KWANTAN ƁAUNA

By Nana_haleema

2.3K 136 17

Izza, mulki, k'asaita sun tattara a gare ta ita kad'ai. Y'ar sarki ce, jikar sarki, matar sarki. Bata k'aunar... More

001
002
003
004
005
006
007
008
009
010
11
012
014
015
016
017
018
019
020
021
022
023
024
025
Trailer
KWANTAN ƁAUNA Book2

013

60 4 0
By Nana_haleema

*KWANTAN ƁAUNA*
      FitattuBiyar 2023

             ©️ *Nana Haleema.*

*Book 1*
*013.*

Rai a b'ace Rauda ta shiga gida Khalil ya taimaka mata ta ajjiye sandar hannun ta ta zauna a kan farar kujerar da take tsakar gida shi kuma ya zauna a k'asa. Yanayin ta Umma ta kalla tasan an tab'o ta kuma tasan bazai wuce akan maganin ba hakan ya saka tace, "ko baki ce ba nasan ya hana ki maganin ne shiyasa kike kunbura fuska, sai kiyi hak'uri." Rauda tace, "daga neman taimako Umma sai ya zage ni? Har yana cewa da yasan halin Baba tun farko bazai bada bashi ba."

Umma ta murmusa tace, "ban ga laifin sa ba Rauda; yanzu kafin wannan kud'ad'e masu tarin yawa su fito daga hannun baban ki a shekara goma a fama. Yayi k'ok'ari fa da ya baki ma dan ba kowa ne zai bada magani mai tsada kamar naki ba, Allah yasa baki masa rashin kunya ba dan ya taimaka miki." Shiru tayi bata amsa ba Baba da yaji komai ya shigo yana fad'in,

        "In ma tayi masa rashin kunyar ita ta jiyo ai ita k'afar zata damu da ciwo sabida rashin magani bani ba." Shiru sukayi dukkan su kafin Khalil yace, "Umma wani kyakykyawa kamar balarabe ya kusa kad'e Anty yanzu har sai da ta fad'i k'asa." Umma tace, "Kuma dai?."
"Amma ai bata ji ciwo ba ai. Umma ta yi masa rashin kunya yace muzo ya kawo mu gida tak'i kuma baki ga motar ba babba" ya fad'a yana fad'ad'a hannayen sa alamun girma.

     Baba da yake alwala a durk'ushe furzar da ruwan bakin sa yace, "A koda yaushe ke ai bak'in halin ki yake ja miki alkhairi yake tsallake ki ya koma kan wanin ki. inda kin shiga motar da bai siya miki maganin ba." Umma tace, "Rauda akan me zaki masa rashin kunya? Meyasa ke baka jin kunyar yiwa babba rashin kunya ne?." Rauda tace, "Umma nifa ba rashin kunya nayi masa ba na fad'a masa abinda yake raina ne. shine wanda nace miki ya mare ni lokacin da na raka su Habiba gidan sarki shine na amayar masa da abinda yake zuciya ta a lokacin ban samu dama ba ina jin tsoron doki ya hana ni mayar masa."

Umma ta wara idanu tace, "D'an sarkin Katagum guda masu ji da kud'i da mulki kika yiwa rashin kunya Rauda?, Yaron da an masa shaida bashi da kirki ina ke ina shi?, in ya saka aka yi miki wani abun fa?." Rauda ta turo baki gaba tace, "To Umma dan yana d'an sarki sai yayi min abinda yaga dama na k'yale shi? Bafa haifata yayi ba da zai fad'a min magana na tsaya ina kallon sa, wallahi saina rama dan mutum ne shi nima mutum ce."

         "Sannu y'ar gidan dangote, nace sannu y'ar gidan shugaban masu kud'in duniya. Wato in ana neman talaka mai fad'in rai wanda aka fad'a a hadisi aka same ki Rauda an shafa Fatiha. Tunda bake ban tab'a ganin yarinya mai karanbani da nuna isa kamar y'ar wani ko y'ar wata sai ke da kanki yake rawa. D'an sarki guda kika yiwa rashin kunya, bakya jin tsoron wani abun ya same ki ke ga fitsararriya mai ji da fitsara. Har yace miki kizo ki shiga mota ya kawo ki kika ki sabida girman kai yayi miki yawa. To Allah ya isa abinda yayi niyar baki in ya kawo ki kika yi mana bak'in ciki da yau nasan kaji zamu ci mu kwanta, sakamakon rashin kunya duk abinda ya saka aka yi miki ke kika ja kar sunan Adamu ya fito a gaban sunan ki" Baba ya fad'a yana buge rigar sa ya fita.

