KWANTAN ƁAUNA

By Nana_haleema

2.4K 136 17

Izza, mulki, k'asaita sun tattara a gare ta ita kad'ai. Y'ar sarki ce, jikar sarki, matar sarki. Bata k'aunar... More

001
002
003
004
005
006
007
008
009
010
11
012
013
014
015
016
017
018
019
020
022
023
024
025
Trailer
KWANTAN ƁAUNA Book2

021

69 4 0
By Nana_haleema

*KWANTAN ƁAUNA*

             ©️ *Nana Haleema.*

*Book 1*
*021.*

           Hankalin Mama in ya kai miliyan ya tashi jikinta har rawa yake sabida tashin hankali ta tashi ta bar wajan da sauri ta nufi ciki hankalin a tashe sosai. Bata tab'a jin abu mai munin abinda Aliyu ya fad'a mata ba gabad'aya ya gigitata ta rud'e jikin ta har rawa yake yi sabida rud'ani. Kallon agogo tayi taga k'arshe sha d'aya na safe ya kusa ta saka takalmi da sauri ta fita zuwa b'angaren y'ay'an nata dan tana so ta tabbatar da abinda akace mata. Gab da zata shiga falon taji sautin muryar Hydar yana cewa, "Deaf in love, ban tab'a amincewa zaka fara soyayya da wata mace ba duba da yanayin ka da yanayin maganar, sai gashi ka fad'a ba tare da ka shiryawa hakan ba, wannan soyayyar taku itace silar accident."

Asad dai baice komai ba Mama jin abinda ta jiyo ta sake firgicewa ta kuma tabbatar Aliyu bai mata k'arya ba abinda ya fad'a gaskiya ne tunda gashi har Hydar ya sani yana kuma kiran soyayyar da silar accident, har zata shiga falon sai kuma ta koma da baya da sauri ta koma b'angaren ta ta shiga cikin d'akin ta hannu na rawa ta d'auki waya ta kira Mum. Buga biyu Mum ta d'auki wayar kafin tayi magana tace, "Sadiya in kina da time ki shigo yanzun nan." Daga can b'angaren Mum tace, "An gama ranki ya dad'e, bani mintina goma zan iso." Mama bata kuma jin me tace ba ta yanke wayar ta cillar kan gado tana zaga d'akin hankalin ta yayi mugun tashi.

        Zagaye take daga nan zuwa nan ta kasa zama abinda bata tab'a tunanin zai faru ba shine yake k'okarin faruwa jinin ta wanda ya fito daga jikin ta shine da son y'ar talaka, jinin talakawa kuma nakasashshiya. Jinin nata ma kuma Asad da ta k'wallafa rai a kansa ace shine yake son y'ar talaka gurguwa mummuna wannan ba k'aramin abun kunya bane a wajan ta. Shigowar Mum ya saka Mama ta juya Mum ta k'araso da sauri tana fad'in, "Ranki ya dad'e lafiya kuwa?."
"Ina fa lafiya; zauna mu tattara" Mama ta fad'a tana zama itama Mum d'in ta zauna.

"Me ya faru?."
"Meye ma bai faru ba Sadiya. Wani abu naji wanda yayi bazanar tarwatsa min zuciya ya jefa ni cikin wani hali wanda ban shirya tsintar kaina a cikin sa ba." Mum tace, "Ranki ya dad'e meye wannan d'in haka?."

Mama tace, "Ace wai jinina wanda na haifa da kaina ne zai so jinin talakawa, y'ar talakawar ma y'ar tallah a titi bak'a kuma gurguwa? Ta yaya hankali na bazai tashi ba?." Mum ta dafe k'irji ciki da firgici tace, "mun shiga uku, gaskiya dole hankalin ki ya tashi domin kuwa wannan babban cin mutunci ne da cin fuska a gare mu duka ba ke kad'ai ba."
"Bari kawai, yanzun nan naji maganar yanzun nan na tabbatar da ita amma zafi nake ji a k'irjina kamar ana tafasa min zuciya."

