KWANTAN ƁAUNA

Da Nana_haleema

2.2K 112 17

Izza, mulki, k'asaita sun tattara a gare ta ita kad'ai. Y'ar sarki ce, jikar sarki, matar sarki. Bata k'aunar... Altro

001
002
003
004
005
006
007
008
009
010
11
012
013
015
016
017
018
019
020
021
022
023
024
025
Trailer
KWANTAN ƁAUNA Book2

014

62 1 0
Da Nana_haleema

*KWANTAN ƁAUNA*
       FitattuBiyar 2023

             ©️ *Nana Haleema.*

*Book 1
*014.*

      A sanyaye ta shiga gida hannun ta rik'e da leda ta zauna a inda ta saba zama Umma ta kalle ta tace, "Lafiya yake neman ki?." Ledar hannun ta ta nuna mata kana tace, "Wai cewa yayi nayi hak'uri da abinda ya faru jiya ga maganin wani ya siya min kuma ya biya bashin baya ya kuma bada kud'in wanda zan karb'a nan gaba."  Da mamaki Umma ta rik'e baki tace, "ikon Allah! Waye kuma ya biya?."

"Ban sani ba Umma, na tambaye shi yace shima turo wani aka yi amma wanda ya siya d'in bai zo da kansa ba."
"Wanne d'an albarkan ne da wannan aikin?."
"Nima kaina ya kulle Umma."
Umma ta nisa kafin tace, "to wama zai miki haka in ba Anas ba? Shi kad'ai ne saurayin da yake zuwa wajan ki yanzu shine zai shiga lamarin ki, Jikina yana bani shine ya siya miki."

Rauda tace, "Amma kuma Umma Anas baya garin nan tun ranar da muka had'u had'uwar k'arshe ya cewa Baba zaiyi tafiya ban kuma ganin sa ba,  bai ma san halin da nake ciki ba a yanzu." Umma tace, "Ke kamar ba y'ar zamani ba Rauda? Kin manta yanzu waya tana isar da ko wanne irin sak'o a kuma duk inda kake a duniya?."
"Haka ne Umma, amma ina tantama gaskiya."
"To in ba shi ba waye Rauda?."
"Babu kowa" ta fad'a a sanyaye Umma tace, "to kin gani, amma Allah ya yi masa albarka ya raba shi da iyayen sa lafiya."

Rauda ta murmusa har cikin zuciyar ta take jin farin ciki tace, "Amin Umma Karon farko kenan a rayuwar ta da naji ya burge ni" ta fad'a farin ciki na shiga zuciyar ta sosai. Umma tace, "kin ga bara na kawo miki ruwa ki sha maganin nan jiya kin sha wahala" ta fad'a tana mik'ewa ta kawo mata ruwa a kofi ta sha maganin ta shafa na shafawa ta ajjiye ragowar.

        Inna da take d'aki taji komai ta fito fuskar ba yabo babu fallasa ta wuce su bata ce komai ba daman Umma tasan baza ta ce ba dan idan magana ce akan Anas k'arara zata nuna miki tana bak'in ciki da ba Rahma yake so ba. Baba ne ya shigo a gigice fuskar sa taf fara'ar da basu tab'a ganin irin ta ba yana fad'in, "mutanen gidan nan kuna ina! Kuzo kuji abin arzuk'i da farin ciki" ya fad'a yana shigowa yana kallon su. Umma tace, "Malam lafiya?."
"Bari kedai, ai babar ki ta iya haihuwa da ta haifo ki na aura kika haifo min Rauda. Bawan Allah shigo mana" ya fad'a yana kallon k'ofa.

Mutumin ya shigo sanye da k'ananu kaya hannun sa rik'e da leda ya durk'usa har k'asa ya gaishe su kafin yace, "An turo ni akan na kawowa Baba keke napep guda biyu, sannan ance na bawa mahaifiyar Rauda wannan kud'in" ya fad'a yana d'auko kud'in daga leda.  Da hanzari Baba ya kaiwa kud'in cafka mutumin ya hana shi ya kalle shi yace, "Ita aka ce na bawa Baba." 

