KWANTAN ƁAUNA

By Nana_haleema

2.4K 136 17

Izza, mulki, k'asaita sun tattara a gare ta ita kad'ai. Y'ar sarki ce, jikar sarki, matar sarki. Bata k'aunar... More

001
002
003
004
005
006
007
008
009
010
11
012
013
014
015
016
017
019
020
021
022
023
024
025
Trailer
KWANTAN ƁAUNA Book2

018

67 4 0
By Nana_haleema

*KWANTAN ƁAUNA*

             ©️ *Nana Haleema.*

*Book 1*
*018.*

         Cizo ya kawo mata karen shine ya saka ta yin k'ara ta kulle idanun ta tana jiran taji sukar hakoran sa a a naman ta amma sai taji shiru, ta bud'e idanun ta a hankali taga karen baya gaban ta kamar d'azu ta juya gefen ta ta ganshi a tsaye ya juyo yana kallon ta kusa da wanda bata tantance waye ba. A hankali yake takowa yazo kusa da ita suka had'a ido sai jikin ta ya cigaba da tsuma ya had'e hannayen ta waje guda tana kuka amma ta kasa magana.

      D'auke kai yayi daga kanta ya kalli wad'anda suka sato ta sai suka zube a k'asa cikin girmamawa hannun su na jinjina d'aya yace, "Tuba muke ranka ya dad'e, zamu aikata abinda ka umarce mu yanzu, ka yafe mana zamu yi."
"Aliyu ya saka ku kawo ta nan?" Ya fad'a a tausashe cikin muryar sa mara hayaniya wacce bata fita sosai yana kallon su.

       Sai a sannan suka gane bafa Aliyu ne a gaban su ba babar giwa ce da kanta sai jikin su ya k'ara kaimi wajan tsuma d'aya yace, "Kayi mana aikin gafara ranka ya dad'e. Yarima Aliyu ne ya umarce mu da mu kawo ta nan mu sakar mata Bobby ya cize ta sannan muyi abinda muke so da ita. Mun tuba wallahi baza mu sake aikata hakan ba." Kai Asad yake girgizawa kaf yasan plan d'in nasu sune da Aliyun basu san ya sani bane amma tunda yasa a fara tracking d'inta yasan da haka.

Kallon da yayi musu ya saka jiki su rawa suka fara fad'in, "Kiyi hak'uri yarinya muma ba san ran mu bane ba wallahi saka mu akayi babu yadda zamu yi, kiyi hak'uri ki yafe mu." Kanzil Rauda bata ce ba sai kuka da take mai tsuma zuciya ya sake kallon su duk sai suka sake diriricewa dan basu fahimcin kallon na meye ba.

D'aya ne ya mik'e da sauri ya kawo mata sandinan ta guda biyu yace, "kiyi hak'uri." Da hannu yayi musu alamun da su wuce su tafi a da sauri suka hau mota suka ja da gudu. Dawo da kallon sa yayi kanta yadda jikin ta yake tsuma tana kuka hakan ya tabbatar masa da ba k'aramin tsoro take ji ba sai ta sake bashi tausayi yana so yayi mata magana amma bai san me zaice ba.

Yana tsaye tana kuka sai da ta gaji dan kanta sannan ta fara k'ok'arin tashi tsaye, bata iya tsayuwa da k'afafun ta hakan ya saka tashi yake gagarar ta ganin sai juyi take kamar wancan lokacin ya saka shi mik'ar da ita tsaye ya bata sandar ta rik'e sai kuma ta dafe kai da hannayen ta guda biyu jin yadda yake sarawa. Bata daina kuka bai kuma ce komai ya juya wajan motar sa ya shiga karen shiga mazaunin baya ya dawo da motar daidai kusa da ita amma har lokacin bai ce k'ala ba.

Wajan take kallo babu alamun abin hawa in tak'i shiga motar ta cuci kanta dan bata san a inda take ba balle tabi hanyar da zata sami mota, tana so ta shiga amma rashin yi mata magana da baiyi ba ya saka take shakka kar ta shiga ya wulaqanta ta.

