KWANTAN ƁAUNA

Av Nana_haleema

2.3K 136 17

Izza, mulki, k'asaita sun tattara a gare ta ita kad'ai. Y'ar sarki ce, jikar sarki, matar sarki. Bata k'aunar... Mer

001
002
003
004
005
006
007
008
009
010
11
012
013
014
016
017
018
019
020
021
022
023
024
025
Trailer
KWANTAN ƁAUNA Book2

015

57 5 0
Av Nana_haleema

*KWANTAN ƁAUNA*

                ©️ *Nana Haleema.*

*Book 1*
*015*

Fuska a had'e Rauda ta shiga cikin gidan su Khairi na bayan ta tana gurshek'en kuka sai Khalil da yake biye dasu a baya. Ganin su haka ya saka Umma ta kalli Rauda tace, "Tun d'azu Rauda sai yanzu?." Zama Rauda tayi kafin tace, "Sai da naje titi." Umma tace, "Ke kuma Ummin ce ta dake ki kike kuka?."
Khairi tace, "Anty Rauda ce, dan kawai naga wanda ya siya mata fruits a asibiti na yi masa magana shine ta mare ni" ta k'arasa fad'a tana sake fashewa da kuka.

Umma ta kalli Rauda tace, "Akan me zaki mare ta Rauda bayan abin arzuk'i tayi? Ai ba laifi bane da taga wanda yayi mata alkhairi ta nuna ta san shi. Inda arzuk'i kema gaisawa ya kamata kuyi dan taimakon ki yayi." Rauda tace, "Umma bai cancanci a kula shi ba, bai san darajar d'an adam ba kwata-kwata." Da mamaki Umma tace, "Ke ya akayi kika sani?."
"Umma ina wannan d'an sarkin da muka had'u dashi a gidan sarki..? Wanda muka sake had'uwa dashi har Khalil yake cewa yace na shiga mota nak'i...?. dashi muka kuma had'uwa yau, shine fa wanda take cewa ya siyi kayan marmari dan tsabar k'arya."

"Wallahi ba k'arya nake ba shine Umma" Khairi ta fad'a tana kuka. Umma ta kalle ta zatayi magana Rauda tace, "Sai sake marin fuskar ki sannan zakiyi mana shiru naga alama. Bashi da kirki fa ko kad'an Umma yau ma baki ga kalar rashin mutuncin da yayi min ba."

Umma tace, "Kuma dai?." Rauda tace, "Kin san Khairi da shegen surutu ta dinga zuba a gaban sa maganar da ba'a tambaye ta ita take furtawa shiyasa na mare ta, wannan ai ba wanda za'a kula bane ba. Habiba tace min har neman mata yake yi garin haka in yayi mata wani abun fa tunda yasan babu abinda zamu iya?." Umma ta rik'e baki tana nuna Rauda da yatsa tace, "Ina raba ki Rauda da irin wad'annan zantuttukan wallahi, kinga ki kiyayi bakin ki kar ki jawo abinda zaki zo kina dana sani. Ina ruwan ki da sabgar sane wai? Ba abinda ya had'a ku ki dinga k'okarin gefa rayuwar ki a hatsari sabida tsiwa. Kuma kar na k'ara ji kince yana neman mata tunda kedai bai neme ki ba bai kuma nema a gaban idanun ki ba, ki kiyayi tsayuwa gaban Allah."

"Wallahi Allah na tsane shi tsana mai muni Umma, ban tab'a jin tsanar wata halitta a duniya kamar sa ba, bana son ganin koda fuskar sa ce." Umma bata ce komai ba ta wuce tana d'aura alawar magriba dan bata ga amfanin yi mata magana ba.

         Bayan an idar da sallah suna zaune cikin k'aramin hasken fitilar tsakar gidan Baba ya shigo kamar an cillo shi har tuntub'e yake yi, "Ke Rauda maza jeki ga Anas can yana jiran ki." Abincin hannun ta ajjiye dan tasan ko bata ajjiye ba tunda yace ta tashi sai fa ta tashj tana k'okarin mik'ewa cikin fad'a yace, "ki k'arfafa jikin ki malama ki tashi." Babu wanda ya tanka ta tashi ta saka hijjabi ya d'auki kujerar da take zama da kansa yayi gaba tana bin sa baya.