Yak'e Baba yayi yace, "Daman zan mik'a mata ne ai."
Mutumin ya k'arasa wajan Umma  ya ajjiye kud'in a gaban ta yace, "sannan yace a gaida wacce bata da lafiya shima baya jin dad'i ne da ya zarar ya samu lafiya zai baro inda yake yazo in sha Allah. Gashi yace a bata" ya fad'a yana sake d'auko kud'i a rufe a takarda ya sake ajjiyewa Umma.

"Sannan akwai kayan abinci da yace a tawo dasu gasu can za'a shigo dasu yanzu." Umma da ta saki baki tana kallon mutumin tace, "bawan Allah waye ya turo ka da wad'an nan abubuwan haka?."
Kafin yayi magana Baba yace, "Anas mana, da shi mukayi maganar zai siya min abin hawan da zan dinga samun kud'i dashi, gashi kuma ya cika alqawari." Umma ta jinjina kai tana kallon mutumin tace, "Amma hidimar tayi yawa bai kamata mu karb'i abin hannun sa ba tunda babu wata magana mai k'arfi tsakanin sa da Rauda, gaskiya a mayar masa."

Baba yace, "ai na riga na ba shi auren ta, ko bana raye shine mijin Rauda tun ba yau ba na mallaka masa ita" ya fad'a hakora a bud'e dan kar ma a mayar da kud'in. Mutumin ya murmusa ya mik'e tsaye yace, "Za'a shigo da kayan yanzu" ya fad'a yana fita jim kad'an aka fara shigo da kayan abinci babu abinda babu harda yankakkun kaji da d'anyen nama. Bayan an gama shigowa da su yace, "To Baba zan wuce ni." Umma tace, "Bawan Allah da gaske Anas d'in ne ya turo ka?." Zaiyi magana Baba yace, "Kina da matsala Binta, in ba shi ba waye zai aiko mana da wannan abin arzuk'in? Shine an fad'a miki sai faman maimaita magana d'aya kike yi."

Umma tayi Jimm sai tace, "mun gode bawan Allah kayi magana godiya dan Allah. bamu da bakin gode masa sai dai muce Allah ya biya masa dukkan buk'atun sa na alkhairi."
Ya amsa da amin Umma tace, "Tsaya bawan Allah a baka tukwici." Yayi dariya yace, "Haba hajiya ki bar shi na gode sosai. Sannan Baba yace a fad'a maka dan Allah kar kace zaka ja keken da kanka ka bayar a dinga yi maka ana kawo maka kud'i har gida."

Baba yace, "In sha Allah hakan ce zata kasance, Allah ya biya buk'atar duniya da lahira."
"Amin ya Allah. sai an jiman ku" ya fad'a yana fita Baba yabi bayan sa.

Rauda dai ta kasa cewa komai bakin ta a bud'e tana kallon abincin da kuma kud'in dake kusa da Umma zuciyar ta na mugun bugawa da sauri-sauri bakin ta ya mutu murus ta rasa wacce irin kalma zata furta. Umma ta kalle ta tace, "Rauda baki ce komai ba bayan duk abinda ya faru ta silar ki ne." Kamar kuma an mata allura a lokacin ta sauke ajiyar zuciya tace, "Umma na kasa magana ne gabad'aya ban san me zance ba."
"Haka zaki ce kuwa Rauda domin duk abinda aka bamu ta dalilin kine."
Kafin tayi magana Baba ya shigo fuska washe yana kallon kayan abincin yana fad'in, "yau ko fita kasuwar ma bazan ba a dafa mana kajin nan muci mu karya k'asusuwa."

Umma ta kalle shi bata ce komai ba ya kalli Rauda yace, "Allah ya yi miki albarka Rauda, ke farar haihuwa ce wallahi ko cikin y'ay'ana ke ta daban ce." Inna da take tsaye tace, "Su kuma bak'ak'en haihuwar sai a zubar dasu ace ba'a so" tana fad'a ta shiga d'aki ya bita da kallo baice komai ba ya cigaba da santin kayan abinci.

