KALLABI..! A tsakanin Rawuna...

By Mai_Dambu

37.7K 9.5K 1.7K

The gap between Love and Hate is not the same as the gap between Death and Life ... But to be killed or to wi... More

Hello's my Fanmily
BABI NA DAYA
BABI NA BIYU
BABI NA UKU
BABI NA HUDU
BABI NA BIYAR
BABI NA SHIDA
BABI NA BAKWAI
BABI NA TAKWAS
BABI NA TARA
BABI NA GOMA
BABI NA SHA ƊAYA
BABI NA SHA BIYU
BABI NA SHA UKU
BABI NA SHA HUDU
BABI NA SHA BIYAR
BABI NA SHA SHIDA
BABI NA SHA BAKWAI
BABI NA SHA TAKWAS
BABI NA SHA TARA
BABI NA ASHIRIN CIF
BABI NA ASHIRIN DA DAYA
BABI NA ASHIRIN DA BIYU
BABI NA ASHIRIN DA UKU
BABI NA ASHIRIN DA HUDU
BABI NA ASHIRIN DA BIYAR
BABI NA ASHIRIN DA SHIDA
BABI NA ASHIRIN DA BAKWAI
BABI NA ASHIRIN DA TAKWAS
BABI NA ASHIRIN DA TARA
BABI NA TALATIN CIF
BABI NA TALATIN DA DAYA
BABI NA TALATIN DA BIYU
BABI NA TALATIN DA UKU
BABI NA TALATIN DA HUƊU
BABI NA TALATIN DA BIYAR
BABI NA TALATIN DA SHIDA
BABI NA TALATIN DA BAKWAI
BABI NA TALATIN DA TAKWAS
BABI NA TALATIN DA TARA
BABI NA ARBA'IN CIF
BABI ARBA'IN DA DAYA
BABI NA ARBA'IN DA BIYU
BABI NA ARBA'IN DA UKU
BABI NA ARBA'IN DA HUƊU
BABI NA ARBA'IN DA BIYAR
BABI NA ARBA'IN DA SHIDA
BABI NA ARBA'IN DA TAKWAS
BABI NA ARBA'IN DA BAKWAI
BABI NA ARBA'IN DA TARA
BABI NA HAMSIN CIF
BABI NA HAMSIN DA DAYA
BABI NA HAMSIN DA BIYU
BABI NA HAMSIN DA UKU
BABI NA HAMSIN DA HUƊU
BABI NA HAMSIN DA SHIDA
BABI NA HAMSIN DA BAKWAI
BABI NA HAMSIN DA TAKWAS
BABI NA HAMSIN DA TARA
BABI NA SITTIN CIF
BABI NA SITTIN DA DAYA
BABI NA SITTIN DA BIYU
BABI NA SITTIN DA UKU
BABI NA SITTIN DA HUƊU
BABI NA SITTIN DA BIYAR
BABI NA SITTIN DA SHIDA
BABI NA SITTIN DA BAKWAI
BABI NA SITTIN DA TAKWAS
BABI NA SITTIN DA TARA
BABI NA SABA'IN CIF
BABI NA SABA'IN DA DAYA
BABI NA SABA'IN DA BIYU
BABI NA SABA'IN DA UKU
BABI NA SABA'IN DA HUDU
BABI NA SABA'IN DA BIYAR
BABI NA SABA'IN DA SHIDA
BABI NA SABA'IN DA BAKWAI

BABI NA HAMSIN DA BIYAR

380 128 25
By Mai_Dambu

BABI NA HAMSIN DA BIYAR

Wani irin zaburar dokin yayi, tare da kaiwa Gidado cafka ya sha gaban shi.
"Insha Allah zan nima maka, amma da sharadin zaka kula Fulani Bintu domin ta cancanci zama wata alkaryar agefen ka"

Dariya yayi ya kara a guje, yana me kallon Lamido har suka bar masarautar, sai da ya raka shi wajen gari lokacin an fara sallah asuba suka tsaya suka yi,sannan yana kallon Lamido ya bar kasar borno,cike da kewar juna. A hankali ya juya baya, yana jin kamar ya bi dan uwan shi.