        Sanyin khamshi taji tunda ta shigo soron gidan nasu Baba ya ajjiye mata kujerarya kalli Anas da yake tsaye yace, "Gata ta fito maka da ita da kaina, zauna mana" ya fad'a yana kallon Rauda. Ba musu ta zauna Anas ya duk'a har k'asa yace, "Allah ya saka da alkhairi Baba." Baba ya amsa da amin ya fita.
Zama yayi kan irin tata kujerar yana kallon ta cikin hasken fitilar da aka ajjiye a soron ga hasken wayar sa da ya kunna gana waje wanda yake shigowa, bata d'ago ba shi kuma baiyi magana ba.

        Jin shirun yayi yawa ya saka ta d'ago sai suka had'a ido karon farko tayi murmushi mai kyau tace, "Ina wuni." Jinjina da kujerar Anas yayi ji yayi in bai jingina ba iskar soyayya da take kad'a zata iya d'auke shi ta kai shi wani wajan shiyasa ya nemi mafita tun da wuri. Bai jima sosai ba ya kalle ta yace, "Dan Allah ki sake min murmushi da kika yi yanzu." Bata san lokacin da murmushin ya sub'uce mata ba ya sauke ajiyar zuciya yace, "Na gode my love, Allah ya biya ki da aljanna."

"Baka amsa ba na gaishe ka" ta furta a hankali.
"I'm sorry My love, murmushin da kika yi min a karon farko a rayuwa ta ya saka na manta duk abinda kika ce. Lafiya lau ya jikin ki?."
"Da sauk'i."
"Allah ya k'ara lafiya. Kiyi hak'uri na nemi wayar Baba lokacin da abin ya faru ban same shi ba, ina can hankali na yana kan ki Rauda duk da tarin aiyukan da suka min yawa."

A sanyaye tace, "haka Allah ya k'addara, babu komai a hakan ma na gode sosai, mun ga abubuwan alkhairi Allah ya saka da alkhairi ya biya buk'ata. Umma tace nayi maka godiya sosai." Murmushi yayi yace, "Babu komai Rauda kar ki damu."

Shiru ya sake biyo baya kafin yace, "Munyi magana da Baba akan aikin k'afar ki in sha Allah tafiyar ki zata dawo kamar dah indai ina da rai tunda aikin ba wani mai wahala bane indai aka bar nigeria, cikin satin nan in Allah ya amince za'a yi aikin." D'ago ido tayi suka had'a idanu yayi murmushi sai tace, "Na gode."
"Haba Rauda ni dake babu godiya wallahi, fatana ki amince da soyayya ta ki yadda dani har ta kai mu ga aure."
Murmushi tayi kad'an bata ce komai ba domin ita kam bata d'auka zai sake dawowa inda take ba sabida lalurar da ta same ta.

"Naga kin gaji sosai ga sallah ana yi, zan koma amma in sha Allah gobe zan yiwa Baba bayanin aiki da za'ayi in sha Allah." Kai ta girgiza kafin tace, "Allah ya saka da alkhairi."
"Amin. Amma kin san wacce irin addu'a nake so kiyi min?."
Kai ta girgiza alamun a'a yace, "Ki min addu'a Allah ya mallaka min ke a matsayin matata." Murmushi tayi sai tace, "Ban d'auka zaka yi wannan fatan ba duba da irin iftila'in da ya same ni."  Murmushi yayi yace, "Wai da sai na guje ki kenan?."

Ya sake yin murmushi yace, "Ni Rauda nake so ba abinda yake tare da Rauda ba, zuciyar Rauda nake so ba gangar jikin Rauda ba. Ilimi, halayya, tarbiyya, nutsuwa, iya magana, girmama na gaba, su nake so a tare da Rauda ba k'afar ta ko hannun ta ba. Rauda a yadda nake jin ki a zuciyata ba fata nake ba ko ido da k'afa da hannu kika rasa wallahil azim ni mai iya auren ki ne, soyayyar gaskiya nake miki ba soyayya dan wani abun ba. Ina fatan ki fahimta?."

