KWANTAN ƁAUNA

By Nana_haleema

2.3K 136 17

Izza, mulki, k'asaita sun tattara a gare ta ita kad'ai. Y'ar sarki ce, jikar sarki, matar sarki. Bata k'aunar... More

001
002
003
004
005
006
007
008
009
010
11
012
013
014
015
017
018
019
020
021
022
023
024
025
Trailer
KWANTAN ƁAUNA Book2

016

73 6 0
By Nana_haleema

*KWANTAN ƁAUNA*

             ©️ *Nana Haleema.*

*Book 1*
*016*

        Yarda take jin gaban ta yana fad'uwa shima haka yake ji bai mata magana ba kuma bai d'aga glass d'in motar sama ba balle ya bar wajan yana tsaye har lokacin ko motsi bayayi. kanta ta sunkuyar k'irjin ta na bugawa duf, duf, duf, kamar wacce tayi gudu mai nisan zango tana raba idanu a k'asa tana ji kamar ta tashi ta gudu daga wajan. Ya bud'e baki zai yi magana sai kuma ya fasa ya d'aga glass d'in motar ya ja motar ya bar wajan a guje.

          Nannauyar ajiyar zuciya tayi har da dafe k'irji jin ya tafi ta bi motar da kallo har lokacin k'irjin ta bugawa yake yi tace, "Ni Rauda na shiga uku, na d'auko abinda yafi k'arfi na" ta fad'a tana haki har lokacin tana kallon inda motar ta bi.
"Ke kuma zaman me kike a nan?" Aka fad'a daga gefen ta ta kalli inda taji maganart aga Habiba da Walida sai taji dad'i a ranta tana k'okarin mik'ewa suka zo suka kama ta ta mik'e tsaye.

      "Bari kawai gidan gaiswar can zan je fa har na shiga layin naga maza shine zan koma gida an jima Khairi ta rako ni." Habiba tace, "Mu ma can zamu je ai yanzu, muje to." Ba musu suka jera suna tafiya a hankali sabida yanayin tafiyar ta. Waiwaye suka ga tana yi suka juya suma suka babu abinda take kallo Walida tace, "Wai me kike nema ne?."
Bata amsa ba suka cigaba da tafiya har suka shiga cikin gidan rasuwar.

Ba jima suka fito bayan sun yi mata gaisuwa sunyi nisa da gidan Walida tace, "Oh yanzu in kin ga an cika a rasuwa to gidan mai kud'i ne an san za'a ci a sha, in iyayen mu suka rasu ko wani namu babu wanda zaki gani amma nan da yake akwai kud'i kalli motoci da maza dan Allah."
Habiba tace, "Ai yanzu daman in kin ga gidan rasuwa ya cika to tabbas akwai wani babban mai kud'i a gidan, ki duba irin abincin dake fitowa dashi fa kamar gidan biki ga kaji ga naman rago ga kuma ruwa da lemo kamar bikin gidan gwamna. Har da gwamna fa akayi jana'iza d'azu."

Walida tace, "An ce sarkin garin nan ma dashi akayi." Habiba tace, "A'a yanzu fa daga gidan sarkin nake bai zo ba baya jin dad'in amma ya turo wakilan sa Asad da Aliyu. Kuma shi ai yana da k'okari wallahi ko ba masu kud'i ba yana zuwa jana'iza, ki tuna ta gidan su Salima da baban su ya rasu shine ma ya ja sallar gawar, yanzu ne ance baya jin dad'i shiyasa ya turo wakilan sa kuma na jiki."

