IZZAR SO 9

673 15 3
                                    

9

_🌹IZZAR SO Littafina na kuɗine kada kiyi tunanin zaki siyi Littafin nan domin ki watsawa media🙏🏻ga dukkan wanda zai siya 200 kacal katin mtn zaki ɗauki picture nasa ki turo ta wasapp no 08119237616🤟🏻kota Btu accout no 0116886423 Na'ima sulaiman s,unioun bank,idan zaki haɗa da ducoment ɗin SAI NA AURETA zaki biya 300 kawai domin samun duka book ɗin guda biyu🥰_

Shuru yayi mata ba tare daya ce komai ba, tashi tayi a hankali ta fata tafiya zuwa inda yake kwance,zama tayi kosa tashi tare da sauke numfashi mai zafi tace.

  "Babu shakka ni nasan bana da gata kuma akwai ƙaddara a cikin rayuwata,bana da wani wajen jin daɗi face wajanka,nasan akwai wani abu mafi muni a rayuwata tunda mahaifina da kansa yasu yimin fyaɗe,a koda yaushe idan na tambayi zuciyata wanda ya dace da ita,sunanka take kira"

      Lumshe idonsa yayi ya najin ya heartbeat ɗinsa na,ƙaruwa mai yasa ba zata fahimci baya sonta,ta riƙa data zubar da ƙimarta akan idonsa,bai taɓa sonta ba haka kuma bazai auri wacce baya soba,yasan daman wata rana dole ne ta duƙawa izzarsa domin yasan meye wekness nata,ware idonsa yayi sannan ya tashi zaune kusa da ita har numfashinsu na haɗuwa waje guda,kanta ta sunkuyar ƙasa,ɗan murmushin taƙaici yayi sannan yasa lallausan hannunsa ya riƙe habatar sannan ya juyo da face ɗinta zuwa wajansa,cikin idonta yake kallo yayinda itama take kallon nasa zuciyarta na ƙara bugu da sauri,ɗan motsa lips ɗinsa yayi yace.

     "sunana zuciyarki ke kira?to meye sunan nawa THE POOR MAN ko?idan hakane zuciyarki kam tayi maki ƙarya"

    Yana kaiwa nan ya tashi ya shige ciki abinsa hankali kwance,bayansa tabi da kallo yayinda hawaye kebin kuncinta,hannu tasa ta dafe saitin zuciyarta inda yake mata zafi,ɗan lumshe ido tayi tana tunanin mahaifinta mafi soyuwa a gareta.

     ****Makka***
Dukkan wani bin cike daya kamata ayiwa YARIMA anyi masa amma babu wani cigaba,yayinda duk wani result na binciken da akai masa yake nuna lafiyarsa ƙalau,sosai hankalin TAKAWA ya tashi ganin tilon ɗansa na shirin rasa ransa,dan haka ya yanke shawarar daga nan zasu huce EXGPHAT domin yi masa binciken gaggawa,wani Dr ne ya nemi da sukeɓe da TAKAWA.

   Dr ne ya kalleshi sannan ya cire glass ɗin face ɗinsa yace.

  "am sorry to say ranka ya daɗe,duk inda zaku kai YARIMA ba za'a samu yadda ake suba,tuna nina yaban wannan aikin MAGIC ne domin munsha karɓar problmes irin wannan,a shawarce gwara a koma gida a fara yi masa na hausa da kuma addu'ar karya duk wani tsafi da kuma sihiri"

  Jinjina kai TAKAWA yayi tare da faisar da numfashi mai zafin gaske,babu shakka da ace yasan wanda ya aikatamawa yaronsa haka,wallahi saiya nuna masa bashi da wayo kuma baisai ƙarfin mulki da izzar saba,kallon Dr yayi tare dayi masa murmushi alamar ya gamsu da wannan suka shirin komawa Garinsu wanda ni kaina bansan ko wanne gari suke ba.

     ***KANO****
Kano birnin damu koda me kazu anfika,yau kwanan GIMBIYA OMEHI 5cif a garin kano,wanda ta sauka wajan ONKWO (kawu)ta sosai ta samu nutsuwa a wajansa domin baya ta kurata komai takeso yana mata,yayinda ya gargaɗe ta koda wasa kada ta sake ta nuna wata ƙabila ce ita.

     Tare suke zuwa wajan aikin kawun nata,ba wani waje bane face gidan SARKIN KANO inda yake kula da dawakan SARKI yayinda ita kuma take jire masa dawakan idan zaije wani waje anan suke yini sai yamma suke tafiya gidansu.

  A kullum tana tsintar kanta da tunanin YARIMA tana ji inama zata ganshi da babu abinda zai hana tabishi domin ta fahimci shine rayuwarta shine dukkan wani farin ciki nata,gashi zuciyoyinsu sun rabu da juna,amma babu shakka bugun zuciyarsu nayi ne lokaci ɗaya.

   Wasu hawaye ne suka shiga zubuwa daga cikin idonta,sannu a hankali bugun zuciyarta ke ƙaruwa.

  Haya niya taji tana tashi a hankali tare al'gaita mai daɗi da kuma ratsa zuciya,ɗan tashi tayi ta ɗeka,a dai² lokacinne taga an turo wata kujera kamarta gurago daɓe baki tayi lokacin da akazu hucewa dashi,ƙara leƙawa tayi amma bata iya ganin kowa waye akan kujerar.

      ***KATSINA***

Kwanan su 4cif babu wanda ya ƙara ganin kowa,ita ta gujeshi ne akan soyyayarsa da taji ƙarfinta,yayinda shi kuma ya daina fitowa sabida wani zazzafan zazzaɓi daya rufesa,ko tashi baya iyawa.

    Wanka tayi ta saka wata duguwar abaya mai bin jiki,cikin sauri ta fito da niyar zuwa ɗakin da yake domin ta gaji da zama babu shi,tana shirin barin ɗakin nata taji wata iska na kaɗawa a ɗakin nata mai karfi kafin taji wata kururwa da ihu na karaɗe cikin ɗakin nata.

   Wajan 10min iskar ta ɗauke idonta ta buɗe a hankali a razane tayi baya tare da dafe ƙirjinta ganin mahaifinta SARKI KHALEFA a gusa da ita,cikin takun isa da gadara yayin kanta gadan²,yana zuwa yasa hannu ya fisgota ta faɗa saman bed ɗin kafin..

     200 naira kacal,domin jin yadda zata kaya tsakanin UBA DA ƳARSA,SHIN SARKK KHALEFA KOWA ZAI SAMU CIKAR MURADIN RANSA?amsar sai kun biyoni zaku jita.

        Wattpad pls Comments and vote

IZZAR SOWhere stories live. Discover now