KWANTAN ƁAUNA

By Nana_haleema

2.4K 136 17

Izza, mulki, k'asaita sun tattara a gare ta ita kad'ai. Y'ar sarki ce, jikar sarki, matar sarki. Bata k'aunar... More

001
002
003
004
005
006
007
009
010
11
012
013
014
015
016
017
018
019
020
021
022
023
024
025
Trailer
KWANTAN ƁAUNA Book2

008

69 5 0
By Nana_haleema

*KWANTAN ƁAUNA*
        FitattuBiyar 2023

             ©️ *Nana Haleema.*

*008.*

         Washe gari ta kama ranar Asabar kamar jiya da wuri Hydar ya d'auki mota ya tafi asibitin da Rauda take duk da ciwon kan da yake fama dashi haka ya jure dan da ita ya kwana a ransa.  Dak'yar ya iya k'arasawa yayi parking motar ya shiga cikin asibitin kansa na sara masa sosai. D'akin da take ya fara shiga da sallama a bakin sa cikin takun nutsuwa da izzar sarauta da k'asaita da take yawo a cikin jijiyoyin jikin sa.

        Yana shiga idanun sa ya sauka a cikin na Rauda da take kallon wanda ya shigo, bai d'auke idanun sa daga cikin nata ba ganin yadda idanun ta sukayi ja duk da bai san su a yadda suke a baya ba amma yadda ya gan su ya san sun canja.  Kwarjini da fad'uwar gaban da ta ziyarci k'irjin ta ya saka ta janye idanun ta ta saukar k'asa duk da tsananin azabar da take ciki.

Babu kowa a d'akin sai ita kad'ai ya k'araso yana yatsine fuska sabida kansa ba k'aramin sarawa yake yi ba, ko takawa yayi sai yaji takun har kwakwalwa sa. Kallon ta yake yi ganin yadda take juya kanta kana gani kasan tana cikin azaba jikin ta har rawa yake ga k'afar tata a d'aure goshin ta manne da flasta, k'arewa fuskar ta kallo yake a karon farko k'irjin sa ya cigaba da bugawa yayi saurin d'auke fuskar sa yana kallon gefe guda.

Bud'e k'ofar akayi aka shigo ya kalli wanda ya shigo yaga Dr ne da kuma mahaifin ta ganin sa ya saka Dr k'araso yace, "barka da zuwa." Idanun sa ya lumshe ya bud'e kafin ya kalli Baba kafin yayi magana Baba yace, "Barka da safiya, da fatan an tashi lafiya."
"Ya mai jiki?" Ya furta a nutse yana kallon Baba.

"Mai jiki da sauk'i" Baba ya bashi amsa jikin sa har rawa yake yi.  Hydar ya kalli Dr baiyi magana ba hakan ya sake yace, "Komai zai tafi dai-dai in sha Allah." Kai kawai ya girgiza ya juya zai fita cikin takun isa sai kuma ya tsaya cak ya juyo yana kallon Baba kafin yace, "ba wani damuwa?."
Sai kuwa Baba ya gyara tsayuwa yace, "To Alhaji kasan lamarin abubuwan sai a hankali, ga gida ba abinci ga kud'in motar zuwa asibiti ga kuma......." hannu Hydar ya d'aga kawai baice komai ba ya saka hannun a aljihu ya d'auko d'aurin dari biyar guda biyu ya mik'awa Baba ya k'araso jikin sa har yana rawa ya karb'a baice komai ba bai kuma bari Baban yace komai ba ya fita.

Baba yabi kud'in da kallo yayi murmushi yana shafa fuskar sa yace, "To ke Rauda ai sai ayi fatan ki ta zama a asibiti wannan abin arzuk'i haka?, tunda nake na d'auka zan rik'e kud'i manya haka nawa na kaina ni kad'ai? Ai ban tab'a ba sai silar kwanciyar nan taki. Yo ba sai nayi ta addu'a kita zama ba indai irin wannan zasu zo hannu."

Rauda kallon Baba take yi duk da ciwon da take ciki hakan bai hana jin takaici da bak'in ciki a zuciyar ta ba, ji ta kud'i ma yake bata lafiyar ta ba gashi da ya shigo ko ya jiki bai mata ba dan ta fahimci shine ya buge ta.
Hydar dak'yar ya iya zuwa office d'in Dr ya zauna kansa yana juyawa a ya saka duka hannayen sa biyun ya dafe kansa, ganin hakan hankalin Dr ya tashi dan masomin tashin ciwon Hydar kenan hakan ya saka shi ya rud'e yace, "Prince lafiya? Me yake damun ka?."