Umma tayi dariya tana girgiza kai jin yau Rauda ake cewa ko a cikin y'ay'an sa ita ta dabance, ita yake yiwa wannan fara'ar har yana ce mata farar haihuwa. "Allah yayi mana arzuk'i" Umma ta furta a bayyane tana sauke numfashi.

Umma ya kalla yace, "Nawa ne kud'in da aka baki?." Yana fad'ar hakan ta d'auke takardun kud'in da nata dana Rauda ta rik'e bata ce komai ba ganin hakan ya saka yace, "Ga b'arawo zan sace miki kud'i shine kika d'auke ko?." Ita dai bata furta ba ya girgiza kai.

Ranar Umma ke da girki abinda baya faruwa a gidan ranar shine ya faru, lafiyayar shinkafa da miyar kaji aka yi a gidan kowa y'an makaranta suka dawo cikin ikon Allah akayi bak'i a yayyen su mata duk suka zo aka ci aka sha kowa da farin ciki a zuciyar sa ana ta santin auren Anas da Rauda. Rauda sai taji alfahari a zuciyar ta ganin ana ta santin abinda ta dalilin ta ya samu lokaci d'aya taji Anas yana samu kyakykyawan gurbi a zuciyar ta.

*☆☆*

       A jingine yake da fuskar gado idanun sa a lumshe kana kallon yanayin sa kasan bashi da cikakkiyar lafiya haka zalika baya jin k'wari a jikin sa dan fuskar sa da yanayin sa ya gwada hakan. kamar wanda aka yiwa magana ya bud'e idanun sa yana kallon d'akin kafin ya sauke numfashi ya kalli k'ofar da za'a shigo d'aki jin motsi.
Mama ya gani ta shigo ya tashi zaune sosai yana kallon ta ta k'araso da sauri ta zauna kusa dashi ta tab'a fatar kansa tana kallon sa tace, "Asad ya jikin? Tun d'azu nake zuwa kana bacci."

"Naji sauk'i, Barka da safiya."
"Ka tabbata lafiya lau ka ke?" Ta furta ba tare da ta amsa gaisuwar ba. "Naji sauk'i" ya sake fad'a yana kallon ta. Fuskar sa ta rik'e tana kallon sa tace, "ka rame Asad yanayin fuskar ka ya nuna min akwai abinda yake damun ka bayan ciwon da kake fama dashi, meye?."
"Mama kwana biyu ta daina zuwar min cikin mafarkina, ina so na ganta ban san inda take ba, ina kewar ta sosai" ya furta yana kulle idanun sa yana nuni da tsantsar abinda yake zuciyar sa kenan.

Da mamaki mai had'e da fad'uwar gaba Mama tace,  "Wacece take zuwa mafarkin ka har kake so ka ganta?." Bud'e ido yayi yaga ta kafe shi da idanuwa sai kuma ya dawo hankalin sa tunawa da wacece a zaune kusa dashi ya sauke kai k'asa baice komai ba.

"Magana nake maka wacece?."
"Margayiya Hajiya mai babban d'aki" ya furta a hankali ba tare da ya kalle ta ba. Nannauyar ajiyar zuciya tayi jin abinda yace sai ta murmusa tace, "Ka dinga mata addu'a itace zata amfane ta a yanzu. Ni har ka bani tsoro na d'auka wata ce take kutse cikin mafarkin ka." Shiru yayi bai amsa ba gaban sa mugun fad'uwa haka kawai ba tare da ya san dalilin hakan ba.

Tashi tayi ta fita jim kad'an ta dawo da abincin sa da kanta ta zauna kusa dashi ta had'a masa duk abinda zai buk'ata ta bashi tace, "maza ka cinye akwai maganin da Abie ya aiko dashi zaka sha." Bai ki ba ya ci abincin daidai yadda zai iya ya bar sauran ya sha maganin da ta cika masa a k'aramin kofi.

Kallon sa tayi bayan ya shanye maganin tace, "mahaifin ka ya dawo d'azu in ka samu lafiya sai kaje ku gaisa. Sannan na hana kowa shigowa apartment d'in nan koda Hafiz ne ko Suhail ban lamunci su zo nan ba, in suna son had'uwa da kai suje wani wajan amma banda gidan nan na lura masu son ganin bayan ka suna da yawa." Kai kawai ya girgiza dan bazai kuma iya cewa komai ba.

