KWANTAN ƁAUNA

By Nana_haleema

2.3K 136 17

Izza, mulki, k'asaita sun tattara a gare ta ita kad'ai. Y'ar sarki ce, jikar sarki, matar sarki. Bata k'aunar... More

001
002
003
004
005
006
007
008
009
010
11
012
013
014
015
016
017
018
019
020
021
022
023
025
Trailer
KWANTAN ƁAUNA Book2

024

60 4 3
By Nana_haleema

*KWANTAN ƁAUNA*
           Fitattubiyar 2023

           ©️ *Nana Haleema.*

*Book 1*
*024.*

         Asad baiga Baba ba da ya fita a mota ya tarar da Hydar kawai ya shiga ganin hakan Hydar yaja motar ya tafi yana satar kallon Asad da yake murmushi mai kyau kana gani kasan zuciyar sa fari tas take a wannan lokacin. Shima murmushi Hydar ya mayar da hankalin sa kan tuk'in kana yace, "in aka ce min deaf zai so wata mace lokaci d'aya haka bazan amince ba, amma sai gashi na gani na kuma tabbatar kana cikin soyayyar da baka san iyakar ta ba." Hannu Asad ya saka ya shafa kansa yana kallon titi shi kansa mamakin kansa yake yi domin bai tab'a d'auka akwai soyayyar wacce zata yi masa kamu lokaci guda kamar ta ba, bai kuma d'auka akwai macen da zai yiwa wannan son na farar d'aya haka ba sai gashi ya tabbata yana kuma kan faruwa a lokacin.

"Ka fad'a mata kana sonta face to face dai ko?." Asad ya girgiza kansa alamun a'a Hydar yace, "to meyesa baka ce mata ba? Meye amfanin zuwan da mukayi?, dan fa ka sanar da ita kana sonta ya saka na d'auko ka muka zo nan."
"Oho" ya furta ya shafa fuskar sa yana lumshe idanun sa. Hydar yace, "gashi ai yanayin ka ya dawo daidai da kazo ka ganta, kana cikin damuwa amma gashi daka ganta ka dawo normal. But da ka sani kayi mata bayanin yadda kake sonta, ina so ka sani Asad lokaci yayi da zaka ajjiye wannan rashin maganar taka, ka san ita soyayya ba ruwan ta da mulkin ka ko nasabar ka ko kud'in ka, a iya kwanakin da ka fada tarkon sonta nasan ka tabbatar. Ka fuskanci abinda zuciyar ka take so in ba haka ba zaka iya rasa ta, soyayya tana son kulawa sosai."

Kallon sa yayi idanun sa a bud'e sosai yace, "babu maganar rasata" ya fad'a yana cize bakin sa cikin jin zafin kalmar rasa ta da yace zaiyi. Hydar yayi y'ar dariya kana yace, "na sani shiyasa nace ka dage Asad, a kan idon ka aka nuna mana wanda yake sonta zai iya kwace ta in ya fika iya kula da ita, na farko kai ga yanayin nature d'in ka ga kuma yadda abin yazo in ba mayar da hankali kafi ba zaka zama looser, kuma sun saba da wancan kai kuma kalma mai tsaho bata tab'a had'a ku ba." Murmushi kawai Asad yayi bai kuma cewa komai ba ya mayar da hankalin sa kan in ya tuna Mama gaban sa sai ya fad'i yaji komai ya fice masa a rai.

             Washe gari.

           K'arfe tara na safe Mum tazo ta d'auki Mama a mota suka fita su biyu kacal ko hadiman Mama bata bari sun biyo ta ba babu wanda yasan inda zasu je sai su kad'ai.  Tunda ta shiga motar take k'wafa Mum da take tuk'i dai bata ce komai ba domin itama nata ran a b'ace yake sosai sai daga baya Mama tace, "Wai ni Takawa zai yiwa fad'a kamar zai dake ni akan wata banza y'ar matsiyata bayan hak'urin da ya saka na basu?, kamar ni ace na bawa wad'annan k'ask'antun hak'uri....? Me suke dashi a duniya da zan kalle su nace suyi hak'uri....? an cuce ni wallahi" ta fad'a tana dukan jikin motar ranta a b'ace.


Mum dai bata tanka ba tafiya suke yi lokaci kad'an suka shiga wata unguwa da babu jama'a ko kad'an sai gidaje kad'an-kad'an kamar rugar fulani suka faka motar suka fito dukkan su suka shiga cikin gidan.