        Kansa yake nuna masa jikin sa har rawa yake hankalin Dr ya tashi ya kalle shi yace, "Prince kana buk'atar drip." Kai ya girgiza alamun a'a kafin kuma ya ja dogon numfashi jin yadda kansa yayi mugun sarawa daga nan idanun sa duhu ya mamaye su amma duk da haka yak'i kulle idanun nasa.
"Prince! Prince!! Kana jina?, Prince!!!" Dr ya fad'a hankali a tashe amma lokacin idanun Hydar ya rufe ruf yana zaune idanun sa a kulle jikin sa ya saki duka.

"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un" abinda Dr yake maimaitawa kenan jikin sa na mugun rawa ya bud'e k'ofar Office d'in sa yana fad'in, "Nurse!, Ashiir kana ina?!" Ya fad'a da k'arfin gaske wanda yake kira ya tawo a guje. "Zo ka taimaka min" ya fad'a yana komawa ciki suka shiga tare suka d'aga Hydar da jikin sa yake a sake kamar gawa  suka d'ora shi akan gado Dr hankalin sa tashe suka tura gadon Hydar zuwa babban d'aki na musamman.

Ta underground aka shiga babu wanda zaice akwai wani d'aki ko hanya a wajan aka shiga da Hydar aka jona masa ruwa na'urori sai da ya tabbatar yayi masa abinda ya kamata sannan ya fito da sauri yana kiran wayar Mama amma bata d'aukar wayar.

Dafe kansa yayi hannun na rawa ya rika number Asad kamar yadda yayi zato bazai d'auka ba bai kuma d'auka d'in ba, "Hasbunallahu wani'imal wakil" ya furta yana danna layin Aliyu shima bai d'auka ba har kira biyu.
Suhaima ya kira na farko bata d'auka ba sai a na biyun yana ganin ta d'auka da sauri yace, "Princess where are you?."
"At home."
"Ina Mama?."
"Lafiya?."
"Ki sanar da ita Hydar yazo nan wajan yarinyar da ya kad'e kuma ciwon sa ya tashi yanzu haka yana kwance."

      "What!" Ta fad'a a firgice tana dirowa daga kan gado ta fito daga d'akin ta cikin sauri, bata yi tafiya mai nisa ba ta iso babban falon mahaifiyar tata bata same ta a shi ba ta nufi ciki ta ganta a tsaye tana amsa waya, "Mama ciwon Yaya Hydar ya tashi" ta fad'a a firgice bata jira ta gama wayar ba ma. Ba shiri ta sauke wayar daga kunnen ta ta zaro idsnu tace, "me kika ce? Ciwon Hydar? Yana ina?."
"Dr Yasir ne ya kira ni yake sanar dani yanzu haka ma yana asibiti."
"Oh my god!" Mama ta fad'a tana yin ciki da sauri.

Ita da sauri ta koma ta canja kayan jikinta da sauri ta dawo ta tarar Mama har ta fita tabi bayan ta da saurin gaske, a mota ta samu Mama da sauri ta shiga kusa da ita aka ja motar aka fita da motar da saurin gaske.

         Hajiya tana tsaye jakadiyar ta ta shigo a guje tana haki ta zube a gaban ta, da sauri ta juyo ta kalle ts tana fad'in, "ke kuma lafiya zaki fad'o min ko sallama babu."
"Tuba nake ranki ya dad'e, Allah ya wuci zuciyar ki."
"Lafiya?."
"Wato ranki ya dad'e ciwon yarima Hydar ne ya tashi yanzu zancen da nake miki gimbiya ta tafi asibiti wajan sa." Waje Hajiya ta samu ta zauna tace, "yanzu kenan abin ya faru?."
"Yanzun nan ranki ya dad'e dan yanzu ta fita a gigice da ta shirya tafiya Kano amma a halin yanzu tafiyar ta watse."

Kyakykyawan murmushi tayi tana cize baki tace, "jeki."
"Na gode ranki ya dad'e, ki huta lafiya" ta fad'a tana fita jiki na rawa ta bita da kallo tana murmushi.

"Master planer!" Ta furta a bayyane tana murmushi ganin duk abinda ta tsara ya tafi nan take taji farin ciki yana mamaye mata zuciyar ta. Y'arta Khaleesat sa'ar Suhaima ce ta shigo ta kalle ta itama ita take kallo tace, "Khaleesat kin san me nake so dake?." Kai ta girgiza kai Hajiya tace, "Jeki ki samo min zogale yanzun nan."
Wara idanu tayi tace, "zogale? Hajiya a ina zan samo zogale yanzu?."
Tsaki taja ta shige ciki ita ma tabi bayan ta da sauri.