      Umma ta girgiza kai tace, "Wai Allah ya isa, Malam har ya saka a ran sa ma za'a bashi wani abun bama illar shiga motar tasa yake hangowa ba kawai a bashi kud'i koma me yayi miki in kin shiga motar ke kika jiyo. Kai Allah ya kyauta" Umma ta fad'a tana murmushin takaici kafin ta kalli Rauda tace, "Kinga Rauda na raba ki da y'ay'an masu kud'in nan babu ruwan ki dasu in ba so kike ki jawo mana matsala muna zaune lafiya ba. Ina ke ina yi masa rashin kunya? In yaso a batar dake yana da damar yin hakan babu wanda yasan shine yayi, ki dawo hankalin ki dan Allah bana son wannan fitsarar taki." Rauda bata ce komai ba tayi shiru k'afar ta na ciwo rashin shan maganin da batayi ba.

*☆☆☆*

         Tun a mota yake tunani har ya isa guest house d'in mai martaba ya shiga kamar yadda ya saba shi kad'ai ya zauna a akan kujera yana sauke ajiyar zuciya. kallon katin yake yana kallon sunan ta kamar a jikin sunan yana so ya gano wani abun.  _Sa'ar ka guda nasan darajar d'an adam da babu abinda zai hana ban wanke maka taka fuskar da mari kamar yadda ka mari tawa._ kalaman ta suka fad'o masa a rai ya runtse ido jin abinda bai tab'a ji ba yana kawo barazana ga kunnen sa.

     "Ta tab'a had'uwa da Aliyu" ya furta a hankali idanun sa har lokacin a kulle zuciyar sa na bugawa da sauri-sauri. "Wacece ita?" Ya tambayi kansa yana dafe kansa da duka hannayen sa idanun ta da goshin ta na sake dawowa masa cikin kansa da idanun sa a hankali.
Sake kallon katin yake maganar Khalil na sake dawo masa zuciyar sa ya kai idanun sa sunan asibitin da aka rubuta mata maganin. Mik'ewa  zaune yayi sosai mamaki ya kama shi ya wara idanun sa ganin sunan asibitin su ne ya tafi k'aramin tunani kafin ya d'auko waya daga aljihun sa da azama.

        Sai da ya danna number Dr Yasir ta shiga sai kuma yaji haushi ma akan me ma ya saka shi ya kira Dr, "Assalamu Alaikum, Ranka ya dad'e" muryar Dr ta katse tunani ya kalli wayar kamar bazai yi magana ba sai yace, "ehemmm Hydar" sai kuma yayi shiru jin hakan Dr yace, "Jikin sa ana samun ci gaba saura kiris ma ya farfad'o domin ana samun cigaba fiye da baya."
"About yarinyar da ya buge fa?." Gaban Dr ya Fad'i jin abinda yace yayi shiru Asad yace, "tana ina?."

            Dr yace, "Prince Mama ta saka an sallame ta tun kwanakin baya." Asad yayi shiru cike da mamaki yasan tsaf Mama zata aikata abinda yafi haka ma hakan ya saka shi yin shirun kafin yace, "meye sunan ta?." A sama Dr yaji maganar hakan ya saka shi yin shiru kafin yace, "na manta ne prince abubuwan da yawa marasa lafiyar da yawa babu lallai na rik'e." Shiru dukka sukayi kafin Dr yace, "Na tuna, sunan ta Rauda sunan mahaifin ne dai na manta."

       Asad baice komai ba ya yanke wayar ya sake kallon katin yaga sunan da ya fad'a masa ya ajjiye katin a gefe yana kallo, _Mama meyasa?, ga yarinya yanzu a cikin yanayi mara dad'i, babu kud'in magani gashi har tana yawo da sanda a silar Hydar._ ya fad'a a zuciyar sa yana sauke numfashi shi jikin sa duka babu dad'i.