       Wani k'aramin d'aki suka shiga wanda yake baje da magunguna na itace dana gari da turarruka kana dosar d'akin kasan d'akin maganin gargajiya ne, wanda yake zaune a gaban faranti da aka zuba masa yashi da k'aton mudubi a kusa dashi yana ganin shigowar su ya murmusa yace, "Barka da zuwa Fulani." Waje suka samu suka zauna kafin Mum tace, "Malam mun same ka lafiya."
"Lafiya lau Sadiya, ya yara suke?."
"Lafiya lau. Matsala ta taso dole muka zo da kanmu shiyasa nace basai kazo ba zamu shigo nida Fulani."

Mama ta kalle shi bayan ta d'age nikaq d'in fuskar ta tace, "kamar yadda ta maka bayani a waya Sunan yarinyar Rauda inaso a duba min aga kodai asiri ta yiwa Asad har ya furta yana sonta duk da tarin nak'asun dake tare da ita da kuma tarin y'an matan da suke so ya kula su ya tsallake su yaje wajan ta." Jin abinda Mama tace ya jawo farantin gaban sa ya fara dubawa kusan minti d'aya da wani abun kafin ya karkad'e hannun sa yace, "a abinda muka gani bata yi masa asiri ba had'uwar jini ce kawai."
"Ka dai sake dubawa ko wani ne daban yayi masa asiri dan ya sota" Mum ta fad'a tana kallon sa.

Malamin ya kalle su yace, "Kamar yadda na fad'a muku babu batun asiri a tare da lamarin nan soyayya ce daga Allah wacce ya dasa masa ita a zuciyar sa."  Mama tace, "To meyesa yake sonta?."
"Ranki ya dad'e soyayya ce da kuma had'uwar jini ce."
"Ban amince da wani had'uwar jini ba dole akwai wani abun a k'asa. Kai kanka da zaka ga yarinyar na tabbatar zaka bada shaidar akwai abinda aka kulla." Mum ta kalle shi tace, "to yanzu ya za'ayi kenan?." Malam d'in ya sake duba farantin sa sannan yace, "Asad yana son yarinyar sosai lokaci guda Allah ya saka masa ita a ransa, yana sonta kamar ya had'd'iye ta. ita kuma yarinyar kamar har yanzu babu wani tsayayyen abu a ranta amma dai......" Mama ta katse shi ta hanyar fad'in, "Amma me..? A datse soyayyar kawai."

Malam yace, "ranki ya dad'e kenan hakan yana nufin a yiwa Asad aiki ko?." Mama tace, "A'a ba tun yau ba kasan bana san a yiwa Asad wani abu a yiwa ita yarinyar amma bashi ba." Malam ya murmusa yace, "Ranki ya dad'e banda abin ki ita da babu abu tsayayye a ranta shine akwai soyayya a ransa sai dai in shi za'a yiwa aikin a cire ta daga zuciyar sa. "Mama ta girgiza kai tace, "A'a ko kad'an bana son hakan, a nemo wata hanyar." Malam ya sake bincikawa ya kalle su yace, "Kun sani bana fad'ar k'arya dan na samu wani abun a wajan kowa, haka zalika bana fad'awa mutum abinda zaiji dad'i koda bana jin dad'in na gani ba, ina fad'ar abinda Allah ya bani ikon gani ne komai d'acin sa. Maganar gaskiya auren yarinyar nan da Asad bazai lalatu ta sauk'i ba akwai wani abu mai k'arfi da yake rik'e dashi."

      A firgice Mama ta kalle shi tace, "A lalata shi ta k'arfi, a saka k'arfin da yafi nasu k'arfin a tarwatsa shibana son hakan ta kasance ne ko a mafarki." Malam ya jinjina kai kafin Mum tace, "A yiwa yarinyar asirin da zata ji ta tsane shi gabad'aya taji bata son ganin sa ko kad'an, kaga koda tayi niyar amincewa dashi zata fasa." Malam ya sake dubawa kana yace, "Yiwa yarinyar aiki ba abu bane mai sauk'i, tana da rik'o da ibada fiye da tunanin ki Hajiya Sadiya." Mama ta dafe kai cikin takaici tana cizan yatsa zuciyar ta na tafasa sabida b'acin rai jikin ta har zafi ya d'auka kamar mai zazzaɓi, bata k'aunar talaka ya rage ta balle kuma y'ay'an ta.