          B'angaren Mama a gigice suka isa asibitin b'angaren da aka ajjiye shi shiru wajan babu motsin komai tsittt ko tsuntsu baya bi ta wajan ta shiga inda Hydar yake kwance, yana kwance sanb'al kamar koda yaushe ko ina na jikin sa baya motsi an jona masa na'ura a kan sa idanun sa a kulle ko wanne lokaci. Kallon Dr tayi ta kalli Suhaima da take gefen ta ta dawo da kallon ta ga Dr tace, "me yazo yi asibitin nan?."
"Ranki ya dad'e yazo duba yarinyar da ya buge ne."
"Yarinyar da ya buge? Kana so kace min a wannan asibitin ya ajjiye y'ar talakawar da ya kad'e?."

Suhaima tace, "Mama muje waje kin san ba'a yi masa hayaniya." Ba musu duka suka fito ta kalli Dr tace, "Kai nake sauraro."
"A nan ya ajjiye ta ranki ya dad'e, yau d'in ma yazo duba ta ne."
"Ita wacece da zai zo duba ta da safe ko wajena bai shiga na gansa ba?, me take dashi?."

Dr yace, "Bata da komai ranki ya dad'e." A fusace tace, "a kan me za'a ajjiye ta a nan? Meya zo yi wajan ta ko wajena bai shiga ba?, me yake nufi da yarinyar nan?." Shiru Dr yayi ya sunkuyar da kansa k'asa baice komai ba tace, "akan ta Hydar ya kwanta rashin lafiya, yasan ba'a son ya cika zirga-zirga mussmman da safe amma sabida ita yake fitowa har hakan ya kai shi ga kwanciya, y'ar gidan uban wacece?."

Dr yace, "Allah ya wuci zuciyar ki, ba y'ar kowa bace hasalima iyayen ta talakawa ne." Dogon tsaki taja takaici da bak'in ciki na damalmale mata zuciya tace, "Ayi gaggawar sallamar su daga asibitin nan su koma asibitin gwamnati suje can su k'arata, bazai yu yana kwance a nan itama tana nan ba matsayin su ba d'aya bane ka gane ko?." Kai ya girgiza alamun eh cikin girmamawa tace, "a shirya komai zai tafi da Hydar gida" ta fad'a tana niyar komawa d'akin Suhaima tace, "But Mama zaman sa a nan zaifi samu kulawar da ake nema." Hararar ta tayi hakan ya saka ta yin shiru bata ce komai ba domin an gama magana ta shiga ciki.

Suhaima ta kalli Dr tace, "please Dr ka bar yarinyar ta samu sauk'i in yaso sai ku sallame ta, a bata kulawar da ya kamata please" tana gama fad'a tabi bayan maman ta shima ya bisu da kallo. K'irji ya dafe yana fad'in, "Allah ya fidda ni lafiya" ya Fad'a shima yana bin bayan ta.

Yana shiga ta kalle shi tace, "a had'a komai zamu tafi dashi gida." Kai ya girgiza da sauri ya fita aka had'a mota nan da nan aka turo gadon da yake kai aka saka shi a mota ita da Suhaima suka shiga bayan wata motar ta kalli Dr tace, "a tabbatar yarinyar nan ta bar asibitin nan."
"In Allah ya amince ranki ya dad'e." Daga haka aka ja motar aka tafi.

        Har k'ofar apartment d'in ta aka je da motar aka bud'e da gaggawa aka tura gadon da yake kai zuwa cikin babban d'akin da yake kusa da nata, a kan gadon da yake kai aka barshi Dr ya jona masa abubuwan da aka tawo dasu ya tabbatar komai yayi sannan ya tafi. Kallon sa take ta zauna a gefe ta rik'e hannun sa jikin ta duk yayi sanyi domin abubuwan suna neman fin k'arfin ta.

       B'angaren Asad bai san abinda yake faruwa ba dan bai ma kalli wayar sa ba ya fito daga d'aki zuwa falo babu kowa daman dai yasan Aliyu baya nan amma yayi mamakin rashin ganin Hydar, numfashi ya sauke ya juya zai koma yaji maganar Hajiya a bayan sa tana fad'in, "Asad."