        Kiran magrib ya tashe shi yayi alwala ya fita masallacin estate d'in yayi sallah sannan ya dawo ya  d'auki motar sa zuwa gida. Wajan Mama ya wuce kai tsaye bai same ta a falo ba ya shiga d'akin da Hydar yake a nan ya ganta a zaune kusa dashi kamar koda yaushe. Da sallama ya shiga ta kalle shi ta d'auke kai ya tsaya a kan Hydar yana kallon sa.  Har zai mata magana sai kuma ya fasa ya d'auke kansa itama kuma bata ce masa komai ba. Ganin bata kallon sa ya saka yace, "Mama ko meyasa aka sallami yarinyar da Hydar ya buge daga asibiti?" Ya fad'a a tausahe kamar ko yaushe. Kallon sa tayi ta harde hannun ta a k'irji tana kallon sa alamun bazata yi magana ba kenan.

"Na saka an sallame ta d'in sabida bata dace da zaman wannan asibitin ba akwai abinda za'a yi min ne?. kuma ahir naji kaje wajan ta da niyar wani abun, shima Hydar nice na dakatar dashi kar ka jawo abinda raina zai b'aci a kanta iya abinda aka yi mata a asibiti ya ishe ta" ta fad'a a kausashe tana kallon sa.  Ajiyar zuciya yayi yace, "Allah ya wuci zuciyar ki, ban fad'a dan ranki ya b'aci ba." Kai ta kawar gefe tayi masa alama da ya bata waje ya kuwa fita kamar yadda tace.

         Masallaci ya fara wucewa yayi sallah kafin ya nufi d'akin sa jikin sa duk babu dad'i, zuciyar sa na bugawa sosai yana jin bak'on abu yana zaga jikin sa kamar yadda jini yake zaga jijiyoyin jikin sa.  Yana tsallaka k'ofar d'akin yaji kansa yayi mugun sarawa ya tsaya cak yana bin wajan da kallo amma baiga komai ba ya runtse idanun sa.
"Lafiya?" Aliyu ya fad'a daga bayan sa ganin yanayin sa duk ya canja. K'arasowa Aliyu yayi yana kallon sa yace, "baka da lafiya?." Asad ya cize bakin sa ya kalle shi yace, "Kaina" abinda yace kenan ya shiga ciki shima yabi bayan sa.

          Suhail da yake lab'e a bayan babban gate d'in da ya raba apartment d'in su da gidan ya fito yana murmushi ya bar wajan da sauri ya fiddo waya daga aljinun sa ya danna kira ana d'auka yace, "An zuba masa kuma tabbas ya taka yanayin sa ma ya canja." Waziri yace, "Good boy." Daga haka ya yanke wayar yayi saurin barin gidan gabad'aya.

       Shigar Asad falo keda wuya kansa yayi mugun nauyi ya rasa me yake masa dad'i bai san lokacin da yayi saurin dafa bango ba yana furta, "Ya salam!." Ganin hakan ya saka Aliyu ya rik'o hannun sa yace, "you're not okay deaf, zauna" ya fad'a yana jan sa kan kujera ya zaunar dashi yana juya kansa. Yadda kansa yake mugun ciwo da sarawa fita yayi daga hankalin sa idanun sa suka firfito waje ya saka hannayen sa biyu ya dafe kansa yana ji kamar ana saka guduma ana dukan kansa.

         Aliyu ganin abin yayi yawa sai hankalin sa ya tashi ya zauna kusa dashi ya rik'e kan nasa jin yadda jijiyoyin kan nasa suke bugawa a guje sune ya sake tayar da hankalin sa yace, "oh my God wannan wanne irin ciwo ne?." Da sauri ya lalubo waya ya kira Dr Yasir amma bai same shi ba ya tashi tsaye ya kira number Mama ya sanar da ita halin da ake ciki.

        A gigice Mama ta tawo apartment d'in nasu gab da zata shiga Hafiz ya tsaya a gaban ta yace,"Mama kar ki wuce nan wajan." Hararar sa tayi kafin tace wani abu yace, "Wani abu aka zuba masa ya wuce ta wajan, kalli kiga" ya fad'a yana nuna mata wani bak'in ruwa a wajan ga garin magani a cikin sa har yellow yake yi.

Kallon wajan take gaban ta na fad'uwa da sauri ta k'arasa ta kunna hasken wayar ta ta sake haska wajan ta kalli Hafiz tace, "Waye ya shigo nan b'angaren?." Hafiz yace, "ban sani ba Mama."
"Kuna ina! Kuzo nan" ta fad'a cikin d'aga murya sosai masu tsaron wajan suka k'araso a guje suka zube kafin suyi magana tace, "Kafin Asad ya shigo wajan nan waye ya shigo?." Jikin d'aya yana rawa yace, "Ranki ya dad'e Suhail ne ya shigo."