Murmushi tayi mai d'auke da jin dad'in kalaman sa ko babu komai ta tabbatar da soyayyar ta ta gaskiya ce a zuciyar sa tace, "Na amince da duk abinda ka fad'a, ina kuma alfahari da hakan." shima yayi murmushi yana kallon ta yace, "A karo na farko da nake ganin murmushi a kan fuskar ki har kike min doguwar magana haka lallai addu'ar da nake ba dare ba rana Allah ya karb'a ya kuma fara biya min." Murmushi ta kuma yi ya kalli agogo yace, "Ana ta sallar i'sha zan tafi."
"Ka gaida gida da mutanen gidan."
"Zasu ji in sha Allah. A gaida Umma da kowa da kowa." Ta amsa da to kafin suyi sallama ta koma cikin gida.

       Sallah Umma ta samu tana Khalil ya d'auko mata kujerar ta ta zauna dan ita ba sallar zatayi ba, bayan Umma ta idar da sallah Inna ma na zaune ita da Rahma Umma tace, "Har ya tafi?." Kai ta d'aga alamun eh.
Baba ne ya shigo da sallama suka amsa ya nemi waje ya zauna yana fad'in, "Ke Rauda Anas yace zai biya ko nawa ne ayi miki aikin k'afar ki, zuwa gobe zan nemi likitan da ya amince da aikin sa ayi komai a gama."
Umma ta kalli shi tace, "Amma malam hidimar yaron nan bata yi yawa ba? Ka duna irin abubuwan da aka kawo mana fa yanzu kuma ya kuma biyan kud'in aiki...? Bafa ayi auren nan ba kar a fara zagin mu a gari."
"Bafa rok'on sa mukayi ba shi yayi niya ya bayar."
"Allah ya saka masa da alkhairi ya biya shi" Umma ta fad'a kawai dan babu yadda zatayi.

Baba yace, "Abinda ya kamata kice daman kenan." Yana fad'a ya juya zai fita Inna tace, "motar kwadayi in ka hau zata sauke ka a tashar wulaqanci." Juyowa yayi ya kalle ta yace, "kinga munafurcin ki da bak'in cikin ki shine ya saka ga y'ar ki nan a zaune kusa dake babu wanda yake tayawa, kuma wallahi in baki kiyaye ni ba sai na bayar da ita sadaka a masallaci."

Bata ce komai ba ta mik'e ta shiga d'aki Rahma ma ta bi bayan ta yaja tsaki ya fita. Umma ta kalli Rauda bayan sun bar wajan tace, "Rauda kin masa godiya yadda ya kamata kuwa?."
"Nayi Umma."
"To ya kike jin sa a ranki yanzu? Nidai ina miki sha'awar auren sa badan yana da abin hannu ba sai dan yana son ki, duk da abinda ya faru dake bai guje ki ba sai ma sake bibiyar ki da yake yi wannan alamu ne na masoyin gaskiya."

Shiru Rauda tayi bata ce komai ba Umma tace, "kiyi tunani ki kuma yi addu'a in shine alkhairi Allah ya tabbatar, in ba alkhairi bane Allah ya watsar da maganar ya kawo miki mai alkhairi." Shiru nan ma tayi bata amsa ba ta lumshe idanun ta nan take fuskar Asad ta ziyarci fuskar ta sai ta bud'e idanun ta tana tsaki.
Umma ta kalle ta ganin bata ce komai ya saka ta ja bakin ta itama tayi shiru.