     Mum tace, "A kashe ta ko a haukata ta!." Malam ya yi murmushi yace, "Kar ayi gaggawa ranki ya dad'e, shawara a nan aje a same ta a tsoratar da ita har a cusa mata tsanar auren tak'i amsawa zata aure shi, a fitar mata da sha'awar auren jinin sarauta a zuciyar ta. A ganina wannan itace kawai hanya mai sauk'i in tak'i sai a dauki mataki." Mum tace, "Kenan mune zamu same ta?."
"Kwarai ku da kanku zaku same ta in akayi sa'a hakan zaiyi aiki, domin indai ba ita tace bata so ba Asad bazai fasa auren ta ba haka mai martaba bazai fasa bashi ita ba."

Mama ta sauke numfashi tace, "ya batun sarautar sa?." Malam ya bincika kana yace, "Tana nan, kamar yadda na sha fad'a miki shine zai mulki katagum har gobe maganar haka take; amma kamar koda yaushe akwai qalubale manya ma wanda suka fi na baya yawa. Na farko maganar auren nan zata sake dagula komai, na biyu wad'annan wanda nake fad'a miki suna aiki a kansa sun sake zage dantse sun k'aro makaman yak'in yak'ar ku, na uku suna gab da yin nasara a kanki da kuma kan Asad d'in." Mama ta sauke ajiyar kana ta sassauta murya tace, "ya batun tsarin jikin sa?."

"Ranki ya dad'e komai lafiya yana k'ok'ari wajan ibada da rok'on Allah shiyasa suka kasa nasara akan sa har yanzu." Kai ta girgiza kafin ta mik'e tsaye tace, "Zamuyi waya, muje" ta fad'a tana yin gaba tare da sakin niqab d'in fuskar ta. Mum ta kalle shi bayan ta tashi tace, "Akwai maganar da zamuyi ma tattauna a waya" ta fad'a tana fita daga d'akin tabi bayan Mama da sauri. Suna shiga motar Mama ta kalle Mum tace, "muje gidan su yarinyar."

Zaro idanu Mum tayi tace, "muje muyi me? Kin manta rashin kunyar ta dana baki labari?; marina fa tayi."
"Zamu je mu gyara komai ne yanzu."
"Kamar ya mu gyara Fulani? Kema in ta maren ki fa?."
"Ko uban uban ubanta bai isa ya tab'ani ba balle ita; dalilin da Malam ya fad'a shine zai kai mu wajan ta."
"Amma fulani......?" Dakatar da ita Mama tayi ta hanyar cewa, "Muje kawai. Zan nuna miki gidan da suka koma."

Shiru Mum tayi zuciyar ta a wuya take tuk'in har suka zo k'ofar gidan su Rauda Mama ta fita daga motar tana kallon gidan ta tabbatar nan ne inda aka binciko mata ta nufi zuwa cikin gidan, juyowa tayi taga Mum bata fito ba ganin tana kallon ta ya saka ta fitowa suka shiga cikin gidan.

K'ofa biyu suka gani suka tsaya suna kallon k'ofar cikin tunanin waccw zasu bi a ciki, bud'e d'aya akayi aka fito hakan ya saka suka kalli wacce ta bud'e k'ofar ta kalle su tace, "Bayin Allah daga ina?" Inna ta fad'a tana kallon su. Mum ta kawar da kanta gefe da alama baza ta bada amsa hakan ya saka Mama tace, "Muna neman wajan su Rauda."

"Gashi nan" ta fad'a tana nuna musu d'aya k'ofar suka wuce ba tare da sun kuma kallon ta ba. Da sallama suka bud'e k'ofar sai gasu a falo Rauda na zaune ita da Umma da kuma Yaya Ummi suka amsa suna kallon su, ido Rauda suka had'a da Mum ta bita da kallo kana tace, "tofa kice shugabar y'an daba ce da kanta ta kuma dawowa, to yau kuma da me kika zo mana...? zauna ki bamu labari" ta fad'a tana kallon Mum cikin sigar rashin mutunci.

         Mama ta zauna ta d'age nikaq d'in fuskar ta ta kalli Umma tace, "Sannu ya jikin?." Umma tace, "lafiya lau Alhamdulillah. Amma ban sanki ba." Mama ta murmusa tace, "Sunana Fulani Rabi'atu mata a wajan sarki katagum ya a wajan sarkin Kano, jika wajan sarkin Kano, uwa a wajan sarkin Katagum mai jiran gado" ta fad'a tana kallon su. Yaya Ummi tace, "Allah sarki! To sannu." Mama ta kalli Rauda tace, "wajan ki nazo." Rauda da mamaki ta kalle ta tace, "gani ai kin ganni."