      Sauke glass d'in gefen ta yayi da hannu yayi mata alama da ta shiga a sanyaye ta ja handle d'in motar ya bud'e, so take ta fara saka sanda guda d'aya sannan ta shiga sai ta shigo da d'ayar amma ta kasa ta rasa yadda zatayi. Babu tsammani taga ya fito daga motar ya dawo inda take ya karb'o guda d'aya ya saka a ciki ta saka k'afar ta mai lafiyar ta shiga cikin motar, saka mata d'aya sandar yayi kana ya kulle k'ofar ya zaga ya shiga.

Ganin ta yayi duk a tsorace tana kallon baya ya juya yaga Bobby ya san shi take jin tsoro bai ce komai ba yaja motar. kuka take cigaba da yi tana goge idanun ta har lokacin jikin ta bai daina rawa ba shi kuma bai ce mata ci kan ki ba tuk'i yi a nutse. Kukan ya dame shi har tsakiyar kansa yake jin kuka amma bai san me zaice mata ba shiyasa yayi shiru ya jure abinda yake ji ya cigaba da tafiya.

Ba tare da tayi zato ba taji sun tsaya tana d'ago kai ta gan su a k'ofar gidan su d'an hasken kwan solar da ya haske wajan gidan nasu duk da babu wani haske sosai amma dai yafi babu ya haska wajan, kallon sa tayi ta kalli gidan nasu ta tabbatar fa nan ne mamaki da tsoro suka yi mata yawa tunanin ta a ina ya san gidan su?.

"Kina da Yaya?." A sama taji maganar tasa ta juyo ta kalle shi sai taga kamar ba shine yayi maganar ba dan bama ita yake kallo ba. Idanu ta goge ta girgiza kai alamun a'a kafin tace, "Bani dashi."
"Mahaifi?" Ya sake fad'a bai kalle ta ba har lokacin.
"Ina dashi" ta bashi amsa muryar ta na rawa sosai.

Sai da ya kusa kwashe sakan hamsin sannan yace, "kice ana sallama dashi" ya fad'a yana danna lock d'in motar ta bada sautin k'ut alamun ta bud'e. "Na gode. kayi hak'uri da abinda na fad'a maka a baya ban san kai bane ba, ka bawa d'an uwan ka hak'uri ya fita a rayuwata nasan nayi kuskure duk da laifin sane amma na karb'i laifin." ta fad'a murya na rawa sosai.
Yadda maganar take rawa shine ya jawo hankalin sa ya kalle ta yaga yadda hawaye suke ambaliya daga idanun sa sai yaji rauni ya sake mamaye ko ina na jikin sa zuciyar sa na harbawa da sauri-sauri wani abu nayi masa yawo tun daga yatsan sa har cikin kansa.

"Allah ya saka maka da alkhairi ya biya maka dukkan buk'atun ka na duniya, na gode ka taimake ni Allah ya taimake ka kai ma" ta sake fad'a tana bud'e motar ta saka sandar ta sannan ta sauka ta d'auki d'ayar ta kulle motar ta nufi cikin gidan su. Da kallo ya bita yana kallo ta cikin wani abu mai kama da kewa a zuciyar sa da shauki wanda bai tab'a jin makamancin sa ba a kan kowa sai ita kawai, duk takun da zatayi sai zuciyar sa ta buga hakan ya saka shi dafe zuciyar sa yaji tana harbawa a guje kamar zata faso k'irjin sa ta fito.
Gidan yaga ta shiga ya sauke numfashi yana k'arewa gidan kallo tausayin ta na sake ninka na baya a zuciyar sa.