"Suhail again" ta fad'a tana dafe kanta kafin ta juya da sauri ta nufi falon Asad d'in, bata sake bi ta kan maganin dake wajan ba ta tsallaka ta shiga ta same shi a zaune hannu sa duka biyu a kan sa jikin na rawa sosai. Da sauri ta k'araso ta rik'e shi ta d'ora hannun ta a akan sa tace, "Aliyu kayi wani abun please." Aliyu yace, "Mama na kira Dr yana hanyar zuwa yanzu."
"Sannu Asad" ta fad'a kamar zatayi kuka tana kallon sa.

      Ya canja lokaci d'aya jijiyoyin kansa sun fito radau jikin sa na rawa sai juya kai yake alamun yana cikin azabar ciwo, hankalin Mama ya sake tashi ganin numfashin sa yana k'ok'arin tsayawa ta kalli Aliyu da yake a tsaye hannun sa rik'e da waya shima duk ya rud'e. Shigowar Dr Yasir ya saka Mama kallon sa tana fad'in, "yi sauri kazo ka duba shi." A guje ya k'araso ya tab'a kan Asad jin yadda yake bugawa sai da ya d'auke hannun sa da sauri.

         Hannun sa har rawa yake ya saka masa ruwa ya kuma yi masa allura ya fara auna bp sa, abinda ya bashi mamaki komai normal yake dan yadda yaji kansa yana bugawa ya d'auka ko jinin sane yayi k'asa hakan ya saka ya kalli Mama itama shi take kallo duk rauni ya bayyana a tare da ita kamar zatayi kuka. Hannu Asad ya saka ya cire ruwan da yake shiga jijiyoyin sa sabida ji yake kamar azaba tana shiga cikin jikin sa. "A'a Asad ya zaka cire?" Mama ta fad'a tana kallon sa hankali a tashe.

Juya kan nasa yake yi cikin tsawa Mama tace, "Dr kana ganin abinda yake yi ka tsaya kana kallon sa!?." A firgice ya kalle ta yace, "Ranki ya dad'e na rasa gane kan matsalar, bara nayi masa allurar bacci" ya fad'a da gaggawa yana yi masa allurar bacci amma ko gezau baiyi ba.

Aliyu yace, "Dr muje asibiti kamar zai fi." Hafiz yace, "No prince zaman sa a nan yafi safe, dan Allah Yasir kayi iya k'ok'arin ka a samu yayi bacci."  Gabad'aya sun rud'a Dr ya rasa ma abinda zaiyi yayi masa allurar bacci baya son sake yi masa wata dan tabbas zai zama cikin risk domin abubuwan zasu yi masa yawa a blood d'in sa. "Prince in aka sake masa another injection abubuwan zasu yi masa yawa" ya fad'a yana kallon Aliyu.

"Kayi masa mana, ko meye kayi masa abinda zai bar wannan condition d'in!" Mama ta fad'a a fusace tana kallon sa dan hankalin ta a tashe yake, bai san sanda ya balle kan allurar ya ja a sirinji ya dannawa Asad a jijiyoyin jikin sa. Lumshe idanu Asad ya fara yi har lokacin yana rik'e da kansa idanun sun k'i rufewa yadda ake so.

      Abin mamaki da al'ajabi Dr ya tsaya yana kallon ganin har lokacin bacci bai d'auke sa ba sai kansa ya kulle ya rasa abinda zai bashi kuma nan gaba. Domin allurar da yayi masa bata second biyar a jikin mutun bata saka shi bacci ba. Hafiz da yake tsaye ya lura da yanayin Dr hakan ya saka ya k'arasa wajan fridge da sauri ya d'auko ruwa ya bawa Mama yace, "Mama ki masa tofi ya sha zai fi samun sauk'i." Ba musu ta karb'a ta fara tofa masa duk ayar da tazo bakin ta kafin ta bashi yasha ta shafa masa ragowar a fuskar sa. Komawa gefe Dr yayi yana kallon ikon Allah har lokacin bacci bai d'auke Asad ba kuma kansa bai daina ciwo ba.

      "Hafiz kama shi mu kai shi d'aki ya kwanta" Aliyu ya fad'a yana kallon Hafiz. Tare suka d'aga shi aka kai shi kan gado ya kwanta har lokacin hannun sa na dafe da kansa idanun sa kuma a bud'e. Mama na zaune a gefen sa hannun ta guda d'aya ta rik'e nasa tana tofa masa addu'a a hankali, sun kwashe sama da mintina arba'in a wajan kafin bacci ya d'auke shi.