        Juyowa yayi yana kallon ta ya d'an saki murmushi kad'an yace, "barka da rana Hajiya."
"Barka ka son, ya komai da komai."
"Alhamdulillah" ya amsa yana d'auke kansa gefe.
"Mafarki nayi da mai babban d'aki daren jiya sai ta tuna min da k'aunar ka da zogale hakan ya saka ni shiga kitchen da kaina na had'a maka, ina fatan zakayi farin ciki?" ta fad'a tana mik'a masa bowl da aka rufe shi da foil.

       Ba musu ya sanya hannu ya karb'a ya murmusa yace, "Godiya nake." Itama ta fad'ad'a murmushin ta tace, "Babu komai kar ka damu Asad" ta fad'a tana juyawa ta fita baice komai ba ya ajjiye bowl d'in ya shiga d'aki. Jim kad'an ya fito ya tarar da bowl d'in kamar yadda ya barsa ya zauna ya bud'e, zogalen ya burge shi sosai yaki kayan had'i yadda ya kamata hakan ya saka shi deba da hannun sa ya kai baki sai kuma ya dakata.

_Hajiya kamar Mama take baza ta bani abinda zai cutar dani ba, yeah baza ta cutar dani ba tana sona._ ya fad'a a zuciyar sa ya kai zogalen bakin sa yana taunawa a hankali. Sosai yayi masa dad'i ba kad'an ba dan ya jima bai ci ba ya cigaba da ci har ya kusa cinyewa sannan yaji ya ishe shi ya tashi ya bar shi a wajan ya shiga d'aki.
Yana fitowa daga d'akin yaga Mama a tsaye ita da Suhaima ya kalle ta ya durk'usa har k'asa yace, "barka da fitowa."

Bata kalle shi ba tace, "Daman yau a cikin abinda ake kawo maka breakfast har da zogale?." Mik'ewa tsaye yayi ya kalli bowl d'in ya kalle ta yace, "A'a Hajiya ce ta kawo min d'azu." Mama ta wara idanu tace, "wacce Hajiya kenan?."
"Hajiya dai."
"Amma dai baka ci ba ko?." Kallon bowl d'in yayi ya kalli Mama yace, "ki gafarce ni,na ci."

"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, Asad why" ta fad'a a gigice tana kallon sa kamar zata zubar da hawaye. Marairaicewa yayi baice komai ba yana kallon ta, "Asad meyasa baka ganewa ne kai? Meyasa kake d'auka yadda zuciyar ka take mai kyau haka ta kowa take da kyau?, meyasa yadda kake ganin baza ka cutar da kowa ba haka kowa yake?.  Baka san a yanzu ba abincin kowa zaka ci ba?, meyasa kaci abin hannunta?, akan me baka sanar dani kafin kaci ba?!" Ta k'arasa fad'a cikin fad'a tana kallon sa.

        Runtse idanun sa yayi ya sunkuyar da kansa baice komai ba, sake tunzura ta yayi ganin yayi mata shiru tace, "baza kayi magana ba sai na mare ka?." D'agowa yayi ya kalle ta a sanyaye yace, "Allah ya wuci zuciyar ki."
"Asad meyasa kaci yanzu in ta zuba maka guba a ciki ka mutu fa? Ya kake so nayi kenan?." Nan ma shiru yayi baice komai ba ta rik'e hannun sa tace, "muje duk yadda zakayi ka amayar da abinda kaci zai maka illa Asad" ganin duk ta rud'e sai ya rik'e nata hannun shima yace, "Calm down Mama, babu abinda zai same ni sai Allah ya nufa."
"Asad tana so ta cutar da kai ba tun yau ba zata iya aikata komai wajan ganin ka cutu, kar ka kuma cin abin hannun ta dan Allah" ta fad'a kamar zata zubar hawaye tana kallon sa.

       Kai ya girgiza alamun to yana kallon Maman tasa da girmamawa kamar ko yaushe  kallon sa take itama kafin tace, "Baka jin komai a jikin ka?." Kai ya d'aga alamun eh kafin tace, "jikin Hydar ya tashi Asad kazo muje ka gan shi" ta fad'a tana fita shima ba musu ya biyo bayan ta. D'akin da yake suka shiga yana kwance kamar ko wanne lokaci Aliyu na tsaye a gefen sa yana kallon sa Asad ya k'arasa d'aya barin yana masa addu'a yana tofa masa a fuskar sa.