Mama tazo wuya jin amsar da ta bata amma ta jure tace, "d'ana Asad ya furta kalmar so a gare ki a lokacin da ban shiryawa hakan ba, ya nuna ke yake yi kuma na riga da nayi masa mata tun ba yanzu ba, gidan sarauta gida ne na rikita-rikita kanki bazai d'auki abinda yake faruwa a cikin sa ba koda an baki labari, duk inda kike tunanin abun ya wuce haka gwara ki zauna a gefe hakan zaifi miki alkhairi. Nasan halin mahaifin sa tunda yace amsar ki ake jira ita ake jira indai kika amsa zance ya k'are in kuma kika yi akasin haka za'a fasa shiyasa nazo na shawarce ki akan karki kai kanki ga halaka matsayin da kike k'okarin takawa yafi k'arfin ki akwai mata sosai a gaban ki." Kallon Umma tayi kana tace, "Ke uwa ce baza kiso ki rasa d'iyar ki ba ki bata shawarar kar ta amsa batun Asad domin kuwa tana niyar shiga wuta ne da k'afar ta."

Umma tace, "banda abin ki kinji ance y'ar mu zata auri d'anki ne?." Mama ta tab'e baki tace, "ko d'aya nasan baza tak'i tayin ba ai shiyasa nake fad'a mata gaskiya."
"Ai kuwa sai muce a kai kasuwa domin kuwa tana da wanda yafi Asad d'in" Yaya Ummi ta fad'a tana kallon ta. Kyakykyawan murmushi Mama tayi tace, "tana da daidai ita dai amma bawai wanda yafi Asad ba ko yarinya..? Ta samawa kanta lafiya da kuma zaman lafiya."

Rauda da take gefe tace, "in kuma na amince masa fa?." Mama ta kalle ta tace, "abinda ma bazai yu ba kenan, keda shi sai dai taimako amma yafi k'arfin ya zama mijin ki har Allah ya tashi duniya, Rauda sunan ki ko?" Ta fad'a tana kallon ta cikin k'ask'anci da rainin hankali Rauda tayi dariya tace, "kodai nafi k'arfin sa ba tunda shine yake jiran amsa ta bani nake jiran tasa ba, shi ya gani ya mato yace yana so har kika kasa dakatar dashi kinga kenan nice nafi k'arfin sa bashi yafi k'arfi na ba. Ki rike d'anki daman bana sha'awar auren kuramen maza ni."

"Ke yarinya ki iya bakin ki! Ki san da wacce kike magana" Mum ta fad'a a fusace tana kallon ta Rauda tace, "in kuma nak'i fa akwai abinda za'ayi min ne?." Mama tace, "Naga alama kanki yana rawa sosai kina ji da y'an matanci, ki saita harshen ki tun kafin ya kai ki ya baro ki" ta fad'a tana nuna ta da yatsa. Umma tace, "Rauda ya isa haka." Mama tace, "ya kamata dai kija mata kunne ta san da wacce take magana."
Rauda tace, "Ke kika tako k'afar ki kika zo har inda muke dan haka baki isa ki fad'a mana maganar da batayi mana ba kuma nayi miki shiru ba."

Mama tayi k'wafa tace, "Ba wannan ne a gabana ba abinda na fad'a miki shi ya kamata kiyi, maganar auren Asad ki d'auka a mafarki kika tab'a ji ba a gaske ba" ta fad'a a kausashe. Rauda ta tab'e baki tace, "Umarni ne ko shawara?."
"Umarni ne!" Ta fad'a a fusace tana kallon ta.
"Dalili?" Rauda ta fad'a tana binta da kallon raini. Mama tace, "ke banzo wajan nan dan na fad'a ki fad'a ba, ina so kisan badan Jan kunnen da zan miki ba uban ki ma bai isa na fad'a ya fada ba balle ke y'ar k'aramar tsakuwa. naga alama baza kiji maganar a nutse ba sai an fad'a miki da yaren da talaka yafi ganewa wato duka. Ki samarwa kanki lafiya ki bar Asad in baso kike wani abun ya same ki ba."