Shi kuwa Lamido ko juyawa bai yi ba, domin yana jin yadda dan uwan shi yake kallon shi yasan kewar shi yake ji, dan haka yaki juyawa shima ai kewar Gidadon yake ji.
Haka yayi ta tafiya sallah da cin abinci yake tsayar d shi, sai da yayi tafiyar wuni guda. Kafin ya yada zango ya kwanta.
**
Wannan abin da ya faru sai da yasa Anum ciwo sosai, domin ko magana bata yi, muryan ta ya dishe ainun bata ko iya wani motsin kirki jikin ta kamar an kareraye ta, idan ka ganta akwance kamar danyen nama, ga masifar Inono, ga fitinar matan gidan su.
A hankali tayi ta ja da ciki domin yunwa take ji, tura kofar karanta tayi ta hango Dadah tana ta kokarin sauke dafaffen madara, sako kai tayi tana kallon ta. Hawaye na zuba daga idanun ta, yunwa take ji kamar tayi ihu, amma ba a jin me zata ce. Dan haka ta daura kanta a dokin kofar, tana kuka a hankali, wani irin Haushin Mamanta take ji akan me bazata tafi da ita ba, ina ma take yanzun,gashi Abbanta ya rasu bata da kowa sai Allah.
Kamar ance Dadah ta juya, idanun ta ya sauka kan Anum da take kwance. Komawa daki tayi ta dauko fura ta dama sannan ta zuba zuma a kai, sannan ta zuba dafaffen madara, ta kawo mata. D'aga ta tayi sannan ta yi ta bata da bakin ƙwaryan anan ta fahimci ciwon Anum har da yunwa, dan tana bata,ta shiga sharbe zufa.
"Me yasa wannan ranar kika fita cikin dare?"
Kurawa Dadah idanu tayi sannan ta ce mata.
"Nima Gwaggo Bingel ce ta saka aka tafi da ni" sanin halin Anum bata yarda da kowa ba, balle har tayi magama da kai, sannan yarinya ce da tun tafiyar Mahaifiyarta duk abin da zata fada gaskiya ne, bawai ta yarda anum ba zata mata karya bane, amma bata san lokacin da zuciyar ta ya amince da abin da Anum din ta fada mata ba.
"Kiyi hakuri kin ji, haka Allah ya halicci wasu da son zuciya, nasan Barkindo baya cikin masu irin wannan yanayin don Allah ki kaunace shi"
Hawaye ne ya zubo mata, ta kauda kan ta sannan ta ce mata.
"Daadah ina niman wanda zai kare rayuwa ta ne ba wanda ni zan bashi rayuwa ta ba, Daadah hawai na rena tayin bane Wallahi sam bai min ba, ina son shi amma ba zumunci, ban da son soyayya da za a gina rayuwar aure akan su ba."
Cike da mamaki take kallon Anum gashi dai gaskiya ta gaya mata, amma ya zata yi da Bingel da ta matsa lallai ta nima mata yardan Anum.
"Baki ganin shi din sarki ne gaba" goge bakin ta tayi tana kallon Daadah sannan ta tattaro hankalin ta baki daya ta Zubawa Daadah.
"Daadah shi mulki jarumi ake nima, wanda zai gyaran murya jikin kowa ya dauki rawa ba Lusari ba wanda da shi da babu ɗaya ne"
Murmushi Daadah tayi tana faɗin.
"Mulkin baya gabanin kenan?"
"Eh Daadah" ta fada lokacin da ta hada karfi da karfe ta mike, ta fita waje.
"Toh yar iska kin samu lafiya daga yau ba zaki kuma fita domin aikin wasu ba, su shanun da Ubanki ya bar Miki mune zamu miki kiwon su?" Tura baki tayi tana faɗin.
"Idan aka ce na tafi da su kiwo ai ba zan ki tafiya da su ba, da sai an hada da Ubana da yake kabarin shi bai ji ba bai gani ba, Insha Allah yau babu me shan ruwa cikin salama" ta fada kasa kasa,tana nufar waje bayan ta dauki tulun diban ruwa, tun da tafiya ta tafi bakin rafi ta zauna tana kallon ruwa, a hankali ruwan ya shiga rinewa zuwa jajjur kamar ruwan jini, ita kanta idanun ta wani irin rinewa yayi kamar yana ci da wuta, Murmushin keta tayi tana faɗin babu me shan ruwa cikin salama sai kun ji a jikin ku.
Sannan ta dauki tulunta ta tafi bakin rafin ta shuri ruwan, aikuwa inda yake ya sauya zuwa ruwa me kyau da ɗaukar ido, diba tayi da saka akan.
"Naga wanda zai sha ruwan nan"
Haka kawai take jin yin mugunta, tana tafiya aka yi dace wasu tsuntsaye suna ihun su na alamar a firgice suke, d'ago kai tayi ta Kalle su, murmushi tayi aikuwa suka fado suna me ci da wuta.
Tsabar masifar da take ji a ranar duk in da ta saka kafarta, wuta ne yake kama wurin yayi bakikkirin.
(Wannan shine yanayin da Baffa'm yayi kokarin hana Aminatun shiga idan har ta kai yanayin haka amadadin alkhairi a ranta amfani da baiwar ta zata yi tayi tana cutar da mutane, a binciken da aka yi wani cibiyar nazarin ilmin dan Adam, sun gano kowani dan Adam yana da Super natural,shine ake kiran shi da Kambun baka, kuma kowa yana da wannan baiwar sai dai wasu kalilin ne nasu yake fitowa, wasu kuma idan ya bayyana iyayen su na maza a boye musu dan kar ya zama tashin hankali a gare su da Al'umma)

