Kasa karasawa tai ta fashe da kuka wanda gaba dayansu jikinsu ya fara rawa, Nafeesat ko jikin ta nai ya fara rawa dan ko bata karasa ba tasan mai takardar ta kunsa cikin kidima ta ce .

"Mama ki sanar dani saki nawa yai mun dan Allah Mama ki sanar dani? innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un! tabbas na san Mama Arfan ya rabu dani bai tsaya a abun da yai mun ba nida kanwata daku iyayena sai ya sakeni.

Ya barni na mutu cikin sittira mana, ya bar ni na mutu da hijabin aure mana, amma ya gaza yimun wannan alafarmar" sai kuma ta shide gaba daya ta fita daga hayyacinta abun da ya daga hankalinsu ke nan.

Cikin kidima aka kirawo likita nan da nan aka shi ga da ita emergency dan dubata, ina haihuwa tazo gadan gadan nan da nan aka ce sai dai ai mata cs bazata iya haihuwa da kan ta ba gaba daya kuka suke dukansu.

Abba kuka yake kamar ransa zai fita yayi nadama mara amfani ta yadda ya fifita kudi akan yaransa, ga shi yanzu abun da san kudin nasa ya haifar masa shi ya sa hannu aka shi ga da ita, anyi nasarar ciro mata diyarta mace mai kama da ita sak amma karama ce dole sai an sata a kwalba.

Amma kuma Allah yai ikonsa akan mahaifiyar inda kafin ma agama ta cika, tashin hankali wanda ba'a sa masa rana wannan ahali suka tsinci kansu a ciki.

Inda Abba ya yanke jiki ya fadi Mama tayi tawakalli hawaye kawai ta ke ita ta koma tana rarrashin Umma, ta ke ta kira Daddy ta sanar masa da abun da ke faruwa a gigice ya sanarwa Momy suka taho asibitin kota kan Arfan basu bi ba.

Suna shi ga asibitin suka kara rikicewa ganin ta akwance sambal kamar kai mata magana ta amsa, Daddy nai ya tsaya yai duk wasu cike cike da suka da ce aka basu gawar saboda ta dade tana jinya a asibitin ya bukaci su wuce da ita gidanta ai mata suttura a can.

Mama ce cikin fushi ta ce "me zata koma tayi a gidan wanda bai san kara ba ko yakanah, wallahi dan ku yayi asara bata da hurumi da wannan gidan tun da ya aiko mata da takaddarta saki uku rigis, wanda yai sanadiyyar rasa rayuwarta ai ya huta ko kuma mun bar shi da Allah."

Jikin Daddy har rawa ya ke saboda tashin hankali "haba Hajiya wasa kike Arfan din da duka yaushe ya fito daga asibitin yana gida ma fa shi ba lafiya" murmushi kawai tai ta mika masa takardar ya karanta fashewa yai da kuka duk dakiya irin ta namiji.

Ya din ga kuka duk sai da jikinsu yai sanyi "tabbas ka haifi da baka haifi halinsa ba, amma dan Allah kuyi mun alfarma idan har mun zama daya a sallaceta a gidana" Umma ce ta ce ba komai su tafi.

Yana kwance a daki yana ta tunani anya ko yaiwa Nafeesat adalci bai kamata ba sam abun da ya aikata, dan yana san kanwarta bai kamata ya rabu da ita ba tun da tana masa tsananin biyayya, bai mata adalci ba tabbas kafin dan aiken ya risketa gwara ya janye dan tabbas yana san Nafeesat amma Maryam fa?

Nata mai sauki nai gwara su rabu da Nafeesat cikin salama, yadda zai Dora mata lefi yadda iyayensu bazasi jayayya wajen bashi auren Maryam ba, da wannan shawarar ya samu karfin gwiywar mikewa ya fice.

Haka ya mike yana layi ya nufi gate ya tarar driver ya dawo ya ke tambayarsa yaya ya kai ya ce eh, cikin tashin hankali ya koma dakin sai kuma yaji fitar su Daddy, yana nan kwance yana karanta wasikar jaki ya kira Maryam missed call bakwai yai mata sannan ta daga.

Fashewa tai da kuka "Arfan ka cuceni ka gama da rayuwata ciki wata biyar na shege ni Maryam? Wallahi ka gama zaluntata saboda wannan abun yar uwata ta ke halin mutuwa da rayuwa, tun ranar data samu labari bata kuma rayuwa mai dadi ba a duniya.

Zabura yai kina nufin dama ba rainon ciki Nafeesat ke ba lalura ce tasa har yanzu bata dawo ba, kina nufin kice ciki ne da ke? alhamdulillah! naji dadi amma zan je duba Nafeesat, nasan kodan cikin jikin ki zan mallake ki cikin ruwan sanyi" "bansani ba munafiki kana nufin bama kasan halin da iyalinka ke ciki ba ke nan, to karka kuma nai ma na dan ni yanzu uwace a gareka dan mahaifinka zan aura" tana kuka ta kashe wayar.

DAN ISKAN NAMIJIWhere stories live. Discover now