

54K 3.1K 50
Na kasa fahimta da gasgata abinda zuciyata ke ayyana mini a kansa, SO ne ko BIRGEWA?. Komai nasa birgeni yake, ban taɓa ji ko ganin wanda ya haɗa abu...
29.1K 1.8K 22
Tayaya ummi da salman zasuyi rayuwar aure wanda da abaya basu son junan su an hada su AUREN HAĎI ku biyoni muji yadda zata kaya
868 65 13
Labarin soyayyar Aaliyah Badamasi Bulama da Sa'eed Aliyu Modibbo a shekarun 80's...
44.3K 1.5K 5
Is all about, love, sacrifice and Royal👑