Jin hakan sai gaban Rauda yayi mugun fad'uwa ta kalli Habiba tace, "Waye Asad a y'ay'an nasa waye kuma Aliyu?." Habiba ta kalle ta tace, "ke dai kina son labarin gidan sarkin nan. Aliyu shine babba shine baya ji bashi da mutunci ko kad'an bai d'auki talaka a bakin komai ba, shine ya mare ki ranar nan badan nayi masa wannan kirari ba wallahi sai yace a kai ki ki share turken dokunan da kike jin tsoro kuma wallahi sai kin yi in ba haka ba a zane ki" ta fad'a tana kallon Rauda ta cigaba da fad'in,

"Bashi da mutunci ko kad'an ya raina talaka ganin talaka yake kamar ba mutum ba, in fa ya tawo bayi ko dogarai suka tawo wallahi sai kin koma can baya duk nisan wajan ya wuce sannan zaki wuce, ga shi kowa ya shaida a gidan shaye-shaye yake da neman mata shiyasa basa shiri da mai martaba. Naji ance a da yafi son Aliyun amma rashin jin sa ya saka ya fita a ransa tunda yayi yayi Aliyu ya shiryu yak'i kullum sake wastewa yake yi, gashi baya yafiya ko kad'an. akwai wani labari da naji y'ar sarkin Zamfara tayi masa rashin kunya ya saka aka d'auko masa ita yayi mata fyad'e na wulak'anci ya azabtar da  k'arshe yarinyar rasa ranta tayi, amma da yake babar sa ba kanwar lasa bace wallahi tuni an manta da maganar."

Habiba bata kula da halin da Rauda ta shiga ba tace, "Asad kuma shine Kamili mai kirki duk da baya fara'a amma kowa ya shaida a gidan nan shine ya fita zakka kamar ba jinin sarauta ba in yayi miki wani abun, bazai ga ana wulak'anta d'an adam a gaban sa ya k'yale ba, bazai ga ana cin zarafin wani a kyale ba, shiyasa ko hukunci Aliyu ya saka a yiwa wani da sun ga Asad zasu daina domin tasu tukunyar ce zatayi zafi a wajan sa. Ga taimako ko a hanya yaga tsoho zai tsallaka titi Asad yana iya parking mota ya fito ya tsallakar dashi ya bashi kud'i sannan ya koma mota yaje inda za shi, labari in yaji na gidan ku baku dashi ko kuna neman wani taimako sai ya taimaka muku wallahi, wani lokacin baza ma kusan shine yayi ba. Kuma kaf gidan nan babu mai kud'in sa hatta mai martaba bashi da kud'in da Asad yake dashI, sai dai mai martaba ya nunawa Asad kadarori amma zunzurutun kud'i Asad ne yake dashi tunda shi bada Nigeria yake aiki ba. Kullum fa sai ya bawa su Gwaggona dubu d'aya sadaka, sama da mata d'ari a gidan nan kowa sai ya samu yara da manya, in kana da buk'ata ma in Allah ya had'a ku ka nemi taimakon sa an gama shiyasa kullum yake gaba baya b'ata yin baya a rayuwar sa."

"Shi bar shi da baya magana dan ya kwana uku ma bai fito daga d'aki ba abu ne mai sauk'i a gare shi tunda ba zaman k'asar yake so ba, duk inda kike tunanin miskili mara son magana da hayaniya ya wuce nan, shiyasa y'an gidan da dama kurma suke ce masa domin ance sai su zauna meeting na cikin gidan su a tashi bai ce kanzil ba, sam baya k'aunar magana shi yafi son shiru shiyasa ko gaishe ki kayi a hanya sai dai ya d'aga hannu in yaga dama yayi murmushi. Amma fa naji ance duk tsiyar Aliyu in Asad yayi fushi bai kama k'afar tasa tsiyar ba, ance duk ya fisu zafi ta Aliyu ce ta bayyana."

Walida tace, "shi na ukun fa?." Habiba tace, "Hydar kenan gidan fara'a, shine kuma basa kama da y'an uwan in kika ganshi ma baza kice y'an ukun su bane, wad'ancan sune masu kama kwabo da kwabo kika ga Asad kika ga Aliyu baza ki banbance ba. A da adon gemu ne yake banbanta su na Asad bak'i ne sosai na Aliyu kuma ya shirka da ja, cikin kwanakin nan shima ya mayar da nasa bak'in kafin ki gane su zaki sha wahala. Hydar halin su d'aya da Asad kawai shi yana da wata cuta ce da in ta tashi sai ya shafe wata a kwance kamar yadda na fad'a muku ranar nan, yanzu haka ma ciwo ya tashi yana kwance ya jima ance ko motsi baya yi."
"Allah sarki Allah ya bashi lafiya."
"Amin. Ke Rauda lafiya kike kuwa?" Habiba ta fad'a ganin kamar ta fita a hayyacin ta.