Rauda tace, "babu abinda zai same ni sai abinda Allah ya nufa. Sannan babu wanda ya isa ya saka ni yin abinda banyi niya ba, in naga dama kuma zan iya cewa ina sonsa na aure shi kodan naga yadda zaki koma a lokacin."

A fusace Mama ta mik'e tace, "Kee! Kar ki sake hasashen wannan ranar a rayuwar ki domin baza tazo ba har abada. Ke wacece da zaki zama matar d'an sarki jikan sarki kuma sarkin gobe? Wacece ke? Banza kike, bak'a, mummuna, matsiyaciya, gurguwa mai tallan abinci a titi. Ke ko a mafarki akace zaki zama matar sa sai ki amince?."
Murmushin rainin hankali Rauda tayi tace, "Da alama sirikata kina wasa da ikon Allah kinga ta inda muka samu banbanci kenan ni nasan duk wahalar abu a wajan Allah mai sauk'i ne." ta fad'a tana kallon ta itama tana kallon ta.

Mum tace, "kul kar ki sake kiran ta da wnanan sunan bai dace a bakin mace irin ki ba, ki sani akwai matan da suka amsa sunan su mata sama da d'ari da suke son su furta wannan suna amma yafi k'arfin su." Rauda tace, "ba tsoron ta kar na amsawa Asad zan sa aure ba? To ina so ku sani da zarar lokacin da aka d'iba yayi zan tabbatarwa da mai martaba ina son Asad kuma zan aure shi kodan naga ya zakuyi a lokacin da Bak'a, mummuna, gurguwa, y'ar talaka, mai tallan abinci ta zama matar sarki Asad; kuma sirikar y'ar sarkin Kano babar sarkin jibi. Kunga sai ku d'auki bindiga ku harbe kan ku" ta fad'a tana kallon su one by one.

A fusace Mama tayi kanta zata mare ta Mum ta rik'e tana girgiza mata kai Mama a fusace tace, "matuk'ar kika aikata haka zakiyi dana sanin da baki tab'a yi ba tunda Allah ya kawo ki duniya. Zan iya sakawa a b'atar dake daga duniyar gabad'aya wannan ba komai bane a wajena matuk'ar zan samu abinda nake so. Sai na tabbatar baki tako k'ofar gidan sarauta ba balle ki kasance a matsayin da kika lissafa domin yafi k'arfin kaf dangin ki gabad'aya. Zan miki biyu babu, babu Asad babu sauran wanda suka zo taimakon ki su aure ki tunda abin naki rashin kunya ce" ta fad'a tana nuna ta da yatsa cikin murya mai amo da alama kamar wani abun ma bata san tana fad'a ba sabida b'acin rai.

Rauda ta tab'e baki tace, "Ina jira na gani sirika ta, in kuma nice naci wasan na shigo gidan matsayin sirikar ki nice nayi nasara bake ba." K'wafa tayi fuskar ta har ja tayi sabida b'acin ran da take ji a zuciyar ta wanda bata tab'a jin irin sa ba sukayi hanyar waje kafin Mama ta tsaya ta juyo ta kalli Umma da Anty Ummi tace, "Duk abinda ya samu y'ar ku kuyi kuka da kanku.." Rauda ta d'aga murya tace, "babu abinda zai same ni sai alkhairi. Kii gaida min mijina kinji sirika ta!." Juyowa tayi ta kalle ta Rauda tayi dariya kafin ta girgiza kai ta fita daga falon a fusace.

Kallon Rauda Umma tayi bayan sun fita cikin fad'a tace, "Wannan wanne irin rashin hankali kike aikatawa haka Rauda?. Ke kuma babbar banza mai biye mata ina yi mata magana kina tab'a ni wai na k'yale ta tana yiwa wacce ta haife ta rashin kunya, Ni in aka yi min haka zaku ji dad'i ne?. Matar sarki ce fa bamu yi mata komai ba ta saka anzo gida an ci mana mutunci ina ga kun fad'a mata wad'annan maganganun marasa dad'i...? Ba kaina nake ji ba ke nake ji Rauda zata iya yi miki komai dan ganin bayan ki." Yaya Ummi tace, "Umma ai ke baza ki aikata abinda ita tazo tayi mana har cikin gida ba bayan wanda ta saka akazo har gida aka ji miki ciwo, ai wallahi munyi mata da sauk'i ma irin ta'asar da tayi kamata yayi mu kamata mu rama irin abinda ta saka akayi miki. gani take kud'i shine komai zata iya juya mu tayi mana rashin mutuncin da taga dama bata san bata isa ba wallahi. Dan tana matar sarki baza muji tsoron ta ba tunda ita ta d'auko k'afa tazo har inda muke ko zane ta mukayi itace ta jawo."