        A can gidan kuwa ana ganin shigar ta Umma ta mik'e tana fad'in, "Alhamdulillah! Malam gata ta dawo" ta fad'a tana nufo Rauda da idanun ta suke cike da kwallah har lokacin. Rik'e ta tayi tana kallon fuskar ta tace, "Rauda ina kika tsaya? Meya faru kike kuka?." Tare suke tafiya har suka k'arasa kan kujerar da take zama ta zauna Umma ta kalli Khairi tace, "Kawo mata ruwa."
Da sauri ta tashi ta kawo ruwa a kofi Umma ta bata tasha ta sauke numfashi hannun ta dafe da kanta da yake mata ciwo.

Baba yace, "Sannu Rauda, daga ina kike Shamsiyya ta sanar dani tun la'asar kika baro gidan ta gashi har anyi i'sha yanzu?." Numfashi take yi kafin tace, "Baba ana sallama da kai a waje." Baba yace, "Waye yake sallamar?."
"Wanda ya taimake ni" ta fad'a tana haki jin hakan ya saka Baba fita bai kuma cewa komai ba.

       "Ummulkhairi kawo mata abinci taci" Umma ta fad'a tana kallon Khairi. Mik'ewa Khairi tayi ta d'auko mata abinci ta kawo mata ta karb'a ta bud'e dan taga meye a ciki, shinkafa ce da miya ta sauke numfashi tunda Anas ya aiko musu da abinci suke ci suke sha a gidan shiyasa take bashi babban matsayi a zuciyar ta.
Kad'an ta fara cin abincin duk jikin ta babu dad'i haka ta fara ci gaban ta sai fad'uwa yake ba tare da tasan dalilin faruwar hakan ba.

        Shigowar Baba da sallama ya saka suka amsa har ya k'araso ya zauna ya kalle su dukkan su har da Inna da Rahma yace, "Yayan wanda ya kad'e Rauda ne. abin mamakin y'ay'an sarkin katagum ne." A tare k'irjin su ya buga har da ita Rauda d'in dan bata san waye ya buge ta ba daman. Umma tace, "ko da naji, yadda yaron da ya buge ta yake da izza kana kallon sa kasan jinin sarauta ne."
Baba yace, "tunda ya buge ta ranar da ya dawo da safe ya kwanta ciwo har yanzu bai farfad'o ba yana kwance, shi wannan d'in yayan sane duk da kamar ana masa dole in yana magana har wani yatsine fuska yake yi yace min yana so a madadin k'anin sa zai saka ayi mata aikin k'afar ta a waccan k'asar ta larabawa meye ma sunan ta...." ya fad'a yana yin shiru alamun tunani.

"Yauwa Misra, gobe zai aiko a d'auke ta a kai ta can ofishin da ake yin fasko na tafiya ayi mata cikin satin nan yake so ayi mata aikin. Yace kuma na baku hak'uri bai san da mara lafiyar da wuri ba da tuni anyi mata magani." Umma da take sauraren sa ta sauke numfashi tace, "Shi ya akayi yanzu ya san da ita?." Baba ya kalle ta yace, "Ai bazai miki k'arya ba."
"nidai Malam ina jin tsoro aikin baza'a yi a k'asar nan ba har sai anje Misra? Kuma haka zamu bada ita daga shi sai ita aje ayi mata aiki muna nan baki sake?."

Baba yayi shiru da alama duk kwadayin sa shima maganar bata shige shi sosai ba yace, "To nema mata lafiya za'ayi ai, kamar kuma kin san abinda yace dan ya fad'a a bada babba guda d'aya ko mace ko namiji da za'a tafiyar tare kin ga kenan ya san abinda yake yi. Kuma kina kallon sa kin ga fuskar sarki Sa'ad yadda ya fad'a min sunan sa Asad yafi kowa hankali da ilimj a gidan sarki, kowa ya sanshi da a k'asar saudia yake da zama bai jima da dawowa ba shiyasa na amince da maganar sa tunda nema mata lafiya za'ayi kuma daman sune da hakkin hakan."

