Page 8

756 45 0
                                    

💅🏼  *KUN MAKARO*  💅🏼








*BY HAERMEEBRAERH*






Page 8:





Duba shi ta shiga yi, idan ta hawaye, yau so take ya fada mata me ta mishi yake gudun ta, koba komai shi kadai ta sani ta saba da shi, shi take jin zata iya sharing komai da shi vataji nauyi ko kunya ba, bata sani ba wataqila laifi ta masa shiyasa yake gudun ta.

Qofar dakin shi taje, tai ta kwankwasawa, yana tsaye jikin qofar, a hankali ya saka key, shiru ta danyi, dan taji motsin saka key din, a zaton shi ta hakura ta tafi, da sauri ya murda ya bude, zai leqa ta, sukai gware, baya yayi, yana taba wajen, itan ma haka, wayancewa yayi da,

"Me qaton kai kawai, ji yanda kk sa na bige,"

"Yah ni da kai an ga mai qaton kai ai, Yah Sabeer me nama ne, in wani laifi na maka dan Allah ka yi hakuri ka yafe min na tuba ba zan sake ba, ba zan sake makamancin shi ba ma ko mene ne balle nayi irin shi, ka daina guduna, ka sauya wajen aiki, for only god knw why, amma zaka tafi ko sallama,ina ta bin ka ina kiran sunan ka haka ka fice baka tsaya ba,nice baka son gani ko?"

Tana maganar ne cike da zubar hawaye, kukan ta na qona masa zuciya, baya son ganin koda bacin ran ta ne balle kukan ta, yana son ya bata amsa amma me zai ce mata? Ina son ki? So nake ni na aure ki ba Khaleefa ba? Inaaa ba zai taba yuwa ba.

"Look dear, ni ba wai gudun ki nake ba, yanayin aiki ne haka, kuma ranar na san inna tsaya sai na makara ban tafi ba, in ban manta shagwabar ki ba kina qarama ko nan da can naje sai kinyi ta kuka, kina rikici, ko dake ban sani ba yanzu kin zama babba wataqila kin daina ko?"

Cikn wasa ya qarasa maganar tashi, itan ma murmushi tayi,

"Yah zauna na baka labarin abubuwan da suka faru da baka nan, kuma ina son ka ban shawara, akan Yah Khaleefa, akwai wani sirri nashi da ba na son fada, amma bana son abun, bana son mai yin abun, dan haka nake jin tsanar wannan auren namu, Yah dan Allah ka ban shawara ya zanyi?"

Gaba daya ya shagaltu da kallon ta, a dan watannin da yayi sai yaga ta qara kyau da girma, ga shi for the first time ya gan ta da kwalliya mai kyau haka, hannu tasa ta gaban idon shi,

"Yah magana nake fa,"

A dan firgice ya dauke kan shi, ya kalle ta again,

"Immm kin ga ko zamu bari nayi wanka na ci abinci, bana gane komai yanzu, muguwar yunwa nake ji, kin san ni da ci,"

🙄🙄"amma dai matar ka ta shiga uku, ko daga qafar girki na rana daya ba za ta samu ba,"

Tashi tayi ta na tafiya tana sanar da shi anjima zata dawo, su qarasa magana, ya amsa da to, ta koma wajen su Hajja, nan ta samu Hussai ta dakko kudin da Khaleefa ya wurga mata, suna ta mata dariya, wai amaryar qauye an mata kyauta ta ajiye, ango ya tafi tabiyo sahu ta dauka taga babu, tana son tai kuka, yaqe ta musu ta shuge daki.

Yanda auren nan ke qaratowa haka zuciyar ta ke tsananta bugawa, Sabeer ya tare a gidan Umma, dan bai ma sake komawa ba balle ta gan shi tace zasuyi magana, ba zai juri kallon ta ba, bai san me zai iya aikatawa ba da wanda ba zai iya aikatawa ba indai a gaban ta ne.

*********************



"My baby ina kk son tafiya ne wai? Gobe fa daurin auren ka, na sani in ka tafi ba zaka sake dawowa ba,ka bari na kwashi rabona mana plssssss"

Wani irin narkewa take a jikin shi, shi kuma yana lumshe ido,kamar wadda aka mintsina ta tashi, tambayar ta yayi

"Lfy?"

KUN MAKAROWhere stories live. Discover now