Fita tayi daga d'akin ya sauke ajiyar zuciya ya d'auki ruwa ya sha, "Rauda!." Ya ji bakin sa ya furta ba tare da ya shirya hakan ba ya runtse idanun sa yana hango idanun ta da goshin ta ya bud'e yana cize bakin sa ji yake kamar ya tsinke kansa da mari. Yadda yake jin begun zuciya da fad'uwar gaba abin har tsoro yake bashi ya kalli gefen k'irjin sa yaga yana d'agawa a hankali.

Tashi tsaye yayi yana dafe da kansa sa ya kalli agogo inda ya nuna masa k'arfe hud'u na yamma ya sauke numfashi a karo na babu adadi ya shiga band'aki, bai jima sosai ba ya fito ya shirya cikin manyan kaya kamar koda yaushe yayi kyau sosai duk da ya rame amma kyawun sa bai b'uya ba.

       K'ofa aka bud'e aka shigo bai kalli wanda ya shigo ba dan yasan bazai wuce jinin sa Aliyu ba shi kad'ai ne zai shigo babu izinin sa, "ya jikin ma?" Aliyu ya tambaya yana kallon sa. Juyowa yayi ya kalle shi da niyar bashi amsa sai maganar ta tsaya ganin abinda bai tab'a gani ba tun bayan girman su shi ya gani a tare dashi. kayan da yake jikin Asad irin sa Aliyu ya saka hatta hular kan su iri d'aya ce kamar su ta fito sak babu wanda zai banbance Aliyu babu wanda zai banbance Asad.

"I'm fine, thanks you" ya furta a tak'aice bai kuma kallon sa ba. Aliyu bai damu ba bai kuma kallon sa ba shima ya fita daga d'akin. Sosai Asad yake cikin mamakin canjawar da Aliyu yayi ya koma sak irin sa, hatta yadda yake magana shima ya mayar da tasa hakan babu ta yadda zaka ce ba shi bane in kaga Aliyu a canjin da ya samu abin yana d'aure masa kai. Waya da key na mota ya d'auko duk da baya jin k'arfi a jikin sa ga jiri da yake ji amma baya son zaman gidan ya fito falo. Babu kowa a falon ya wuce ya fita zuwa harabar apartment d'in nasu.

A sannu yake takawa sabida yadda kan yake masa ciwo cikin nutsuwa yake giftawa khamshi yana tashi. ganin yadda ake gaishe shi jiki yana rawa ya fahimci d'auka suke Aliyu ne dan shi ya fara fitowa sun gane kayan jikin sa hakan ya saka shi fita daga gidan da sassarfa.

*☆☆☆.*

        "Khalil! Khalil!!, baka ji ina yi maka magana ne?" Umma ta fad'a daga d'aki tana fitowa amma babu Khalil babu dalilin sa. "Lallai ma yaron nan nace ya jira ni zan aike sa sai ya fice?." Rauda da take zaune tace, "yammar tayi ai ya tafi ball balle yau da garin yake a rufe ba rana" ta fad'a tana cigaba da karanta azkar.
"Ina Khairi?."
"Ta tafi kara Yaya Ummi bakin titi."
"Rahma kuma basa nan?."
"Duka sun fita" Rauda ta sake bata amsa tana kallon ta.

Umma tayi k'wafa tana girgiza kai Rauda tace, "A kira miki shi ne?." Umma tace, "k'yale ni bara na fita da kaina na kira shi."
Da sauri ta ajjiye littafin hannun ta ta mik'e tace, "Haba Umma bana so kina fita irin haka wallahi, bara na kira miki shi da kaina." Umma tace, "in yayi nisa ki k'yale shi kar ki yi nisa kema." Da to ta amsa ta saka hijjabi ta fita tana dora sandinan ta.

       Batayi nisa ba ta hango yara ana ta ball ta kalle su tace, "Ina Khalil?." D'aya daga cikin yaran yace, "Yanzun nan yayi titi." Rauda ta girgiza kai ta bi hanyar titin dan ta kira shi kar ayi magariba yana ball. Titi ta fito amma dai bata ganshi ba, ta dinga kallon titin amma baya nan taja tsaki ta juya da niyar komawa taji kamar tayi karo da mutum.