*☆☆☆*

        Asad yana barin wajan a mota gida ya koma dan ya samu kiran mai martaba, yana ajiiye mota b'angaren mahaifin sa ya nufa aka yi masa iso ya shiga ya same shi kad'ai kamar ko da yaushe a zaune a falo. Da sallama ya shiga yayi masa izinin zama ya zauna kafin yace, "Barka da dawowa, da fatan an dawo lafiya." Mai martaba yace, "lafiya lau, ya jikin naka?."
"Na samu lafiya."
"Amma yanayin ka bai gwada hakan ba."
Shiru Asad yayi bai ce komai ba mai martaba yace, "Asad yanayin ciwon da nake ji a jikina kullum sake gaba yake yi, bana son Allah ya d'auki raina ban bada amanar talakawana a hannun nagartaccen mutum ba, dan haka zan dawo da bara bana."

Asad yace, "Amma Takawa....." Mai martaba ya dakatar dashi yace, "Abinda za'ayi kenan Asad, kai kad'ai ne nayi istikhara akan haka yfi sau babu adadi tunda kaga ina ta maimaita maganar ka d'auka kaine alkhairin katagum. Har yanzu kana mafaran da ka fad'a min?."
Asad yace, "Na kwana biyu banyi ba." Kai ya girgiza kafin yace, "ka cigaba da addu'a ka kuma cigaba da kula ba komai zaka yarda dashi ba, mak'iyan ka na kewanye da kai. wanda kake d'auka masoyin kanewani lokacin shine mak'iyin ka, wanda kake d'auka makiyin ka wani lokacin shine masoyin ka."

Asad cikin gamsuwa yace, "in sha Allah za'a kiyaye."
"Mahaifiyar ka ta sanar dani tayi maka mata za'a gaggauta maganar auren ka ana gama shagalin bikin zan sauka daga karaga na baka."  Shi dai Asad bai iya cewa komai ba dan ba wannan ne a zuciyar sa ba, zuciyar sa bugawa take yi da sauri har sautin ta yana ji a kunnen sa.

Mai martaba yace, "zaka iya tafiya."
"Godiya nake, a tashi lafiya" ya fad'a da girmamawa ya fita mai martaba ya bishi da kallon burgewa da kuma sha'awa.
Sai da akayi sallah ya shiga wajan Mama ya samu bata nan ya k'arasa ciki inda Hydar yake yana nan kwance kamar koda yaushe.

         Yana fitowa daga d'akin ya ganta a zaune a kan kujera tana waya yadda take maganar ya tabbatar da k'anwar ta take waya, zama yayi a gefen ta yana sauraron ta kammala wayar. Bata jima sosai tana wayar ba ta yanke ta kalle shi tace, "lafiya na ganka wani iri?"
"An nemi a k'asar Dubai zanyi....." ganin yadda ta d'aure fuska sai ya kasa k'arasa maganar yayi shiru tare da sunkuyar da kansa.

Fuska a d'aure tace"kalle ni." Ba musu ya kalle ta tace, "ko k'asar Dubai zasu d'auka su mallaka maka baza kayi ba Asad, zaman ka a nan shine burina ba barin ka k'asar ba. Akwai abinda ka nema ka rasa ne a nan d'in?." Kai ya girgiza alamun a'a tace, "to kar na sake jin irin wannan maganar a bakin ka, hukunci ne na yanke babu kai babu wani aiki sai na mulkin garin nan."
"Toh. Allah ya wuci zuciyar ki." ya amsa a tak'aice.

"Ya kuka yi da mahaifin ka?."
"Babu komai." Ta d'auke kanta daga kansa kafin tace, "kaji sauk'i, yaushe zaka je wajan Jidda?." Shiru babu amsa hakan ya saka ta kalle shi kamar zaiyi kuka yace, "san da kika ce."
"Gobe."
"Allah ya kaimu" ya furta a sanyaye.

Da hannu tayi masa alamar ya tashi ya bata waje kamar jira yake ya mik'e ya fita. B'angaren su ya tafi ya samu babu koma an k'ara masu tsaron k'ofa harda jami'an tsaro Mama ta ajjiye a wajan ya shiga d'akin sa yana mamaki a ransa yana aiyanawa tsoro bashi zai hana wani abun ya same shi ba, wanka yayi da alwala ya fito yayi sallah ya kwanta. Kasa jin dad'in kwanciyar yayi a kan gadon ya tashi ya jefa pillow a kan tiles ya kwanta yana kallon saman d'akin.