Umma dai bata kuma iya cewa komai ba ta ja bakin ta tayi shiru. Rauda kuwa sabon tunanin ta afka cikin mamaki da al'ajabi kenan daman yasan d'an uwan sane ya buge ta shiyasa yake k'okarin taimakon ta koda yaushe? Ya akayi yasan nice wacce d'an uwan sa ya buge? Ya akayi ya nemo ni yasan nice har ya san gidan nan?. Babu mai bata amsa sai ta ajjiye abincin dan ya fita daga kanta kuma ta tashi ta shiga d'aki tana shiga ana kawo wuta gidan ya haske d'akin nasu fanka ta fara kad'awa mai sanyi.

         Duk watsewa akayi daga tsakar gidan Umma ta biyo bayan ta tace, "Rauda a ina kuka had'u dashi wannan d'in? Wanne taimako yayi miki yau?." Bata b'oyewa Umma ba ta fad'a mata komai har k'arshe Umma ta jinjina kai tace, "Ikon Allah! Kinga illar rashin kunyar ki da nake fad'a miki ko? Yanzu badan shi yazo ba da me kike tunanin zaiyi miki....?." Rauda ta sunkuyar da kanta k'asa Umma ta kuma cewa, "Ki dinga fad'a har da maza akan wani abu kalilan wanda bai kai ya kawo ba, meye dan ya mare ki a gidan sarki basai ki manta anyi hakan ba tunda kin san yafi k'arfin ki...?. Har da kuka kuma had'uwa wai sai kika ce masa mahaukaci da yake bakya gudun abinda zai je ya dawo. Yanzu me gari ya waya da ya saka karen ya yaga naman ki sun kuma yi miki fyad'e fa?."

Rauda a sanyaye tace, "Umma Allah ya rubuta faruwar hakan ne kawai." Umma tace, "Koma dai meye ke kika ja ai. kenan y'an ukun da ake zance akwai su a shigan sarki kin shiga rayuwar su dukka su ukun. to Allah ya kub'utar dake daga sharrin babban shi kuma wannan da ya taimake ki Allah ya saka masa da alkhairi, d'ayan kuma Allah ya bashi lafiya. Ke kuma nan gaba sai ki kama kanki." Da amin ta amsa a ciki ta shirya ta kwanta zuciyar ta cike da tunane-tunane.

*☆☆☆*

        B'angaren Asad tunda ya bar k'ofar gidan su Rauda inda ake ajjiye karnukan ya kai Bobby ya ajjiye sannan ya nufi gida kamar koda yaushe. jin zuciyar sa yake da dad'i babu dad'i, in ya tuna yayi magana da iyayen Rauda akan ciwon ta sai taji dad'i a ransa, in kuma ya tuna da wani abun sai gaban sa ya fad'i a haka har ya k'arasa gida.
Yana shiga B'angaren su ya samu Aliyu a zaune yana wuci yana shiga ya mik'e ya tare masa hanya yace, "Waye ya baka ikon hana yiwa wacce na saka a yiwa hukunci?."

Asad ya kalle shi kamar zai magana sai kuma ya fasa ya rab'a ta d'aya gefen zai wuce Aliyu ya sake tare shi yace, "Magana nake maka Asad, me kake ji dashi har da zan yi hukunci ka saka a warware?." Asad ya kalle shi ido cikin ido yana juya nasa idanun yace, "Sabida baza'a yi d'in ba."
"Har kai ka isa!, me kake ji dashi da zaka hana ni abinda nayi niya?. Wacece ita a wajan ka da zaka hana ni d'aukar mataki?."
"Special one" ya bashi amsa a tak'aice yana wuce shi ya shiga d'aki ya bar shi a tsaye baki bud'e yana kallon sa.

"Special one? Me yake nufi?, kenan ta musamman ce a wajan sa?. In na fahimta daidai kamar wata ce a wajan sa ko wacce yake so?." Sai kuma ya dafe kansa yace, "A'a Aliyu this is not possible kawai akwai dalilin nasa nayi hakan, tunda har kuwa baya so koda nayi niyar na rabu da ita na fasa, yanzu na fara sakawa a hukunta ta indai hakan zai b'ata masa rai shine fatana" yana fad'a ya fita daga falon da sauri.