Gaban ta yayi muguwar fad'uwa shakar khamshin turaren da bazata manta dashi ba tayi saurin d'agowa ta kalle wanda ta buge. dogon tsaki Aliyu ya ja ya saka hannu biyu ya bangaje ta ta fad'i k'asa ya cize bakin sa cikin takaici da tunanin irin hukuncin da ya kamata yayi mata. kallon ta ya kuma yi itama shi take kallo haushi da tsanar sa take ji a zuciyar ta yace, "Mahaukaciya!" Abinda ya furta kenan ya wuce ya bar wajan zuciyar sa cike da jin haushin zuwan sa ma wajan, in badan mai martaba ba mai zai kawo shi unguwar talakawa kamar wannan, badan mutane da suke kai kawo ba babu abinda zai hana bai sake b'alla mata k'afa ba.

Kafin Rauda ta farga bata kuma ganin sa ba sai k'urar motar sa ta gani ta kyad'a kai tana jin zafi a hannun ta ta furta, "kaine dai mahaukaci bani ba, wanda bai san darajar na gaba dashi ba. Na tsane ka wallahi naso kuma ka tsyaa dana tabbatar maka da kaine mahaukaci bani ba."  ta fad'a tana k'okarin Mik'ewa.

       A hankalin motar Asad kirar range rover ash colour take yin slow daga gefen ta, wajan yake kalla yaga tabbas a nan suka had'u ya sake kallon gefe yaga kamar itace take so ta tashi kamar kuma ba itace ba, zuba mata ido yayi ta jikin glass d'in motar ganin fa da gaske ta kasa tashi ga kuma babu yawan mutane a wajan sai ya b'alle murfin motar ya fito duk da zuciyar sa na hana shi hakan amma gangar jikin sa tak'i karb'ar umarnin zuciyar tasa ya tsallako. Khamshin da taji a kanta ya saka ta d'ago kai ta kalle shi mamaki ya hana ta magana har ya kama kafad'ar ta kamar jiya ya tasar da ita tsaye bata san anyi ba.

Lallai ma wannan mutumin yana raina mata hankali, shi kuwa fuskar ta yake kallo da babu niqab ko face mask zahirin tace a bayyane. d'auke idanu tayi dan yana yi mata kwarjini jin baice komai ba ya saka tace, "wai fuska biyu ce da kai wani lokacin kamar mutumin kirki wani lokacin mutumin banza ne kai, in zaka yiwa mutane fuska biyu banda ni domin na riga na gama gano kai d'in ba komai bane face mahaukaci wanda bai san darajar d'an adam ba. ban tab'a jin tsanar halitta kamar yadda nake jin tsanar ka ba. Na fad'i duk abinda yake bakina in ka dama ka saka a kashe ni a nan shine zaka nuna min lallai kana da k'arfin ikon mulki da sarauta. Ni kuma zan nuna maka k'arfin sarautar Allah domin ahi kad'ai nake jin tsoro a duniyar nan" ta fad'a tana d'ago ido ta zuba masa banzar harara mai d'auke da zallar tsana da k'yama.

       Baice komai ba daman bazai ce ba dan ya gama fahimtar duk abinda take fad'a ba dashi take ba babban abinda yake d'aure masa kai a ina suke had'uwa da Aliyu?, "Lahh Yaya Aliyu!" Aka fad'a daga bayan sa cikin mamaki. Bai juya ba hakan ya saka Khairi k'arasowa da sauri ta tsaya kusa dashi tana dariya tace, "Ashe dai zan gane ka, ina wuni Yaya Aliyu?."
Kallon ta yake yana so ya tuna inda ya santa ganin hakan ya saka Khairi tace, "Wacce ka siyawa Yayar ta kayan fruits a k'ofar asibitiiiiii....?" Ta fad'a tana jan kalmar asibitin lallai sai ya gano.