Wannan yanayin ba karamin dadi ya mata ba, domin bayan ta bar rafin kafin kace kwabo al'amari ya karade ko ina hatta rijiyiyyon da suke kewayen, tsuntsaye kuwa tuni suka yi cida wuta.
Abin da ya d'aga hankalin mutane kenan suka shiga niman agaji domin dai basu ba shan ruwa, ruwan da ta dauka gidan su Baffa'm ta kai tagaishe da Sarkin Gida wanda taki yarda su hada idanun su. Shima kamar wanda yake tsoronta yaki d'ago kai ya kalle ta.

Tana barin kofar gidan ya D'aga yana bin sawun ta da ido, da sauri ya shiga cikin gidan. Ya kira Baffa'm da Galadima.
Kallon wurin suka yi.
"Wayyo Allah na" inji Galadima.
"Ta zarce Aminatu ko?"
"Kowani lokaci zata iya daukar yanayi akan kowa" baffa'm ya tambaye shi a tsorace, domin shima ya gama razana da yanayin Anum, dan haka suka bi bayan ta.
Sanin babu wanda ya gane me take ciki tana shiga cikin gidan takada shanun ta suka bar gidan baki daya, har yankin ta bari, ba tare da ta juya ba, kawai tafiya take da shanu, ta kai ko mugan namun daji suka haɗu da ita sai dai suyi ta gudun ta. Yanayin ta ta'azzara da ko wucewa tsuntsun yayi akan dabobbin ta,ta Kalle shi faduwa yake a mace.

A can kuwa hankalin mutane ya tashi ga ruwa ya lalace dan haka masu maganin dan masu duba,bokaye da yan bori. Suka tawo aka saka ruwan a gaba da bincike, Galadima da Baffa'm sai dare suka samu damar zuwa ganin ruwan,bayan sun gama abinda ya kawo sune suka dawo gida, a hankali Galadima ya sauke ajiyar zuciya.
"Sarkin gida me yan borin suka fada?"
"Sunce tsinuwa ce da alwashi"
"Sun mata wani abu kenan da har ta yi alwashin"
Girgiza kai yayi, sannan suka ce.
"Babu ita babu alamar ta fa a wannan yankin?"
Kasa magana suka yi suna nazarin ta ina zasu dakatar da ita.
**
"Boka ka duba al'amarin yarinyar nan ta bayyana yanzun haka ta gabar din mu sun mata laifi ta musu alwashin ruwan su ya koma na jini" bincike yayi sosai sannan ya ce mishi.
"Sai dai ka nimawa Danka auren ta ba dai kai ba, a yanzu haka tana gab da samun me iya dakatar da ita. Domin ƙaddara ta ja ta izuwa takin da mutuwa ce xata iya shiga tsakanin rikicinda ya kono kai"

"Ban gane ba?" Ya kuma tambaya,
"Ina tabbatar maka ba zaka iya ba, ba zaka iya dakatar da ita ba, Danka da yake sonta bazai iya ba sai dai idan zaku aura mishi ita bata sani ba, shima ba wai karfi zata kara mishi ba,idan yayi wasa mutuwa zai yi domin yanayin ƙaddara ba zai barta haka."
Kamar wanda aka watsa mishi ruwa haka ya mike, ya bar bokan cikin nashi binciken.
--
Tsawon kwanaki uku,tafiya yake ba dare ba rana, fuskar ta yayi fayau kamar wacce ta rasa jini a jikin ta, kawai kada shanun take, gajiya tayi da tafiyar ya samu wani kasar bishiyar, domin yanayin ta ta fara dawowa daidai, shi yasa taji gajiya zama yayi a kasar bishiyar wata tsohuwar tsamiya, ta lumshe idanun ta, wani irin gud'a aka rangad'a daga jikin bishiyar tsamiyar, gyara kwanciyar ta tayi tana me jin kamar an lullube ta d bargo. A hankali ta kwanta barci yayi gaba da ita.