_Sabida Hydar ta zama gurguwa_ zuciyar sa ta cillo masa wannan tunanin ya lumshe idanu a hankali ya bud'e, juyawa yayi ya d'ora kansa a kan hannayen sa yana kallon sama yana tuno yanayin fuskar ta da yadda take masifa akan laifin da ba nasa ba, a bayyane yace, "A ina suke had'uwa da Aliyu? Ya akayi ta san shi?, me ya had'a ta dashi haka?. Ta kira shi mazinaci ya akayi ta sani?."
_ka sani ko itama ya neme ta? Kad'an daga aikin Aliyu zai iya zama dalilin yi masa rashin kunyar kenan._ zuciyar sa ta tambaye shi gaban sa yayi mugun fad'uwa ya mik'e zaune yana girgiza kansa yace, "nooo! In sha Allah hakan bai faru ba."

K'irjin sa yaji yana duka a hankali ya saka hannu ya dafe b'angaren zuciyar sa ya lumshe idanun sa, "What!" Ya furta a bayyane jin abinda yake ji a zuciyar sa da gangar jikin sa mai kama da tsaninin kishi. Tsaki yayi ya koma ya kwanta ya fara k'ok'arin mantawa da tunanin amma ya kasa ko ya ya kulle idon sa sai ta fad'o masa a zuciyar sa, duk yadda yaso kawar da tunanin abin bai yu ba dak'yar bacci ya d'auke shi.

Washe gari.

        Karyawa ake da shayi mai madara har da budori a gidan su Rauda bayan y'an makaranta sun ci nasu kowa ya tafi gidan daga Rauda sai Rahma da iyayen su ana karyawa, Umma ta kalli Rauda da take shan tea a hankali kamar an mata dole tace, "Rauda lafiya dai?."
"Lafiya lau Umma" ta bata amsa tana kallon ta.

"In kin gama ki daure ki lek'a gidan Alhaji Musa ki yiwa matar sa gaisuwa babban yaron ta ya rasu d'azu, har akayi jana'iza kina bacci shiyasa baki sani ba." Rauda ta zaro idanu tace, "Ishaq d'an tane ya rasu Umma?." Ta fad'a tana dafe k'irji.
"Shi fa Rauda. Ki daure in kin gama kije tana son ki matar."
"To Umma in sha Allah, ai ka gaida mai gaishe ka tana sona. Allah ya gafarta masa."
"Amin, maza ki gama kije kafin rana ta bud'e sosai."

        Bata musa ba dan duk jikin ta yayi sanyi dan ta san wanda ya rasu d'in sosai suna gaisawa in sun had'u a gidan su tunda takan je ta gaishe da matar,  mik'ewa tayi ta saka hijjabi mara tsayi sosai ta d'auki abin tafiyar ta ta saka takalmi ta fita daga gidan.

Tafiya take a hankali babu ruwan ta da mutane da suke kallon ta dan in ta biye musu sai ta kifa sabida kallo, kasancewar da y'ar tafiya tsakanin su dan sai ka shiga layikan manyan gidaje zaka je gidan ga kuma yanayin tafiyar ta ya saka ta jima a hanya.
Tana dosar layin taga manyan motoci da runfuna an kafa manya-manyan mutane a zaune ana ta fitowa da abinci kamar ba safiya ba.

        Daga farkon layin babu mutane sai kayi nisa zaka zo wajan mutanen, tsayawa tayi daga baya tana kallon mutanen tace, "Anya zan k'arasa kuwa? Gwara na koma anjima Khairi ta rako ni." Ganin kamar ana kallo ta sai ta b'uya bayan wata farar mota tana cigaba da yanke hukunci a zuciyar ta wata zuciyar tana taje wata tana ta bari sai anjima.