Rauda ta firgita ta kalle su hawaye ya wanke mata fuska tace, "fyad'e kika ce ya yiwa wata dan tayi masa rashin kunya fa, kuma y'ar uwar sa mai kud'i da mulki; Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, Habiba na shiga uku ni yanka ni zai saka yi, bakina ya jawo min abinda yafi k'arfin dangin mu gabad'aya." Walida da mamaki tace, "Me kike nufi?."
Sai kuma Raudan ta saita nutsuwar ta  tace, "Wai da ranar da ya mare ni na tanka masa."

Habiba tayi dariya tace, "ke me zai had'a ki da wannan? Yadda ya raina talakawa wallahi Allah kad'ai yasan mai zai miki. Banza matsoraciya shine har da kuka?" Ta fad'a tana kallon ta sukayi dariya ita da Walida. Habiba ta kuma cewa, "kuma baku san wani abu ba, a kaf gidan babu mai taka masa burki kamar Asad d'in, basa shiri fa amma kamar ba y'an uku ba sam Aliyu da Asad basa jituwa amma kuma in ya tsawatar akan abu ance Aliyun yana shayin aikatawa, dan Asad akwai slicent treatment."

Walida tace, "Ke wai a ina kike jin wannan labaran?."
"Ina fa kwana a gidan, kuma kin san labarin gidan sarauta baya tab'a b'uya ko me aka aikata sai ya bayyana."

        Basu lura da yanayin ta ba suka cigaba da tafiya har aka zo gida Rauda ta shiga gida suma suka wuce nasu gidan. Umma na zaune taga shigowar Rauda a gigice ta bita da kallo tace, "ke kuma lafiya?." Jikin ta har rawa yake tace, "babu komai Umma" tana fad'a ta shiga d'aki ta zauna gefen gadon Umma ta ajjiye sandinan ta a gefe kawai ta fashe da kuka.

"Na shiga uku ni Rauda na jawowa kaina bala'i" ta fad'a a hankali gudun kar Umma taji. Bugawa k'irjin ta yake cikin tsoro da fargabar abinda zai je ya dawo hankalin ta ya mai k'arshe wajan tashi k'irjin ta har d'agawa yake sabida tashin hankali.
Umma da ta d'aga labule ta shigo ta kalle ta tace, "Ki sanar dani abinda yake damun ki."

       Kuka take sosai bata ce komai ba Umma na tsaye tana kallon ta ganin yadda take kuka sosai sai tayi mata shiru tana kallon, sai da ta gaji da kukan sannan ta kalli Umma tace, "Tausayin kaina nake Umma lokaci guda na nakasa." Umma ta girgiza kai tace, "Wani lokacin kamar bake ba, kina mantawa da Allah yana canjawa bawa halittar sa komai tsufan sa, indai ba mutuwa kika yi ba'a gama canja miki halitta ba. Indai baza kiyi imani da k'addara ba kuka yanzu kika fara" ta fad'a tana komawa da baya ta barta.

Kwanciya Rauda tayi cikin tashin hankalin da ya hana zuciyar ta sukuni, hangowa take ya saka an kamo ta itama anyi mata fyad'e kuma an kashe ta lokaci d'aya sai taji hankali ta ya kuma tashi. Tana kuka bacci ya d'auke ta bata sani ba.