Umma ta kalle su tace, "ya dai isa haka bana son tashin hankali da yiwa na gaba rashin kunya. Ku tuna a  gidan d'anta muke ko a yanzu mun ci albarkacin ta dan ba bata haife shi ba damu zauna ba, da badan yazo inda muke ba da wataƙila yanzu bamu san a inda muke zaune ba. Kar na sake ganin kin yiwa wani haka koda nan gaba ne, wannan ba tarbiyya ce." Umma ta fad'a tana kallon Rauda kafin ta tashi ta shiga d'aki.

Yaya Ummi ta kalli Rauda tace, "Ke me kika yanke game da auren shi Asad d'in?." Rauda ta kalle ta tace, "Ban yanke komai bani domin bana ra'ayin auren sa gabad'aya. Ya cika rainin hankali da yawa bazan jure ba."
"Kuna tare da Anas har yanzu?."
"Tun dai ranar yazo har yace min bashi ya aiko mana da kayan abinci ba ban sake jinsa ko a waya ba gaskiya."
"Kuma baki neme shi ba?."

"Na kira shi jiya amma layin a kashe." Yaya Ummi tace, "inda nice ke Rauda da Asad d'in nan zan aura badan yafi Anas kud'i da mulki ba sai dan na nunawa uwar sa ba'a ja da ikon Allah, duk k'ask'ancin mu da take gani in Allah yace yes bata isa tace no ba duk abinda take ji dashi sai dai tayi ta gama ta d'auki jikan da zaki haifar mata. Gurguwa, bak'a mai tallan abinci da take rainawa ta zama mata ga d'an nata da take ji dashi sai naga uwar abinda zatayi." Rauda tayi murmushi tace, "Nima zan so hakan Yaya kodan naga yanayin da zata shiga a wannan lokacin, amma sam ni bana ra'ayin auren sa."
"Kiyi ra'ayin yanzu Rauda, kar ki manta tun ba yau ba kina yawan ce min kinyi mafarki da namiji mai rawani a kansa wataƙila Allah ne ya nuna miki auren sa tun a mafarki. sannan istikhara da kika yi Allah ya nuna miki a mafarki ko?."

Rauda tace, "Haka ne Yaya Ummi amma hakan ba yana nufin shi zan aura ba. Nifa bazan iya zama matar sa ba gaskiya in na aure shi nayi ya da k'iyayayar mahaifiyar sa?." Yaya Ummi ta dawo kusa da ita ta dafa ta tace, "Shi zaki aura Rauda, ki saka a ranki shine mijin ki da zarar an tambaye ki kice kin amince." Rauda ta kalli Yaya Ummi tace, "Nifa bana son sa ta yaya zan amince?."
"Sabida mu nunawa babar sa iyakar ta, mu nuna mata duk abinda kake ji dashi baka isa kaja da ikon Allah ba."
"Ni tsoron gidan sarauta nake fa Allah ya sani."
"Ki ajjiye tsoron ki saka a ranki a nan aka haife ki."
Rauda ta kalle ta da mamaki tace, "Yaya Ummi in na amince da Asad Anas fa? Nayi masa adalci kenan duk tarin d'awainiyar da yayi dani dan na samu wanda ya fishi na watsar dashi...?."

Continue Reading

You'll Also Like

452K 32.3K 43
ပဲပြုတ်သည်ငပြူးနဲ့ ဆိုက်ကားဆရာငလူးတို့ရဲ့ story လေးတစ်ပုဒ်
16.9K 882 32
DR UMAIMAH USMAN BULAMA,Mace yar kimanin shekara ishirin da tara , Babbar surgeon A asibitin CITY TEACHING HOSPITAL , Aure Uku, ƴaƴanta uku . Mace m...
KASHI By stuckinatale

General Fiction

397K 19.8K 42
"So, Mrs. Kashi Abhay Pratap Singh..chalte hai. Goodbye..". Saying this, he left her broken in this world of betrayal. ~~~~~~~~~~ Kashi, a simple gir...
52.7K 2.1K 18
"I promise you Mami, zan nemo miki ƴar'uwarki a duk inda take a faɗin ƙasar nan. SULTAN promises you that." Sultan ya shiga ya fita, har ya aikata...