"Gaskiya komawa zanyi bazan iya wuce mazan nan ni kad'ai ba" ta fad'a tana gyara zaman sandinan ta zata bar wajan.
"Takawar ka lafiya d'an sarki jikan sarki, takawar ka lafiya yarima mai jiran gado, taka a sannu sikari bakai farin banza ba, inuwar kowa kake, dawisu sarkin ado, wallahi in kana wajan ba'a kowa sai kai kad'ai, d'aya kake tamkar da dubu." kirarin da ta jiyo kenan daga bayan ta kafin ta farga har an zo inda take duk sai ta rud'e ganin wanda take jin tsoro masu bulalai a hannun su. Tsawa d'aya daga cikin dogaran da suke take masa baya yayi mata yace, "gafara y'ar talakawa!" Ya fad'a da k'arfin gaske.

Duk sai ta kuma gigicewa tama rasa wacce hanya zata bi zuciyar ta na rawa dan bata k'aunar ganin su ko kad'an gashi bata son tsawa.

"Baza ki matsa bane?!" Aka sake fad'a mata kafin ta dawo hankalin ta. Aliyu face d'in ta yake k'arewa kallo ganin yadda ta rud'e ya kuma tabbatar itace fa ba k'arya idanun sa sukayi masa ba. "You!" Ya furta cike da mamaki yana k'are mata kallo tun daga sama har k'asa kafin ya cize bakin sa yana kallon motar sa wacce yafi so duk duniya tana jikin ta a tsaye har da dafawa.

      Sai a sannan ta dawo nutsuwar ta ta danne tsoron da take ciki tayi niyar barin wajan yace, "ke mahaukaciyar banza, ki kiyayi idanu na su sake tozali da k'aramar mummnar fuskar ki. Duk sanda na sake tozali da bak'ar fuskar ki wallahi sai na canja miki kamannin" ya fad'a a kausasahe yana nuna ta da yatsa.
A fusace ta juyo ta zuba masa banzar harara tace, "indai har ni mahaukaciya ce tabbas kai kakana ne a hauka domin a wajan ka na gani na koya, kaine mahaukaci bani ba a zahirance ana ganin yanayin ka an san na mahaukata ne. Baka isa kayi min komai ba kuma wallahi nafi k'arfi wanda ya fika ma balle kai iskar titi" ta fad'a cikin salon rashin kunya tana hararar sa cikin tsana da b'acin rai.

       Kafin kace kwabo dogarin bayan ta ya zuba mata bulala a baya ta runtse idanu domin bulalar ta shige ta sosai ta hana idanun ta kuka amma tana jin zugin ta a gadon bayan ta, kallon ta kawai yake da mamaki ya rasa abinda zai mata ya wuce daga b'acin ran da ta jefa zuciyar sa a ciki hakan ya saka shi yin cak yana kallon ta. D'aga hannu yayi zai d'auke ta da mari ganin hakan ya saka ta runtse idanu yaji an rik'e hannun nasa daga baya bayyanar wanda ya rik'e hannun nasa ya sake b'ata masa rai yana kallon sa yace, "Aliyu why?."

         Jin shiru ba'a mare ta ba ya saka ta bud'e idanu tana kallon su, gaban ta yayi mummnar fad'uwa ganin sun zamar mata guda biyu hatta kayan jikin su iri d'aya komai nasu sak kwabo da kwabo baka banbance su. Murza idanun ta tayi ta sake kallon su a lokacin da Aliyu ya fizge hannun sa yana fad'in, "look Asad babu abinda ya shafe ka babu wanda ya isa ya hanani ganin waye uban yarinyar nan a kaf duniyar nan, babu wanda ya isa ya hana ni sakawa a sake b'alla mata k'afa."

Asad ya kalle ta itama shi take kallo idanun ta a bud'e yace, "Jeki." Kasa motsawa tayi jin sanyin muryar sa har cikin kwanyar ta ta kasa koda motsi sai kifta idanu da take yi. "Kee y'ar talakawa baki ji abinda yarima yace ba ne!" Aka sake mata tsawar da ta firgita ta har sandar ta guda d'aya ta fad'i.