     Ajiyar zuciya Mama tayi ganin yayi bacci ta kalle su da suke tsaye har lokacin bata ce komai ba ta mik'e aka ja masa k'ofar aka fita ta kalli Dr hakan ya saka shi yace, "Ga magani na koma na d'auko masa in ya farka sai ya sha. Nayi mamakin ciwon nan nasa ban tab'a karo da ciwon kai irin wannan ba gaskiya" ya fad'a yana ajjiye maganin akan table.

Bata ce komai ba ta fita da sauri ta dinga kiran masu tsaron wajan suka k'araso a guje suka zube ta kalle su tace, "Daga yau ban amince a sake barin kowa ya shigo wajan nan ba, ko waye ko wace ban amince ba in kuma aka sab'a abinda na fad'a....." Bata k'arasa ba ta girgiza yatsan ta guda kafin ta bar wajan da sauri.

       Tana shiga b'angaren ta d'akin da Hydar yake ta shiga yana kwance inda yake ta fita ta koma d'akin ta. Waya ta d'auka hannu na rawa ta zauna jikin ta duk yayi sanyi ta nemi number mahaifin ta ta kira shi. yanke kiran aka yi hakan ya bata tabbacin zai kira ta kenan bata ajjiye wayar ba kuwa kiran ya shigo, da sallama ta d'auka muryar ta na rawa sosai kafin tace, "Barka da dare Abbie." Jin maganar ta a haka ya saka yace, "Ban saba jin rauni a muryar Rabi'atu ba, me ya haifar da hakan?."

          Kuka ta fara yi mara sauti kafin tace, "Abie suna neman su kashe min Hydar da Asad. Hydar na kwance har yanzu baya motsawa ga Asad can yanzu na baro wajan sa kansa na ciwo dak'yar aka samu yayi bacci. Ban san me suke nema a wajan su ba so suke suga bayan su."
Abie ya murmusa yace, "Babban kuskuren mijin ki da ya furta zai sauka daga kan kujerar sa ya bawa Asad wannan shine kuskure babba da ya tafka. A yanzu zakiyi mamakin adadin wad'an da suke harin rayuwar Asad sabida son mulki, mulki yana sakawa mutane suyi komai a kansa, mulki yana sakawa idon mutane ya rufe suga in basu samu abinda suke so ba zasu iya ganin bayan kowa. Baza su barki kiji dad'i ba sai kin dage da addu'a sosai dan itace maganin ko wanne mugu. Kiyi hak'uri ki bar lamarin a hannun Allah, nima kuma ina taya ki addu'a bama ke kad'ai ba dukka y'an uwan ki."

"Allah yaja da ran mahaifina lamarin nasu ne yayi yawa na rasa inda zan saka kaina."
"Zama uwa ga sarki ai ba abu bane mai sauk'i ba Rabi'a, duk inda kike tunanin wahalar sa ya wuce nan sai kin jure dole. ki cigaba da addu'a kawai ban amince kiyi shirka ba Allah kawai zaki rok'a zai miki maganin komai. Zan bada sak'o a kawo miki kuyi amfani da maganin dukkan ku."
"An gode Takawa, Allah ya ja kwana, Allah ya tsare, Allah ya rufa asiri" ta fad'a da girmamawa kafin suyi sallama ya katse kiran ta sauke numfashi, ko babu komai hankalin ta ya kwanta da kalaman mahaifinta masu sanya nutsuwa.

*☆☆☆*
        "Umma k'afa ta ciwo take min" ta fad'a tana hawaye mai zafi tana cize bakin ta. Umma hankalin ta duk ya tashi ta kunna k'aramar fitilar hannun ta tace, "Sannu Rauda, kiyi hak'uri kita yiwa k'afar addu'a zata daina in sha Allah." Kai take juyawa kawai sosai k'afar take ciwo rashin shan maganin da bata yi ba.

"Gashi kin cillar da katin maganin balle na fita naje wajan mai chemist d'in nan na baya naji ko za'a samu wasu daga ciki na karb'o miki. Kwalayen ma kin watsar balle naje dasu." Ita dai bata ce komai ba sai juya kanta da take yi kawai hankalin Umma yak'i kwanciya. Addu'a ta dinga yi mata a k'afar haka suka raba dare sai gabanin biyun dare sannan bacci ya d'auki Rauda sai a lokacin Umma ma ta runtsa.

