KUN MAKARO PAGE 28

717 42 0
                                    

💅🏼  *KUN MAKARO*  💅🏼






*BY HAERMEEBRAERH*






Page 28:





"Da uban wa kk waya har kk cewa 'yata 'yar shi?"

"Ban gane kana tambayata da wa nake waya ba, ina ruwan ka dani? Ohhhh sorry na manta ashe fa kai yayana ne, ina magana ne da Yah Sabeer, kuma uban Ameerah ne tinda ko kaqi ko kaso qanin ka ne shi,"

"Me ye a tsakanin ku da kk kashe murya kk magana kamar kina magana da mijin ki?"

"Inshaa Allahu mijina ne, Allah ya amsa maganar ka, kana da matsala akan hakan?"

"Baki da hankali ne?  Da yarinyar tawa zaki wani auren? Kuma ma Sabeer a dik mutane?"

"Yarinyar ka auren ka ne akai na? Sabeer akan dik mutane ai gwanda shi akan ka ma ba mutane ba, kaga ba zan iya sa'in sa da kai ba a mutane, yanzu bakina ya bude, zan iya kwana kana fada ina fada, amma ba mutunci na bane, saboda haka in kana da magana ka zo gida bayan mun dawo daga shooopinggggg,"

Juyawa tai ta shige dakin da aka kwantar da Hadiza, zuciyar ta wasai ko haushin shi datake ji da babu, dan ta samu ta fidda abinda ke qulle a zuciyar ta ta, ya isa haka, haba, mutum kamar wani shaidan.

Sallama ta musu Hajja ta mata fatan alkhairi, ta ce ta gaida mata su Ameenaa, ita kuma ta bada saqon gaisuwa zuwa Baba General, ta wuce, Khaleefa na ganin fitar ta, yace shima gida zashi, su kai shi ha dakko diyar shi, ba zai bar ta a hannun su ba,

"Amma dai ka san ba wai umarnin ka muke bi ba ko? Kai kk bin umarnin mu, in kana so bi umarnin ka kaje ka nemi izini wajen Hajja,"

"Comw on, yarinya ta ce fa wajen wani qato, ba zan taba yarda ta zauna wajen su ba,"

"Kaiii....zo nan,"

Bammm ta maida qofar ta rufe, kallon qofar yayi ya lumshe ido cikin bacin rai, wannan tsohuwar fa tana ban matsala.

"Meye matsalar ka da Ameerah da kuma Aeeshaa da ba saka iya barin mu koma gida ba, a asibiti zaka zo kana sai da mana halin ka kowa na karba,"

"Hajja ba ki ji wai fita zasuyi da Sabeer da Ameerah ba?"

"In na ji sai na hana su? Ba diyar su bace suma, beside kace kai baka son yarinyar nan, ga wadda kk so nan kayi cikin shi ai ba aure ko? Kuma da alama ya shiga ran ka tinda yanda ma ka dauke shi daban ne, har suna ka rada masa, so kar na sake jin maganar Aeeshaa a bakin ka balle Ameerah da Sabeer,in zaka yi maganar su inji alkhairi, yarinyar nan sai in ta girma ta ga damar kula ka amatsayin uba, ba mai bata ka a idon ta amma ba wanda zai baka ita mahaukacn banza kawai,sai kayi kamar ka samu lfy, sai ka qara bazama,"

"Hajja kina nufin banda hankali kenan,"

"Kwarai d gaske, in kana da hankali wanda yake son naka kana da kamar shi ne, Sabeer dinnan da kk gani kwanan nan na san ya dade yana son Aeeshaa a sanadin a baka ita ya hakura, ba dan haka ba da Ameeran ma tashi ce, ka mata sakin hauka saboda kan ka na hayaqi ance ka sake ta, kuma naga dai ba son ta kk ba, tinda ka fada aura maka akai ba kai kace kana so ba,"

"Ni yaushe na taba cewa ban son ta, ni ba wanda ya taba jin nace bana son ta,in ma na fada nace na janye, kawai dan ba sona ake ba shi yasa komai nayi bana daidai, dik wani abu da ba ko son nayi ba na daina ba yanzu, kum nace in son mada min mata ta da 'yata yanzu, ba shikenan b a maida ta shi ya samu wata,"

Hajja ba zata iya da wannan haukan ba, yi masa bayani ma baida amfani, saki uku a gidan uban wa aka taba maida shi?

"John ! Auwal ! Ku maida min shi gida,"

KUN MAKAROWhere stories live. Discover now