Mum tace, "Amma waye da wannan d'anyen aikin? Nadai san Aliyu bazai aikata hakan ba sai dai Hydar dan nasan shine zai iya b'allo mana wannan ruwan." Mama tayi murmushin takaici zuciyar ta na sake cika taf da k'una da b'acin rai tace, "Wanne Hydar ana zaune qalau...? inda Hydar ne ai hankali na bazai tashi haka ba. Babbar giwar fa Asad; wanda yake jiran kujerar masarautar nan wai shine yake soyayya da yarinya irin wannan." Gaban Mum yayi mugun fad'uwa jin wanda aka ambata ta dafe k'irji cikin tashin hankalin da ya bayyana akan fuskar ta itama ta zaro idanu tace, "Asad! Mun shiga uku."  Mama ta girgiza kai bata ce komai ba Mum tace, "Kuma kin tabbatar da maganar? In kika duba yanayin sa ranki ya dad'e sai naga kamar ba zai saurari irin su ba, Anya maganar nan daga majiya mai tushe take?."

         "Da Aliyu ya fad'a min ban amince sosai ba amma da naje na riska suna magana da abokin sirrin sa Hydar a sannan na tabbatar da Aliyu baiyi min k'arya ba. Sadiya jinina tafasa yake yi bazan lamunci wannan lamarin ba gabad'aya." Mum tace, "ni kaina jinin nawa tafasa yake ranki ya dad'e balle ke. Amma fa abinda mamaki anya kuwa ba asiri tayi masa ba? In ba asiri ba a yadda kika lissafo ta meye abin so a wajan ta har da yarima mai jiran gado guda zai d'aga kai ya kalle ta?."
"Babban tashin hankalina kenan Sadiya."
"To shi kin ji ta bakin sa?, ina nufin kun tattauna dashi akan lamarin?."
"Bai san ma na sani ba."
"Amma yana da kyau shima a tsawatar masa a kanta tunda yana jin maganar ki."

         "Wannan ba komai bane ba Sadiya na fara maganin yarinyar shi ba wani abin damuwa bane in nace bana so zance ya k'are; ita yarinyar ita nake so na jawa kunne ko dan tasan wutsiyar rak'umi tayi nesa da k'asa. Ina so tasan ruwa fa ba sa'an kwando bane, ta banbance tsakanin zare da abawa." ta girgiza kai cikin gamsuwa tace, "Haka ne, yana da kyau mu tauna tsakuwa dan aya taji tsoro. Amma wanne mataki kika d'auka a zuciyar ki wanda kike gani zamu aiwatar dashi?."

Mama ta kalle ta tace, "Shiyasa na kira ki domin inaso ko meye a aiwatar dashi yau bana son b'ata lokaci." Mum tayi jim tana tunani kafin tace, "Mu saka a d'auko ta a sace ta mu bata wahala sosai a sake b'alla k'afar ta ta kinga in aka mata haka zata shiga hankalin ta." Mama ta girgiza kai tace, "Shawara ce mai kyau wannan amma bazata yu ba, in labarin ya bayyana daga baya sunan mai martaba zai b'aci a garin nan za'a dinga yawo dashi ace nice na aikata hakan. Canja wata."
Mum tace, "Haka ne. Mu tura mutane su je gidan ayi mata dukan tsiya ita da iyayen ta inda dama a b'alla ta a b'alla iyayen ta a kuma yi musu kyakykyawan warning wanda zai shiga jikin su, kin ga zasu ji tsoro dukkan su bama ita kad'ai ba har da iyayen ta."

Mama tayi murmushi cikin jin dad'in maganar tace, "Wannan shawarar tayi d'ari bisa dari da kuma ita zamuyi amfani; amma fa bana son aje da wani dogari daga gidan nan dan tonuwar wannan maganar ma b'ata suna ne a idanun mutanen gidan nan balle mutanen gari, k'askanci ne a wajena ace yaron dana fi so cikin y'ay'ana yana bibiyar wata y'ar talakawa. Inaso aje dake domin kiyi musu kyakykyawan warning wanda zasu shiga hankalin su." Mum tace, "Wannan ki d'auka an gama ranki ya dad'e, zan samu mutane a waje muje muyi duk abinda kika ce ai abu ne mai sauk'i."