         "Mama garin ya hakan ta faru?" Aliyu ya tambaya yana kallon Mama. Mama tace, "akan wata banza y'ar talakawa ya fita da safe, yarinyar nan da ya buge wai yaje dubawa da safe nayi masa warning akan zuwa inda take amma baiji ba gashi ya kwashi sanyi ciwon sa ya tashi." Aliyu ya tab'e baki yana kallon gefe baice komai ba.
"Assalamu alaikum, surprise" aka fad'a daga baya ana shigowa d'akin.

      Dukkan su kallon k'ofar suka yi banda Asad da har lokacin yake wa Hydar addu'a, Suhaima ta wara idanu tace, "Sis oyoyo" ta fad'a tana hugging nata itama ta rike ta tana murmushi. Har k'asa ta duk'a ta gaisa Mama ta amsa da fara'a tace, "lallai kam surprise, ina Mum d'in?."

       Murmushi tayi wanda ya bayyanar da asalin kyaun ta tace, "Mom tana gida. Mama Yaya Hydar ne babu lafiya?." Kai ta d'aga mata kawai ta k'arasa inda Asad yake tsaye tana kallon Hydar. Sai kuma ta kalli Asad da bai kalle ta ba ta d'an bugi kafad'ar sa  tace, "Kana gani na ko magana babu ko bro? I'm sorry in kaji babu dad'i jiya bance maka zan zo ba, ina so na baka mamaki ne."

       D'ago idanun sa yayi yana kallon ta nan take gaban ta ya fad'i ta d'an yi baya ta kalli Suhaima da take kunshe dariya tace, "deaf kenan, ga Bro Aly nan kina gani." Wara idanu tayi tana kulle bakin ta tana kallon Asad ya d'auke kansa daga kallon ta takaici kamar ya kashe shitace, "Sorry Boss."

In ta samu kallon arzuk'i ma da ta godewa Allah ta bar wajan ta koma inda Aliyu yake shima bai kalle ta ba tace, "Yau sai naga kai ka koma min shi shi ya koma min kai."
Irin kallon da ta samu daga wajan Asad shi yayi mata shima sai ta kalli Mama sai taga Mama tayi murmushi tace, "Yau suna so su rikita ki ne."  Sai kuma Aliyu ya murmushi ya mik'a mata hannu alamun su gaisa.

Sai tayi murmushi ta bashi nata hannun suka gaisa kafin yace, "Welcome" yana furta hakan ya mik'e tsaye har lokacin hannun sa na cikin nata yana binta da kallo itama haka kafin ya zame hannun sa ya fita. Mama ta kalle ta tace, "Jidda kije ki huta, Asad kaje ina zuwa." A hankali yake takawa ya fita ta bishi da kallo tana murmushi Mama na kula da ita itama ta murmusa bata ce komai ba suka fita aka bar Hydar dake kwance.

        Asad tunda ya bar wajan zuciyar sa take masa zafi har ya koma apartment d'in su ji yake kamar ya fashe da kuka sabida takaici. A bakin window ya tsaya yana furzar da iska mai zafin gaske jikin sa har zafi ya d'auka sabida takaici da zallar bak'in ciki. Ta yaya Mama zata ce wannan yarinyar ce zata kasance matsayin matar sa nan gaba?, yarinyar da a gaban sa take gaisawa da namiji wanda ya kasance yayan sa kuma jinin sa, kenan sun saba tunda gashi yana bata hannu ta bashi suka gaisa. dogon tsaki yaja lokacin da ya tuna dukan kafad'ar sa da tayi alamun sun saba ma irin wannan banzayen halayen da Aliyu.

      Kowa yasan shi yana da kishi ko takalmi akace wannan mallakin sane tofa bai aminta yaga wani da takalmin ba sai shi kad'ai balle matar aure, kai yake girgizawa a hankali yace, "Mama bazan iya auren ta ba, I'm sorry" ya fad'a yana barin wajan.

        So yake ya bar gidan yaje company amma ya kasa baya son fita gabad'aya wani irin abu yake ji a jikin sa kamar ana zare masa kuzarin jikin sa.
Zama yayi a kan kujera yana furzar da iska kafin ya buɗe idanun sa ya mik'e zaune yana wara idanun sa a bangon d'akin, dafe kai yayi ya jingina da kujera ya rasa gane fuskar yarinyar da yake mafarki da ita amma yana jin tashin amon muryar ta a kunnen sa amma fuskar ta tak'i tsayawa a idanun sa.
Ko yanzu yaji maganar ta zai iya ganewa amma banda fuskarta gashi ta maqale a zuciyar sa kowa ya motsa sai ya tuna da ita.