"Kar ka sake!" Ya fad'a yana d'agawa wanda yayi tsawar tsayan sa tare da had'e fuskar sa. "Tuba nake ranka ya dad'e, Allah ya wuci zuciyar ka" ya fad'a yana zubewa a k'asa dan bai tab'a jin Asad yayi tsawa haka ba tunda suke. Asad ya sake kallon ta baice komai na kamar ta san me yake nufi ta duk'a zata d'auki sandar ta ya kalli dogarin sai ya zabura ya d'auka mik'a mata yana fad'in, "Wuce ki tafi baiwar Allah, Allah ya baki lafiya" ya fad'a a sanyaye yana bata hanya. Da yake babu mutane a wajan da suke masu zaman makokin suna can nesa ba hango su ake ba hakan ya saka babu wanda ya lura da abinda yake faruwa a wajan.

        A sanyaye take takawa jikin ta kamar an mata dukan tsiya tana tafiya tana waiwayon su taga d'aya daga cikin su yana ta masifa d'ayan kuma yama bar wajan da alama wanda yake k'okarin dukan nata ne yake fad'a, kallon gaban ta tayi ta cigaba da tafiya gaban ta na fad'uwa matuk'a zata iya rantsewa da Allah bata tab'a ganin y'an biyu masu kama da juna kamar su ba.

K'arar mota taji a baya ta Aliyu ne ya wuce a guje ta sauke numfashi tana bin motar da kallo gaban ta na cigaba da fad'uwa tsoro duk ya mamaye mata zuciya. Tunani take son yi amma ta fi to ta samu waje tukunna ta zauna sai tafi yin tunanin dakyau.
Tafiya take a kan hanyar babu kowa kamar yadda ta biyo tana tafe a hankali tana tunani, zafi bayan ta yake yi mata inda suka dake ta da bulala ta runtse idanun ta sosai har lokacin tana ji zafi sosai.

Asad yana hangon ta yana tawowa a bayan ta a mota a hankali ya rasa me yake d'aukar sa akan yarinyar ya san tabbas tana bashi tausayi amma bayan tausayi yana jin wani abu amma ya kasa fassara meye. Yana ganin ta kamar yarinyar cikin mafarkin sa abinda ya saka bai tabbatar ba sabida har lokacin fuskar ta gabad'aya bata tab'a bayyanar masa a mafarkin nasa ba.
Yana so ya k'arasa ya taimake ta ya kai ta gida amma kuma yana jin zai iya hakan gwara kawai ya k'yale ta.

Waje yaga ta samu ta zauna a kan wani dutse dake kan hanyar tana sauke numfashi alamun ta gaji, tsayawa yayi a motar yana kallon ta zuciyar sa na angiza shi akan yaje ya taimaka mata abar a taimakawa ce. Taka motar yayi yazo kusa da ita ya sauke glass ya kalle ta itama ta kalle shi suka had'a idanu duk sai ta dabarbarce kamar mara gaskiya ta fara kallon gefen ta kamar wacce take neman wani abun da ta ajjiye a wajan.  Wani abu take ji mai sanyi yana shiga duk ilahirin jikinta wanda ya kasance bak'o a gare ta shiyasa duk ta dabarbarce jin bak'on yanayi a tare da ita har tana sauke ajiyar zuciya ga bugun da k'irjin ta yake yi.

*Akwai k'ura fan's.*⛹‍♀️⛹‍♀️🤸‍♀️🤣

Fortsätt läs

Du kommer också att gilla

KASHI Av stuckinatale

Allmän skönlitteratur

398K 19.9K 42
"So, Mrs. Kashi Abhay Pratap Singh..chalte hai. Goodbye..". Saying this, he left her broken in this world of betrayal. ~~~~~~~~~~ Kashi, a simple gir...
16.9K 882 32
DR UMAIMAH USMAN BULAMA,Mace yar kimanin shekara ishirin da tara , Babbar surgeon A asibitin CITY TEACHING HOSPITAL , Aure Uku, ƴaƴanta uku . Mace m...
52.8K 2.1K 18
"I promise you Mami, zan nemo miki ƴar'uwarki a duk inda take a faɗin ƙasar nan. SULTAN promises you that." Sultan ya shiga ya fita, har ya aikata...
126K 7.2K 45
Complicated🤐🤐🤐 Find out👇👇👇