Mama ta girgiza kai tace, "kuje a fara aiwatar da komai yanzu bana son b'ata lokaci Sadiya ke kin sani." Ba musu Mum ta mik'e tace, "An gama ranki ya dad'e" tana gama fad'ar hakan ta fita daga gidan da sauri.

         Mum na fita gida ta koma Jidda bata nan gidan babu kowa jikin ta har rawa yake dan tama fi Mama son d'aukar mataki a kan Rauda ta d'auki abinda zata d'auka ta fita daga gidan da sauri. Mata da maza ta had'a duka ta biya su aka tafi gidan su Rauda lokacin rana ta bud'e sosai.

            Rauda na zaune akan kujerar da ta saba zama ita da Umma da Inna bata nan sauran sun tafi makaranta, Baba ne ya fito daga d'aki bai fita da wuri ba Umma tace, "Malam kaji ashe duk abinda aka kawo gidan nan ba Anas ne ya bayar ba?." Baba ya kalle su yace, "kamar yaya kenan?."
"Jiya take yiwa Anas mganar magani yake cewa shi duk abinda aka kawo bashi ya bayar ba, hankalina duk ya tashi ban san abin wanda muke ci ba wallahi, da alhairi yake neman mu ko akasin sa duk bamu sani ba." Baba yace, "Bashi bane ba? Kuma Rauda ba wasa yake miki ba kuwa?."

Rauda tace, "Ya rantse min da Allah akan bashi bane ba." Baba cikin mamaki yace, "To amma dashi muka yi maganar ta kawai, da shi muka yi maganar keke napep d'in nan ya akayi wani daban yasan da ita?." Umma tace, "abinda ya d'aure min kai nima kenan." Shiru Baba yayi sai shiru can kuma yace, "Koma dai waye tunda ba sata nayi ba ai shikenan, ban kuma rok'i mutum ba Allah ne ya kawo min tsuntsu daga sama a gashe akan me zan ki ci ni kuwa?."

Umma tace, "Amma malam ya kamata a bincika." Baba yace, "Na bincika ina? Nida ke da kowa bamu sanshi ba ina zanje na bincika nace ga wanda nake nema nida ban sanshi ba?; kar ki d'aga min hankali ina zaune lafiya dan Allah."
"Assalamu Alaikum!" Aka fad'a daga soron gidan aka wuce Baba suka shigo cikin gidan mata uku maza biyu sai Mum ta hud'u. Baba da yake kallon ikon Allah ganin maza garada sun shige shi sun shiga tsakar gidan sa kai tsaye babu izinin sa ya k'araso yana kallon su yace, "Malamai lafiya kuka shigo min gida kai tsaye haka?."

Mum ta k'are masa kallo ta kalle gidan tace, "Au wai wannan gida ne?, ni na d'auka wani kango wanda y'an zaman banza suke zama suna shaye-shaye da yiwa yara fyad'e muka shigo, wai ashe gida" ta fad'a tana kallon wanda suka shigo sai suka fashe da dariya har da tafawa. Rauda ta kalle su tace, "Malamai lafiya zaku shigowa mutane gida kai tsaye?." Jin yadda tayi maganar cikin tsiwa ya saka Mum kallon ta tace, "Oh kece gurguwar kenan, astagafirullah" ta fad'a tana dariya kafin tace, "Yadda aka kwatanta min munin ki ma ashe kin wuce wajan, wannan sai kace ragowar y'an wuta; wanne bak'in zunubi kuka aikata kuka haifo wannan?" Mum ta fad'a tana kallon Baba tana nuna Rauda.

Rahma ta mik'e tace, "Dallah malamai me ya kawo ku gidan mu har kuke fad'a mana maganar banza?." Mum tace, "Koma gefe keda uwar ki y'an kallo ne. wajan ita da uwarta da uban ta muka zo ba ku ba, so ki tsaya kiyi kallo in kina da waya ki d'auko ki fara d'aukar video."
"Wacece ke da zaki zo kina fad'a mana maganar banza da wofi?" Umma ta fad'a tana mik'ewa tsaye. Baba yace, "Malama lafiya me ya kawo ku gidan nan?." Ta juya ta kalli Baba tace, "Jan kunne nazo nayi muku gabad'ayan ku akan gangancin da kuke neman aikatawa, ina so ku jawa y'ar ku kunne ta fita hanyar wanda take cikin hanyar sa, babu shi babu ita domin shi d'in ba sa'an ta bane tazarar su kamar tazarar sama da k'asa ne. Yafi k'arfin ta ya kuma fi k'arfin dangin ku gabad'aya."