      Asad kuwa wanka yayi ya saka kayan bacci ya fito zuwa falo, yunwa yake ji amma bazai iya cin abincin da ya gani a ajjiye ba haka kawai zuciyar sa bata yarda ba ya fita zuwa apartment d'in Mama. Bai same ta ba daman ba wajan ta yazo ba ya shiga ciki yaga abinci ya zuba yaci yarda yake so sannan ya tashi ya shiga ya duba Hydar ya koma.

Koda ya koma d'akin sa kalmar da ua fad'awa Aliyu ce ta fad'o masa zuciyar sa, ya tsaya a jikin madubi yana kallon kansa a bayyane yace, "Da gaske special one ce?." Sai kuma ya murmusa sosai har hak'oran sa suka bayyana ya shafa gemun sa ya zauna a gafen gadon yana jin muryar ta mai sanyi tana sake rantsa dodon kunnen sa. Ido ya lumshe tunawa da ta bashi hak'uri sai yaji zuciyar sa tayi fess ya dinga murmushi shi kad'ai a haka har ya kwanta yayi bacci.

       Washe gari da misalin k'arfe goma na safe ake kwad'a sallama a k'ofar gidan su Rauda, Baba ya fita ba jimawa ya dawo ya kalli Rauda da take zaune tayi wanka yace, "gashi yarima ya turo zaku je, ki d'auko katin d'an k'asar ki kema ki d'auko naki kuje ke ya kamata ku tafi tare in tafiyar ce" ya fad'a yana Kallon Umma. Umma tace, "Ni da nace cikin yayen ta suje da guda d'aya."
Baba yace, "Duka su kad'ai ne wajan mazan su basa yi doguwar tafiya irin wannan ba. ke dan fa aikin jinya za'ayi da wallahi bazan neme ki ba ni zanje kodan na kashe kwarkwatar idanu na, to jinyar mace sai mace ki tashi ki d'auko ku tafi ana jiran ku."

Umma ba dan taso ba ta tashi ta saka mayafi ta d'auko katin d'an k'asar ta fito tana fad'in, "Amma malam kyau kaima kabi mu muje tare." Baba yace, "wannan a rubuce yake ai ba sai kin fad'a ba, d'an sarki fa da kansa wanda mai martaba yake ji dashi. na san abinda zai kunso muku ai gwraa naje nima." Umma ta kalle shi cikin takaici jin badan tsare lafiyar su zai je ba dan abinda za'a samo ne.

Inna da ta lek'o daga d'aki tana kallon su tace, "duk wanda ya hau motar kwadayi zata juye su a tashar wulaqanci, daga uwar har uban har y'ar." Ba wanda ya tanka mata suka fita. Suna hango su jiki na rawa suka bud'e musu mota su uku a baya aka ja suka tafi.

        Da yake abu ne na manya an sanar da komai suna zuwa aka fara yi musu ashe Baba ma da nasa katin ya tawo wai bai san inda rana zata fad'i ba, kafin azahar an gama musu fasko an awa ashirin da hud'u zai fito da yake na manya ne babu b'ata lokaci. Suna baro wajan d'aya daga cikin dogaran ya kalle su yace, "Mai girma yarima Asad ya umarce mu da in mun gama mu kai ku inda zaku ci abinci sannan a mayar daku gida, yanzu zamu k'arasa wajan in zaku shiga ciki sai muje in zuwa za'ayi a kawo muku duk d'aya ne."

Kafin Baba yace wani abu Umma tace, "A'a ba sai muje ba mu wuce gida hakan ma mun gode."
"A'a ranki ya dad'e, yarima  Asad bazai ji dad'i ba in muka ce masa bamu je ba, ku daure muje sai a kawo muku nan."
"Babu damuwa" Baba ys fad'a da sauri suka cigaba da tafiya. Gaban babban gidan abinci suka tsaya kafin na gaban yace, "ranku ya dad'e me za'a kawo muku?."
"Duk abinda ya samu" Umma ta fad'a kawai suka amsa da to suka fita.
Basu jima sosai ba suka dawo da ledoji manya suka shigo motar suka mik'a musu sai khamshi ne yake tashi sannan suka wuce gida, sai da suka har gida sun shiga sannan suka wuce.