Kallon rana yayi yaga yayi zafi burin shi ya samu wani wurin ya tsaya yayi sallah sannan ya cigaba tafiya. Hango shanu nata kiwo ne ya sa shi tunanin ai ya kusan gari, daga cikin yake hango wani katon mesa yana nad'e bishiyar da take kwance a jikin shi, kafin ya kuma sauka yana Niman hanyar da zai hàdiye ya baki daya, domin ya kwana biyu bai hàdiye dan adam ba, shi yasa da yazo wucewa ya hango ta kwance yaji ya samu kalacen shi na kwana da kwanaki kafin ta rube ya yarda kanta. Sai zaro harshe yake yana zagaye ya, amma zafin wutar da ke fita a jikin ta yasa shi kasa mata kome, sauka a dokin Lamido yayi ya zaro takobin shi, yana zuwa a hankali yadda mesa ba zai fusata ba.

Aikuwa yana isa ya samu dan bakin Naci ya fara na hàdiye kafarta zuwa gwiwar ta,. Dake mesan shima zalamamme ne da sauri ya zaro bakin shi daga kafarta ya nufi Lamido, a fusace shima cikin fushi da yi kan shi tare da sare kan shi da ya bude mishi. Aikuwa jinin ya ce watsu a fuskartar, abin ya firgitatta kenan ya fasa wata irin kara da ya haifar da kamawar bushiyar twamiyar nan, kafin ta kuma kara ihun ya maza ya toshe bakin ta, tare da fitar da ita kasar bishiyar tsamiyar, ya matse bakin ta da karfin tsiya wani irin tururi da zafi yake ratsa hannun shi, ta shiga kokarin kwace kanta, amma haka yayi nasarar matseta a jikin shi. Sai da ya tabbatar ta suma yanayin jikin ta da yake da zafi ya koma yayi sanyi, kamar wata matacciya, sauke ta yayi ya kwantar da ita sannan ya shiga kafa tanti a wurin ya gyara cikin ya saka ta, kafin ya cigaba da tattara mata shanun ta, kallon tafin hannun shi yayi yaga yayi jajjur. Kallon tantin yayi,
Sannan ya shiga niman tattara kome, ha kuma tsinko magani ya zo yayi ta dakawa da wani irin dutse ya matse ruwan a tafin hannun shi. Lumshe idanun shi yayi yana jin zafin na ratsa shi, sai da ya gama sannan yayi Sallah yana idarwa ya fita farauta. Haka ya samo fakara guda uku wato kajin daji, ya kawo ya gasa, sannan ya ciro bushashen naman da Innayoh ta hado mishi ya koma gefe ya ci sosai, har dare bata farka ba, dan haka ya cigaba da hada wuta yana karatun Alqur'ani.
Anan ya raba dare bai kuskura ya shiga dakin ba, wuraren asuba ya ɗan ajiye Kur'anin ya kwanta yana me lumshe idanun shi. Ai kuwa barci yayi gaba da shi.
Ruwa ne gaba da bayan ta, wanda yake cike da jini makil, kai hannu yayi zai riko ta. Amma ina tayi nisa domin ta nutse sosai, fadawa yayi shima ya hango ta kwance. Daukar ta yayi zai fito fa ita yaji ya kasa motsi daga wurin juyawa yayi zai duba yaga kafarta daure da igiya, gidado ne ya kai hannu zai amshi ta wani ya bangaje shi ya amshe ya,.shi.kuma ya kamo wanda ya dauke ta a hannun gidado bayan ya nuna mishi takobi, juyawa yayi ya zai mikawa gidado ita, aka wurge su da wani mashi... Bude idanu yayi sakamakon jin takobi a wuyar shi, Anum ne rike da takobi tana kallon shi.
"Waye kai? Kai barawo ne? Gaya min waye kai?" Buge takobin yayi daga ita har takobin suka fadi can, sake mikewa tayi, ranta a B'ace ta zata kowa kamar Barkindo yake. Kawai ta kuma tawowa kan shi da takobi tana cewa.
"Sai na kashe ka tunda ka sato Ni" juyawa yayi yana mamakin taurin kai irin nata, kafin ta matso gare shi ya samu damar tsayawa da kyau tana zuwa ya kauce mata, tare da damke keyarta ya D'aga ta cak da kasa. Kallon yadda take mutsu-mutsu yasa shi sake ta, aikuwa ta fadi a kan hannun ta.
"Kasssss" kashin hannun ya bada sauti. Wanda yayi sanadin sumarta.