Baba da gaban sa ya fad'i nan take Anas yazo ransa amma baice komai ba sai yace, "Akan wa kuke magana?." Mum ta gyara tsayuwa ta tofar da yawu tace, "Wannan gidan ai sai ka d'auki ciwo, bari kuga" ta fad'a tana d'auko facemask a jaka ta saka sannan tace, "Ina magana ne akan ASAD! Wanda kuka kamowa kurwa kuka asirice shi baya ganin kowa sai waccan bak'ar annobar, kaja mata kunne zata d'auko ruwan dafa kanta matuk'ar bata fita hanyar sa ba zatayi dana sanin da bata tab'a yin irin sa ba har abada."
Rauda dake zaune cikin fusata tace, "Waye Asad? Meye shi suna ne ko gari?, mutum ne ko aljani?" Ta fad'a cikin masifa tana kallon Mum da ba ita take kallo ba. Mum ta juyo ta kalle ta tace, "kin sanshi ai basai na fad'a miki ba, tunda har kuka iya bin bokaye kuke so ku kamo zuciyar sa ai kinfi kowa sanin sa. ke banda tsaurin ido ma da kwad'ayi irin na jikar talakawa ina ke ina Asad?, kalle ki fa kamar wacce aka d'auko daga cikin bak'in gawayi, tsabar bak'in da yake fuskar ki sai a d'auka jikar shaid'an ce ke, kalli k'afar ki abinda ya rage miki hawa kan titi ki fara bara amma ki fara tunanin Asad dan talauci ya toshe miki kwakwalwar ki."

"Kece dak'ik'iya mara hankali wacce bata san darajar d'an adam ba babu girma sai na jiki, shi wanda kike magana a kai bansan da zaman sa bama balle na d'aga idanuna na kalle shi, dan haka kija bak'ak'en k'afafun ki a fitar mana daga gida" ta fad'a cikin rashin kunya tana mata ihu. Mum ta girgiza kai tace, "lallai yarinya zan nuna miki ni ba sa'ar yin ki bace, ga sa'a ta nan" ta fad'a tana tsinkawa Umma dake tsaye mari ba zato babu tsammani. Baba ya yunk'uro zai zo wajan mazan suka rike shi gam ta juya yana kallon sa ransa a b'ace yace, "Ke wacce irin mahaukaciya ce shashasha? Ya zaki shigo har cikin gidana ki saka hannu ki daki matata?."

"Dan na nunawa y'ar ka itace abokiyar yina ba ita ba, kuma....." saukar marin da taji a tata fuskar ya hana ta k'arasawa ta juyo a razane  taga Rauda a tsaye da sandinan ta tana wuci cikin b'acin rai Mum na juyowa a fusace Rauda ta sake bata wani sabon marin da batayi tsammani ba. Cikin fusata da rashin kunya da yatsa ta nuna ta tace, "A kaf duniya babu wanda ya isa ya tab'a min iyayena k'yale shi ciki kuwa har dake, in zafin kai kike ji dashi na fiki, in rashin kunya ce itama na fiki, in iskanci ne shima na fiki, duk abinda kike ji dashi a tafin hannuna kike na dame ki na shanye. Na rantse da Allah kika sake dukar min uwa ko kika sake tab'a min uba sai na sake marin ki sai naga abinda zaki min. Banza babbar banza mara hankali mai tunanin jakuna" ta fad'a tana hararar ta cikin b'acin ran da ya bayyana k'arara a ka fuskar ta.

Mum da take kallon ta hannun ta dafe da kuncin ta kasa cewa komai tayi sai jikinta da yake rawa sosai alamun b'acin rai tsanar ta na shiga ko wanne sak'o da lungu na jikinta, tunda take ba'a tab'a tozarta ta kamar yadda akayi mata yau, yarinya k'arama ta fad'a mata wannan magana mai zafi har ta mare ta..?. Hannu ta saka da k'arfi ta tankad'e Rauda ta janye duka sandinan ta kalli matan tace, "Me kuka jira ne ku fara aiwatar da abinda ya kawo mu ku nuna musu mu ba sa'anin su bace" ta fad'a tana marin Rauda da k'arfin gaske. Nan da nan suka shiga dukan Umma da Rauda kamar Allah ya aiko su Inna da ta shigo lokacin ita da Rahma suka zo ceto aka had'a dasu ana duka Baba yana hannu an rik'e shi ya kasa komai.