         Da asuba Umma taso makara Allah ya taimaka ta tashi bayan ta idar da sallah Baba ya shigo take shiga d'akin sa tace, "Malam daman magana nazo muyi." Yace, "to ina jin ki."
"Akan k'afar Rauda ne jiya kusan kwana mukayi babu bacci tana ta kuka tana yi mata ciwo rashin shan maganin da bata yi ba kwana biyu,  shine nace zamu shiga gidan radio ko muje gidan sarki tunda yana taimakawa mu nemi taimakon kud'in maganin."
Baba yace, "gwara ma gidan sarkin yana taimakawa sosai da zarar maganar taje gaban sa, gidan radio sai aita yad'awa amma kaji shiru wani lokacin. zan tambaya anjima naji yana gari sai aje in sha Allah kuma zai taimaka."

"Allah ya sa" Umma ta furta jikin ta a sanyaye ta juya ta fita. Baba yana ganin ta fita ya k'arasa wajan ajiyar kud'in sa ya tsohuwar riga duk ta yage baza ka tab'a d'auka akwai kud'i a cikin ta ba ya fiddo da kud'in yana kalla, murmushi yayi yace, "da zan iya da an siyi maganin amma bazan iya cire kud'i masu yawa akan magani kawai ba gwara a fita neman taimakon shima riba ce" ya fad'a yana tattare kud'in ya mayar dasu ma'ajiyar su ya fito daga d'akin.

         Da gari yayi haske Rauda ta tashi babu laifi taji dad'in k'afar ta yi wanka ta karya tana zaune a kan farar kujerar da take zama sabida sauk'in tashi tsaye.
"Sallamu alaikum wai ana sallama da Rauda a waje." Yaro k'arami ya fad'a daga soron gidan.

Umma ta d'ago labule ta fito tana fad'in, "Sallama da Rauda kuma? In ji waye?."
"In ji Bala mai pharmacy" ya bata amsa yana kallon Umma. Umma tace, "to jeka kace gata nan." Yaron ya Juya ya fita Rauda ta kalli Umma tace, "Umma naje nayi masa me?."
"Jeki Rauda bamu sani ba ko hak'ura yayi ya kawo miki maganin."
"Ni dai Umma bazan je ba babu cin fuskar da bai min ba jiya."
"To ni bara na je" Umma ta fad'a tana niyar juyawa ta shiga d'aki ta d'auko mayafi.

      Mik'ewa Rauda tayi tace, "Zanje" ta fad'a tana d'aukar sandinan ta tana tafiya a hankali har ta fita soron gidan ta tarar dashi a tsaye da leda a hannun sa. Yana ganin ta yayi murmushi yace, "Rauda sannu, ya k'arfin jikin?."
"Da sauk'i, lafiya kake nema na?."
"Lafiya lau. Maganin na kawo miki nazo kuma na shaida miki duk bashin da yake kan ki an biya an kuma siya miki maganin da zaki ta sha har ki warke, dan haka daga wannan ya k'are azo a karb'a a waje na."

Kallon sa take tana kallon maganin da yake mik'o mata a leda kafin tace, "An siya min? Kuma an biya min bashi?, waye wanda ya siya har ya biya min bashi?." Bala ya gyara tsayuwa yace, "to wanda ya siya d'in aiko min akayi ba shi yazo da kansa ba, amma dai an siya miki."

"Waye wannan wanda zai siya min magani?" Ta fad'a a bayyane fuskar ta d'auke da zallar mamaki.

*Nima kaina abin ya bani mamaki waye ya siyawa Rauda magani kuma?.*⛹‍♀️⛹‍♀️⛹‍♀️

Continue Reading

You'll Also Like

1K 146 16
The legendary story about the mysterious hidden🌄🌄 island the numerous of people and evils fails to find out about it. But find by the unremembere...
231K 16.9K 21
Avantika Aadish Rajawat Aadi, with his fiery nature, adds intensity and excitement to their relationship, igniting a spark in Avni. Avni, like the ca...
KASHI By stuckinatale

General Fiction

398K 19.9K 42
"So, Mrs. Kashi Abhay Pratap Singh..chalte hai. Goodbye..". Saying this, he left her broken in this world of betrayal. ~~~~~~~~~~ Kashi, a simple gir...
126K 7.2K 45
Complicated🤐🤐🤐 Find out👇👇👇