*☆☆☆*

         Tunda ya shiga falon Mama ya zauna bai ce kala ba ganin hakan sai Mama ma ta share shi ta cigaba da danna wayar ta dan duk a tunanin ta Asad ne ba Aliyu ba, shigowar Asad ya saka ta kalle shi taga fuskar sa tayi kama da ta Asad ta dawo da kallon ta ga Aliyu taga sak iri d'aya dai ta Asad d'in ce a d'aure ko wanne da alamun b'acin rai a tare dashi.
Sanda Asad ya zauna lokacin ta kalle su ta ajjiye wayar a gefe tace, "Ikon Allah." Nan ma babu wanda ya tanka mata a cikin su sai suka sake rud'a ta.

"Lafiyar ku kuka shigo min ko wanne fuska a d'aure? taz'aziyar da mahaifin ku ya tura ku kenan?."
Nan ma shiru babu amsa ko wanne na kallon wani wajan daban sai suka fusata ta tace, "Malamai bakwa ji ina muku magana ne? Wanne irin iskanci ne wannan ina magana kunyi banza dani kamar sa'ar ku?. Ku banbance min kan ku tunda kun d'auko sabon iyayin saka kaya iri guda, banbancin ma da yake fuskar Aliyu ya shafe shi."

Tab'e bakin da Aliyu yayi ya skaa ta kalle shi tace, "Kaine Asad kenan" sai ta kalli Asad taga bama ita yake kallo ba nan ta sake rud'ewa dan gabad'aya ko wanen su acting d'in Asad yake yi. Ganin ranta ya fara b'aci ya saka Asad yace, "Allahbya wuci zuciyar Mama, ya jikin Hydar?." Yana fad'ar hakan sai ta gano waye dan Asad yafi damuwa da jikin Hydar akan Aliyu daman kuma tun farko tasu tafi zuwa d'aya, ta kalli Aliyu tace, "baku tab'a rud'a ni kamar yau ba, kamar ku ta fito a zahiri sosai har ta bani tsoro tabbas Aliyu ka koma min Asad a yau."

Aliyu yace, "ina neman izinin magana." Mama tayi masa alama da hannu yace, "Mama wata yarinya ce ta kira ni da mahaukaci a wajan ta'aziya amma Asad ya hana ayi mata hukunci. Ina rok'on Mamana da ta shiga tsakani na da Asad tun kafin raina ya b'aci hukuncina ya shafe shi, babu ruwan sa da duk abinda zan saka ayiwa wani a k'asana yake tunda talakan garin nan ne." Mama ta bud'e baki tace, "What? Mahaukaci! kaine mahaukacin?." Basu amsa mata ba tace, "y'ar gidan uban waye?."
"Ba y'ar gidan kowa bace ba Mama, beside y'ar talakawa ce gurguwa mai yawo da sanda, sau uku kenan tana k'okarin raina min hankali amma na yau yafi na ko yaushe har ta kira ni da mahaukaci amma wannan ya hana a sake b'alla mata k'afafun ta" duk da fad'a yake amma bai fito fili ba sabida a gaban Mama yake dole ya tausasa harshe.

         A fusace Mama ta kalli Asad tace, "For what reason?. Mecece d'in ka da zaka hana a hukunta ta?." Shiru Asad yayi bai amsa ba ta kuma fusata tace, "meyasa kai baka san Allah ya banbanta ku da talakawa bane ba?, meyasa ka kasa gane kai da talaka sai dai taimako in kaga dama?, meyasa baka gane tazarar ku kamar tazarar sama da k'asa ce?. Ni y'ar sarki ce babana sarki ne, kakana ma sarki ne, miji na sarki. Baban ku sarki ne kakan ku sarki ne haka zalika a cikin ku akwai sarki. Ko a jinin sarautar naku daban yake, ko a y'ay'an sarautar ku daban kuke, ko a izza da k'asaitar taku daban take, meyasa kake mantawa da wannan Asad?!."

"Allah ya wuci zuciyar ki, amma dukkan mu bayin Allah ne babu wanda yafi wani ko a wajan Allah. Tunda har ita yarinyar tace masa haka maybe akwai abinds ya fad'a mata ta rama."