Murmushi yayi kad'an alamun ya tuna ganin hakan ya saka tace, "Kaga yayar tawa nan ita ka siyawa. Anty Rauda ina lokacin da kina asibiti Baba ya bada d'ari biyu na siyo miki lemo a wajeeee.. Har Umma ta dinga min fad'aaaaaa? To kin ga wanda ya siya miki yace na kawo." Juyo da kallon ta tayi ga Asad tace, "Yaya Aliyu kaga Antyna ta koma mai yawo da sanda ko? Wanda ya buge ta ya daina zuwa inda take ance kuma sai an mata aiki zata warke mu kuma bamu da kud'in biyan kud'in, shikenan Antyna ta zama gurguwa" ta fad'a kamar zatayi kuka.

Takaici, bak'in ciki, b'acin rai suka tararwa Rauda lokaci d'aya bata san sanda ta tsinke Khairi da mari ba ta jawo ta kusa da ita ciki fad'a sosai ta zare mata idanu tace, "in baki min shiru ba sai na fasa miki baki, banza wacce bata iya shiru a rayuwar ta. Wa kika tab'a gani yana kula wanda basu san darajar mutane ba irin wand'an nan? Wa kike ganin yana kula masu shaye-shaye da neman mata eyeee?."

Khairi da take hawaye tace, "Wallahi yana da kirki Anty." Bai ji mai tace mata a gaba ba tafiya suke yi shi kuma ya juya zuwa cikin motar sa, duk da kalamai ta fad'a masu muni amma sam baiji komai a ransa ba dan maganar ta ta tabbatar masa da Aliyu yake bada shi ba.

     A kan sitiyarin motar ya saukar da kansa yana furzar da iska a hankali yana jan numfashi yana saukewa, kallon inda suke yayi yana hango su da alama fad'a take yiwa Khairi dan yaga tana magana a fusace, duk taku d'aya da take yi tana nisa dashi ji yake kamar ana d'igo masa kewa wacce bai san dalilin ta ba a zuciyar sa tana yin gaba yana sake jin kewar na k'aruwa har ya daina hango su.

_Ya akayi ta san Aliyu?, a ina suke had'uwa haka?. Da gaske silar Hydar ta zama gurgurwa?._ tambayoyin da yake yiwa kansa a zuciyar sa kenan amma babu mai bashi amsa sai ita d'in. Sake kallon layin nasu yayi ya sauke numfashi sunan Rauda na yi masa amsa kuwa a cikin kunnuwan sa. "Inda Aliyu ta fad'awa hakan da me zai faru?" Ya furta a bayyane har lokacin yana kallon inda suka bi dan yasan tabbas sai dai wata ba ita ba, babu abinda zai saka Aliyu bai mata mummunan hukunci ba.

Yarinyar cikin mafarkin sa yake tuno fuskar ta idanun ta da goshin ta yake ganowa kamar ko yaushe, bud'e ido yayi ya tuno lokacin da Rauda ta bud'e idanun ta tana yiwa Khairi fad'a gabad'aya yanayin ta ya koma irin na yarinyar mafarkin sa. "Itace ko A'a" Ya tambaya yana dafe kansa da duka hannayen sa guda biyu jin bak'on  abu wanda bai tab'a jin irin sa ba yana cigaba zuciyar sa da ko ina na jikin sa.

Continua a leggere

Ti piacerà anche

2.3K 99 16
wannan sanyin illa zaiyi miki acancikin ki, ai ita mace da ɗumi aka santa, ai ballagaza ita ke illata ƙanta da ƙanta sai sanyi ya kamaki kizo kisani...
7.2K 254 12
_Duniya makaranta a lokacin da wasu suke shiganta a lokacin ne wasu ke barinta,wasu na zuwa Duniya wasu kuma na barin Duniya, Rayuwa kamar shafin lit...
16.6K 881 32
DR UMAIMAH USMAN BULAMA,Mace yar kimanin shekara ishirin da tara , Babbar surgeon A asibitin CITY TEACHING HOSPITAL , Aure Uku, ƴaƴanta uku . Mace m...
1.4M 128K 62
RATHOD In a broken family, every person suffers from his insecurities and guilt. Successful in every field but a big failure when it comes to emotio...