"Asad yafi k'arfin ta ku sake b'alla k'afar tata dan uban ta" Mum ta fad'a tana daga gefe ana dukan Rauda kamar zasu kashe ta. Baba yace, "Waye Asad din nan da kike magana a kansa? Bamu sanshi ba balle muyi abinda kuke so. Dan Allah ku bar dukan su ko waye zata rabu dashi."
"Ai ko baka ce ba sai ta rabu dashi, ka kuma ce mata ta karya asirin da ta yi masa in tana son zaman lafiyar ta da ta uwar ta har ma da kai ubanta. Ta fita daga sabgar Asad d'an sarki sai y'ar sarki ko y'ar mai kud'i ba d'iyar talaka y'ar tallah kamar ta ba."

      Ganin sun duku ya saka tace, "Guys ku shigo ku d'aye min kwanukan rufin gidan nan naga inda zasu kwana yau daman naga langa-langa ne kawai" ta fad'a daga k'arfi sai ga maza uku sun kuma shigowa suka hau saman d'akin suka farar b'alle kwanon rufin d'akin wanda yayi gardmar cirewa suna huda shi da abu mai kaifi. Mum ta saki dariya tana tafa hannu ta kalli Rauda da bakin ta ya fashe jini na zuba a gefe tace, "Ke ba y'ar marasa kunya ba...? yanzu kika fara gani, har ni zaki saka hannu ki mara da yake baki da mutunci ko? ai kin tarowa kanki bala'i da masifa har ki mutu. Ku k'yale su haka kuzo mu wuce ai ko yanzu sun ji a jikin su; sai ku ja mata kunne in bata fita daga rayuwar Asad ba wallahi nan gaba sai mun saka an rushe gidan nan an kuma yi musu abinda yafi haka, banzaye mahaukata masu kai kansu inda Allah bai kaisu ba" tana fad'a ta shige ta fita suma suka bi bayan ta mazan saman suka diro suka bi bayan ta.

       Suna sakin Baba yayo kan Umma a guje dan ita kamar bata numfashi ma gwara Rauda tana motsawa amma Umma na kwance sosai. Kuka Rauda take yi sosai Rahma da ta maku tana gefe ganin sun tafi ya saka tayo kan Rauda ta d'aga ta fuskar ta duk jini hawaye na bin fuskar ta. Baba ya fita da sauri hankalin sa a tashe ya yi sa'a mai chemist d'in yana nan ya tawo dashi gida aka fara duba Umma da take kwance. Fita yayi ya dawo da kayan aiki aka shiga yiwa Umma taimakon gaggawa aka samu ta farfad'o dukan fuskar ta aka gyara aka saka mata ruwa dan jikin ta yayi zafi sosai ga hannun ta an mata targed'e. Kan Rauda akayi aka gyara mata fuska aka bata maganin ciwon jiki dana ciwon da taji a fuskar ta har loksckn kuka take. Ba kukan dukan take ba kukan zuwa gida da akayi aka wulaƙanta su take yi in ta kalli Umman ta bata sanin sanda hawaye yake sake zubo mata.
Yana fita aka zo da mai gyaran targad'e ya gyara hannun Umma aka d'aure hannun sannan suka tafi Baba jikin sa duka yayi sanyi.

Kuka sosai Rauda take yi tana jikin Rahma Baba yace, "Rauda ban fahimci abinda matar nan take nufi ba, meye tsakanin ki Asad har hakan ta faru?." Kai take girgizawa tace, "Wallahi babu komai Baba, bansan wanda suke nufi ba; sun yi amfani da power sun zo sun wulak'anta mu sabida bamu da gata bamu da wanda zai bi mana hakkin mu. Wallahk Baba bazan yarda ba sai maganar nan taje gaban hukuma sai an bi mana hakkin mu, Baba sai an karb'a mana hakkin mu bazan amince da wannan cik mutuncin ba" ta fad'a tana kuka sosai.