"K'arya kake Asad, ko a wajan Allah akwai banbanci tsakanin talaka da mai kud'i nasan kasan da wannan. Kuma ko zane ta yayi ai matsayin da yake dashi a garin nan godiya ya kamata tayi masa ko babu komai ta samu k'imar da har ya tsaya ya dake ta." Yadda take magana da fad'a ya hana shi sake cewa komai yayi mata shiru.

"Aliyu ko y'ar gidan uban wacece ina so ka saka ayi mata hukunci, ina so ka saka a nuna mata ruwa ba sa'an kwanbo bane sabida gaba, in ka k'yale ta wasu ma zasu gwada tunda sunga wata tayi tasha. Ka tauna tsakuwa ko dan aya taji tsoro" ta fad'a tana kallon sa. Cikin gamsuwa ya girgiza kai domin bayanin da tayi ya saka ya sake jin izza na mamaye masa jikin sa yace, "tabbas zata gane nida ita kamar wuta da ruwa ne baza mu tab'a zama waje d'aya ba, Mama zata san ni ba d'an sarkin Bauchi bane ni d'an sarkin katagum ne."
"Good boy!" Ta fad'a tana masa jinjina.

Asad yace, "Mama yarinyar nan fa ta silar....." Sai kuma ya fasa fad'a yayi shiru da bakin sa yana kallon gefe guda. Tsaki taja tace, "baka gado ni ba sam Asad, bakayi kama da jinin sarauta ba. Har wata yarinya zata kira d'an uwan ka mahaukaci a gaban ka ka hana ayi mata hukunci, ita d'in banza da wofi, ko baban tane ba sai a hukunta shi ba balle ita." Aliyu ya tashi ya fita zuciyar sa cike da tunanin hukuncin da ya dace da Rauda.

Shima Asad d'in tashi yayi ya fita dan ya lashi takobin babu wanda ya isa yayi mata wani abun indai yana raye domin kuwa ta dalilin Hydar ta nakasa, ko babu wannan dalilin a yadda ya samu labarin ta tana da hankali baza ta saurari Aliyu ba sai dai in shine ya fara zagin ta shine ta rama bai ga dalilin da zai saka a dake ta a kuma hana ta kuka ba.

*☆☆☆*

         Yadda suka nutsu suka bada dukkan hankalin su ga wayar hannun waziri zai tabbatar maka da abu nai mahimmaci ake sanar dasu a cikin wayar, motsin kirki basa yi hankalin su gabad'aya yana kan wayar sunyi shiru suna sauraron abinda ake fad'a daga cikin wayar.
"Kamar yadda na fad'a muku mai martaba ya dawo da batun bawa Asad sarauta jiya sun tattauna dashi akan maganar, wanne tunani kuka yi game da hakan?."

Suka kalli juna a tare kafin waziri yace, "bamu san hakan ta kasance ba dukkan mu mun saki jiki akan maganar ta jinkirta ne."
"To bata jinkirta ba ku fad'a min shirin ku naji."
Hajiya tace, "bamu da wani shiri sai abinda kika shirya mana."

Master planer tayi murmushi tace, "Ina da shawara sai dai shawarar tawa tana da wahalar faruwa amma zata faru in kuka jajirce." Waziri yace, "muna sauraron ki."

"Ku jawo Aliyu ya dawo cikin ku." A tare suka wara idanu Hajiya tace, "Wanne Aliyun kike nufi?."
"Aliyu nawa ne daku a gidan?."
Waziri yace, "to maganar ce na jita wani iri master kamar da kamar wuya, Aliyu fa jinin Asad ne ta yaya zai had'a kai damu."

Y'ar dariya tayi tace, "Aliyu ya fi ku son ganin babu Asad a cikin gidan nan, domin Asad shine kawai wanda yake ganin zai hana shi mulkar garin nan. In kuka samu ya dawo cikin ku ya fiku yarinta yana da matuk'ar wayo idanun sa kuma a bud'e yake tafiya zata yu yadda ake so."
Hajiya tace, "Amma in muka nemi Aliyu kamar tonuwar asirin mu ne, zai iya bijire mana yak'i amincewa bayan ya riga yaji sirrin mu."