*☆☆☆*
            A zaune ya samu Mama kusa da godon Hydar ya shigo tana ganin sa tace, "Asad Hydar ya motsa yau da alama yana gab da farkawa" ta fad'a cikin nishad'i tana kallon sa. Murmusawa yayi kad'an ya k'arasa kusa da gadon yana kallon sa.
"Sadiya ta kira ni tace min kaje jiya naji dad'in hakan" ta furta a tak'aice tana kallon sa. Numfashi ya saukar a hankali yace, "kiyi hak'uri Mama, amma bata dace dani ba."
"Ta dace dakai Asad ita na zab'a maka ita nake so ka aura."
"Tohm Mama" Ya furta yana juyawa ya fita daga d'akin gabad'aya.
Yana fita mota ya d'auka ya fita daga gida.

       Gidan da ya saba zuwa yaje ya zauna shi kad'ai yana tunanin da ya saba kansa a kulle kamar ko yaushe. idanun sa a kulle yana zaune ko motsin kirki bayayi babu abinda yake ji a zuciyar yake kuma gani sai Rauda ba tare da yasan dalilin hakan ba kawai ji yake zuciyar sa na motsawa a kan hakan. Ya sauke numfashi mai k'arfi ya tashi zaune sosai yana mutstsika idanun sa, jinin jikin sa yake ji tana shiga ko ina ya rasa gane tausayin ta yake ji sabida ta rasa k'afar ta ta dalilin Hydar ko kuma me? Bai sani ba bai san meyasa yake ganin ta always ba ko yaya ya kulle idanu ita yake gani; ya kasa banbance itace ta mafarkin sa ko ba ita bace?.

"RAUDA!" ya furta a bayyane yana jin wani iri a jikin sa gashin  jikin sa na rinsing ba tare da ya san dalilin hakan ba, wayar sace ta d'auki k'ara ta katse masa tunani ya kalle ta yaga sunan Hafiz ne yayi banza bai d'auka ba aka kuma kira ya kalla yaga d'aya daga cikin wanda ya saka su kai su Rauda ofishin yin fasko d'in ya d'auka, "Ranka ya dad'e, Allah ya taimaki yarima, Allah ya ja zamanin ka, ya baka tsahon rai ya taimake ka a duk inda kake."
"Uhum" ya furta kawai ba tare da yace komai ba.
"Ranka ya dad'e anyi abinda kace, yanzu haka mun sauke su sun shiga gida."
"Good" yana furta hakan ya katse wayar bai tsaya yaji mai zasu ce ba.

Lumshe idanu yayi ya tuno lokacin da take hawaye tana masa godiya sai yaji kasala ta saukar masa ya koma ya kwanta a akan kujera yana jin wani irin yanayi a jikin sa.
'You love her' yaji zuciyar sa ta furta hakan ya saka shi saurin tashi ya bud'e idanun sa yana ji zuciyar sa na gasgata masa abinda ta fad'a.

"A'a ba haka bane" ya furta yana cize bakin sa.
'Da gaske Asad haka ne ka yarda.' zuciyar sa ta sake fad'a ya dafe kansa da duka hannayen sa jin yana juya masa. Tashi yayi ya d'auki makullin mota ya fita daga gidan da sauri jikin har shaking yake yi.

*☆☆*

        "Uncle ka kira ni then kayi shiru ina da abinda zanyi" Aliyu ya fad'a yana kallon waziri da yake zaune yana facing d'insa. Numfashi ya sauke yace, "Wato Aliyu abubuwan ne suke d'aure min kai, ace kamar ka babba kaine namijin farko da mai martaba ya samu amma a dinga mik'a sarauta ga k'anin ka?. Kasan jiya mai martaba ya zauna da Asad kuma ya tabbatar masa da shine zai mulki garin nan?."