       B'angaren Mama suna shiga d'aki ta kalli Jidda tace, "Amma kwanaki zaki mana ko?." Ta yi farrr da idanun ta kana tace, "A'a Ranki ya dad'e anjima da daddare zan wuce."
"To kije yanzu wajan Asad ku gaisa amma nasan Aliyu abokin kine ki daina nuna hakan a gaban Asad, lemme tell u something about your husband to be. yana da kishi, in ya nuna abu aka ce wannan naka ne yace kuma inaso to duk duniya babu wanda zaiyi amfani da abun nan sai shi kad'ai, in kuwa yaga wani ya rab'i wannan abin da yake so tabbas zai bar masa ne shi ya hak'ura. So u have to be very careful Jidda in kuna tare bakya ganin kowa sai shi koda Aliyun ne in ba haka ba zaku yi fad'a" ta fad'a tana kallon ta.

          Juya idanu Jidda tayi jin abinda akace mata sai farin ciki ya mamaye mata zuciya cikin muryar ta mai dad'in ji tace, "In sha Allah zan kiyaye ranki ya dad'e, bara naje wajan sa" ta fad'a tana ficewa Suhaima ta bita da kallo ta kalli Mama tace, "Mama Asad da Jidda sunyi bala'in dacewa, wannan suka tashi haihuwar yara za'a ga larabawa." Murmushi kawai Mama tayi dan ita badan kyau ta had'a su aure ba akwai manufar ta kafin ta fita ya koma d'akin da Hydar yake kwance.

        Asad yana zaune a inda yake aka shigo da sallama ya amsa ba tare da ya kalli wacce ta shigo ba yaji an zauna kusa dashi bai kalle ta ba tace, "barka da hutawa my Asad." Bai kalli inda take bama balle ta saka ran zai amsa. Daman tasan za'ayi haka tayi murmushi cikin shagwaba tace, "Kayi min magana mana." Nan ma bai kalle ta ba idanun sa a kulle suke.

"Dan kai fa na baro gida nazo nan amma shine baza ka kula ni ba?" Ta fad'a a shagwab'e. Nan ma banza babu amsa ta kuma cewa, "My Asad please." Numfashi ya sauke ya juyo ya kalle ta baice komai ba ya sake d'auke kansa yana cize baki lokaci d'aya yaji cikin sa na k'ullewa.

        Ganin hakan sai tayi shiru bata sake magana ba dan tasan kallo na kin ishe ni ne hakan ya saka ta yin shiru tana kallon sa yana yamutsa fuska. Sun jima a haka a zaune kafin ya cize bakin sa ya furta, "Ya salam!." Mugun ciwo cikin sa yake yi bai san sanda ya furta hakan ba idanun sa lokaci d'aya sun canja kala zuwa jajaye haka fuskar sa ma tayi ja jikin sa har rawa yake yi.

"Asad!, Asad me ya faru!?" Ta fad'a tana kallon sa ganin lokaci guda ya canja. Idanun sa da taga ya kulle yana sauke numfashi hannun ta na rawa ta kira number Mama tana d'auka tace, "Mama Asad zai mutu! Kizo Mama" ta fad'a da k'arfi tana kallon Asad da yake jingine a kan kujera kamar baya numfashi..

Continue Reading

You'll Also Like

KASHI By stuckinatale

General Fiction

400K 20K 42
"So, Mrs. Kashi Abhay Pratap Singh..chalte hai. Goodbye..". Saying this, he left her broken in this world of betrayal. ~~~~~~~~~~ Kashi, a simple gir...
372K 22.9K 38
Let's see how different personalities mends with each other to form a beautifull bond together. Where the Eldest is calm and cold, Second is aggress...
604K 27.6K 42
Needs editing [ the destiny series #1] 𝑻𝒉𝒆 𝒇𝒂𝒕𝒆 𝒑𝒖𝒔𝒉𝒆𝒅 𝒕𝒉𝒆𝒎 𝒂𝒑𝒂𝒓𝒕 𝒃𝒖𝒕 𝒅𝒆𝒔𝒕𝒊𝒏𝒚 𝒂𝒈𝒂𝒊𝒏 𝒑𝒖𝒍𝒍𝒆𝒅 𝒕𝒉𝒆𝒎 𝒕𝒐𝒈...
10.7K 549 20
Labari ne dake dauke da darussa kala kala na rayuwa, Mai dauke da tausayi, Al'ajabi ga kuma kauna agefe d'aya.. shin wacece UMMI_A'ISHA?