Sai da yayi Sallah sannan ya koma wurin dokin shi ya dauko kayan aiki ya zo ya kama hannun ya rike addu'oi yayi sannan ya tofa a hannun ya daure mata shi. Sannan ya watsa mata ruwa, ba wai ayayyafa ba, a'a Juye mata yayi a firgice ta bude idanun ta sai lokacin ta ji idanun ta ya cika da kwalla ta ce mishi.
"Kai Azzalumi ne mugu mara imani, Allah sai ya saka min". Ta fada tana matsar kwalla, sunkuyawa yayi zai dauki kayan aikin shi a tunanin ta wani abu zai mata, aikuwa ta fashe da kuka, tana kame kirjin ta. Tabe baki yayi sannan ya dauki abinda zai dauka har tana jin kamshin turaren shi.
"Mugu" ta fada kasa kasa, nan ya juya baya kallon ta,.kafin ya mike abin shi bai kuma bin kanta ba.
"Hala bayan jin ne shima Mugu barawo me kama da yan fashi"
Ita a tunanin ta satotta yayi shi yasa ta rufe idanun ta,.tayi ta gaya mishi.magana abun haushi ko cikanki bai ce mata ba, har ya gama abinda zai yi gari na wayewa ta wuce ta dauki sauran ruwan shi tayi alola, sannan ta gabatar da sallah,.tan idarwa taga ya haɗa wuta yana dumama namar shi, hàdiye yawu tayi.tana kallon shi. Yana halkance da ita amma ko ta kanta bai bi ba, da gayya ya saka namar nan a gaba ya cinye,.aikuwa ya sha bambami.
"Allah ya isa min hàdiye yawun da nayi Mugu me kama da bishiyar kuka,.ka karya min hannu sannan ka cinye kazar jinyata, Allah sai ja gani a ƙwaryan cin tuwon ka, zaka sha mamaki. Idan ba tsoron ba ka bude fuskar ka mana! Yaji tsoron a bashi ruwan madaci ya sha, ragon maza Lusari" wani kallo ya watsa mata, tayi maza ta rufe bakin ta, tana hàdiye yawun tsoro, kafin ta fara kwalkwal da idanu.
"Idan na rashin imani ba, taya zaka cinye abu kaɗai baka ce min bismillah ba, ai ko na maida mugun yawu, Yanzun idan ka mutu wuta za a saka ka...." Wani irin fisgota yayi tare da zare takobin shi ya mai da ita jikin shi yana me buge kifiyar da aka dannota da shi, a hankali mayafin da yake kare a fuskar shi ta warware,aka kuma wurgo musu wani wanda ya dauke rawanin shi da hular baki daya. Tana jikinshi ya sakala hannun shi akan cikin ta, yayi ta kabe harin har sai da mutanen suka gaji dan kan su, suka bayyana sanye da bakaken kaya,juyo da ita yayi da tayi mutuwar tsaye, ya ce mata.
"Rufe idanun ki, ki rike ni sosai"
Kallon shi take sai da ya kuma.daka mata tsawa ta rungume shi tare da boye fuskarta a jikin shi kafin ya samu damar daure ta da rawanin shi ya tam, sannan ya shiga wani irin yakin kota kwana da mutanen da bai san Meye hujjar kawo musu hari ba....
🚶🏾‍♀️🚶🏾‍♀️🚶🏾‍♀️
*Let me waka kai da kazo ganin tsohon ka kaine da shiga yaki na gaya mishi gaskiya ne ko na bari Gobirawa su gaya mishi... Yau na hada muku na yau baki daya domin ba zan yi na dare ba kar ma ku saka rai 👋🔥😍*
#Mai_Dambu

Continue Reading

You'll Also Like

170K 4.7K 197
The Gluttonous house's auction feast had an exceptionally good furnace in constitution of a little girl with sky-high price, everyone in looting. Su...
10.1M 761K 88
Marriage had always been my dream but not to a man about whom I know nothing. The moment my father fixed an alliance of me to a Prince without even t...
JUNOON || جنون By Ira

Historical Fiction

20K 1K 25
An arranged marriage between two contrasting yet similar people. Will it work? Urwa Shah A nineteen year old girl filled with dreams. A strict father...
6M 391K 74
Losing this war means captured by the enemy empire and considered as their prostitutes and servants. Dreaming that situation made my heart race even...