Baba yace, "Nima bazan bari ba Rauda cin kashin yayi yawa. Tunda sukayi maganar Asad d'an sarki zanje wajan mai martabar da kaina na kai masa k'arar abinda ya faru, ai talauci ba hauka bane ba. Meye tsakanin mu dasu in ba silar ciwon nan naki ba? Dan kawai yana sauke nauyin da yake kansu na nema miki lafiya kawai sai azo har gida ayi mana wannan shirmen...? To wallahi bazan amince ba." Kuka take ita dai har lokacin tana kallon saman d'akin Umma da aka kwashe kwanon kai rana tar a cikin sa sai wani b'angaren da aka huda, a hankali bacci ya d'auke ta Allah ya saka akwai inuwar rumfa a wajan.

*☆☆☆*

          B'angaren Asad bai san me yake faruwa ba suna tare da Hydar a company dan bai koma aiki ba yana wajan Asad, sai da sukayi azahar suka bar company suka koma gida dan yunwa Asad yake ji. Suna b'angaren su Suhaima tazo ta kawo musu abinci ta ajjiye ta zuba musu kamar ko yaushe, Asad ya d'auki wanda ta zuba masa ya d'auka zai kai bakin sa Suhaima ta kalli Hydar tace, "Yaya Hydar wai me ya faru ne naga ran Mama a b'ace?."

Hydar ya fara cin abinci kana yace, "Ina zan sani Suhaima nida na dawo yanzu?."
"Naji tana waya tana a dake su bata kai matsayin yin soyayya da wanda ta haifa ba, na d'auka ma ko kaine ka fara soyayya da wata poor lady d'in ta saka ayi mata punishment." Gaban Asad ya fad'i ya ajjiye cokalin daman tunda ta fara maganar bai kai abincin bakin sa ya kalle ta yace, "Suhaima me kika ji tace?."

        "A yadda take maganar dai an tura gidan su yarinyar ayi mata duka amma ban san wacece ba. Naji tana a dake ta inda dama a sake b'alla k'afar ta babu abinda aka siya ayi." Mik'ewa Asad yayi ya d'auki key na mota da sauri ya fita, ganin hakan Hydar ma ya ture abincin ya mik'e  tare da bin bayan sa suka fita Suhaima ta bi su da kallo.

          Mota suka shiga suka tafi gidan su Rauda gaban Asad sai fad'uwa yake yi har suka faka a k'ofar gidan, babban burin sa bai wuce Allah yasa basu illatata ko wani nata ba.
Baba suka gani ya fito yana waige-waige ganin hakan ya saka Asad ya fito daga motar Hydar ma ya biyo bayan sa suka k'araso kusa dashi, Baba na ganin su tun kafin su gaisa yace, "Kamar kusan kune a raina, me muka yi muku haka da za'a aiko azo a ci mutunci na dana iyalai na?, me Rauda tayi muku har haka aka yi mata wannan hukunci....? dan Allah ku fad'a na baki hak'uri."

Asad ya kalli Hydar shima ya kalle shi kafin Hydar ya kalli Baba yace, "Baba meye ya faru?." Baba yace, "Kuzo muje ku gani" ya fad'a yana yin gaba suka bi bayan sa gaban Asad sai fad'uwa yake yi sabida fargaba da tashin hankalin abinda zai gani a cikin gidan.

Continue Reading

You'll Also Like

23.7K 1.5K 75
Emotional and love story
371K 22.8K 38
Let's see how different personalities mends with each other to form a beautifull bond together. Where the Eldest is calm and cold, Second is aggress...
808K 69.4K 59
Zanen ƙaddaransa yana cikin zuciyarta, kamar yanda zanen nata ƙaddan ke cikin tasa zuciyar. Idan zuciyoyi suka haɗe waje guda akan samu wata irin zaz...
17.1K 882 32
DR UMAIMAH USMAN BULAMA,Mace yar kimanin shekara ishirin da tara , Babbar surgeon A asibitin CITY TEACHING HOSPITAL , Aure Uku, ƴaƴanta uku . Mace m...