Kafin Aliyu yayi magana yace, "ga kyau, ka k'ima, ga k'asaita, ga nagarta, ga izza, ga ilimi, ga wayewa, ga sanin ya kamata. Waye ya cancanci zama sarki in ba kai ba?. Kai ka san ina son sarautar nan amma sabida dacewar ka ya sanya na hak'ura na sallama; ranka ya dad'e wallahi inda zaka zama sarki zan cigaba da zama matsayin wazirin ka amma meyasa mai Martaba yake fifita Asad a kan ka? Meyasa kowa maganar sa a akan Asad take sab'anin ka?."

Zuuuuu haka Aliyu yake jin k'asaita da zugar da ake masa na shiga cikin jikin sa, kansa yake ji a sama kamar shine yake mulkin duka duniya, wani irin yarrrr yake ji a jikin sa har bai san ya cize bakin sa ya kalli Waziri yace, "Kana so kace min kana bayana? Kana so kace min kaima ni kake so na zama sarki a garin nan kenan?."
Murmushi waziri yayi yace, "Dari bisa dari, ni daman kaine nawa ai tun kana k'arami ba Asad ba, in kana musawa ka tambayi mahaifiyar ka zats baka labari."
Wani irin kallo Aliyu yake masa na ka raina min hankali amma sai ya murmusa yace, "Ta yaya zan yadda bayan kaima kana harin mulkin nan?."
"A bayyane yake ai ranka ya dad'e, indai kai zaka mallaka wallahi nidai na hak'ura."

Murmushi Aliyu yake na kana mayar dani yaro k'arami bai ce komai ba ganin murmushin da yake yi sai Waziri yace, "shine nace me zai hana baza mu samo mafita ba; matuk'ar Asad ya mallaki garin nan shiga gidan sai ya gagare mu, ya kamata mu san abinda zamu yi."
"Ina jinka."
Ya gyara zama yace,"Na shirya wani abu a raina amma ban sani ba ko zaka amince."
Da hannu yayi masa alama da yana jin sa.

Gyara zama ya sake yi yace, "Daman mafita ce na nemo amma ina jin shayin fada maka." Aliyu ya d'ora k'afa kan d'aya yana kad'awa yace, "Go ahead."
"Daman cewa nayi mai zai hana mu b'atar da Asad ya bar k'asar nan ma'ana ayi masa abinda bazai sake waiwayo mu ba, kai kuma sai ka koma acting d'in Asad a fad'awa duniya Aliyu ne ya b'ata ba Asad ba. Ni da kai mun san Aliyu ne yake nan amma duniya za'a ce mata Aliyu ne ya b'ata; kaga mai martaba zai mallaka maka mulkin katagum a matsayin Asad kaga shikenan ciki lafiya baka lafiya."

Wani irin kallo Aliyu yake masa gaban Waziri sai fad'uwa yake yi yana b'oye tsoron sa babban burin sa kar yak'i amincewa da batun sa hakan ya saka tsoro ya bayyana k'arara a tare dashi duk da yana so ya b'oye amma hakan ya gagara sai da tsoron ya kwanta a fuskar sa. Numfashi Aliyu yayi kafin ya saki dariya mai d'auke da izza da k'asaita kafin ya kalli waziri yace.......

Continue Reading

You'll Also Like

1K 146 16
The legendary story about the mysterious hidden🌄🌄 island the numerous of people and evils fails to find out about it. But find by the unremembere...
KASHI By stuckinatale

General Fiction

398K 19.9K 42
"So, Mrs. Kashi Abhay Pratap Singh..chalte hai. Goodbye..". Saying this, he left her broken in this world of betrayal. ~~~~~~~~~~ Kashi, a simple gir...
1.5M 129K 62
RATHOD In a broken family, every person suffers from his insecurities and guilt. Successful in every field but a big failure when it comes to emotio...
44K 1.5K 5
Is all about, love, sacrifice and Royal👑