Waziri yace, "abinda na gani kenan, inda dama a bar maganar Aliyun nan."
Master planer tace, "shigowar Aliyu shine nasarar mu."
"Ta yaya zai zama nasarar mu bayan in ya shigo cikin mu mun kashe maciji ne basu sare masa kai ba?. Kar ki manta in ya shigo cikin mu kenan mun zubar da makanan yak'in mu na neman sarauta mun barwa jinin Rabi'atu."

"Hhhh! wani lokacin bakwa saurin fahimtar inda na dosa. wato shi kan sa Aliyun amfani zamuyi dashi in mun gama burin mu ya cika mu ajjiye shi a gefe. Abinda nake nufi a nan zamu saka a b'atar da Asad amma za'a bayyanawa mutane cewa Aliyu aka batar ba Asad ba. Aliyu zai koma acting d'in Asad gabad'aya kamar yadda yake yi yanzu, zai dakatar da duk wani abu da yake yi ya dawo Asad a cikin gidan nan. Ko mahaifiyar sa bazata san bada Asad take zaune ba zai koma Asad sak babu wanda zai ce Aliyu ne. Da zarar hakan ta kasance kunga mai martaba zai bawa Aliyu mulki ba tare da yasan shi bane, mu kuma indai aka bawa Aliyun mulkin nan kwace goriba a hannun kuturu abu ne mai sauk'i a wajan mu. Wannan shine amfanin da Aliyu zai mana shiyasa nace ku jawo shi cikin ku."

Waziri ya numfasa yace, "ta yaya Aliyu zai shigo cikin mu? Shine babban tashin hankali shigowar sa cikin mu, sannan in ya shigo an gama komai an bashi mulki ta yaya Aliyu zai amince ya bar mulkin cikin sauk'i bayan kema kin shaida wayon sa?."
"Waziri kana da dawo da bara bana, nice nace zanyi ku gwada abinda nace muku ku gani in ban yi nawa ba."

Hajiya tace, "Abun ne kamar da wahala master, Aliyu fa." Ta ja k'aramin tsaki tace, "nice nace kuyi in kuka tabbatar ya shigo tsagin mu an b'atar da Asad komai zai zo mana da sauk'i, in kuna ganin baza ku iya ba a nemo wata mafitar." Waziri yace, "A'a basai an kai ga haka ba zan san yadda zanyi."
"Better" abinda tace kenan ta yanke wayar.

Hajiya ta kalle shi tace, "da kamar wuya wai gurguwa da auren nesa, tabbas shawarar tayi amma in ka duba ta yaya zamu shigo da Aliyu cikin mu sai kaga gabad'aya maganar bata da ma'ana." Kai yake girgizawa yana nemo mafita a kwakwalwar sa kafin yace, "tunani ya kamata muyi game da lamarin, a ganin ki mu gwada neman Aliyu ko mu bar zancen?."

Hab'a ta rik'e cikin tunani kafin ta kalle shi tace, "a rashin tayi ake barin arwa, haka zakila a yawan tayin ake shan duka. Wanne daga ciki zamu d'auka?."
"Mu taya!" Waziri ya bata amsa yana kallon.
"Allah ya bamu sa'a" ta furta tana kallon sa shima yana kallon ta.

_ya kuke gani anya Aliyu zai karb'i tayin su?. Ina batun Rauda wanne hukunci zai mata?._🤸‍♀️🤸‍♀️🤸‍♀️🤸‍♀️

Continue Reading

You'll Also Like

2.8K 89 36
Labari ne a kan wata mata da kishiyarta ta haukatar da ita da tsohon cikin ta tafi ta haife cikin a halin hauka
23.7K 1.5K 75
Emotional and love story
53.9K 2.9K 12
Labari ne daya kunshi masarautu biyu; Masarautar Katsina, wacce take cikin Nigeria da kuma Masarautar Damagaran, wacce take cikin Kasar Niger. Labari...
1.5M 128K 62
RATHOD In a broken family, every person suffers from his insecurities and guilt. Successful in every field but a big failure when it comes to emotio...