Asiya da yan kano suka fara shirin tafiya yayin da Asiya banda kuka babu abunda takeyi, haka itama Husna aka kaita part dinta da Memartaba ya tanadar musu, yayin da Zakiyyah ita Za'a dauketa a kaita gidan ta dake nan cikin garin Zamfara.

Jama'a duk an fara watsewa amma Shi Jafar ya ringa ya fada ba ranar zai tafi ba sai washe gari sabo da Jikin Dizhwar.

Sai wajan karfe 9pm tukun ko wacce aka tafi kaita, gidan shiru duk babu hayaniya duk an tafi kai amare.

Sai dangin Husna kawai a part dinsu suna shagalinsu.

________
Lailah kuwa tunda aka kaita wannan wajan aka yarda ta, bata san inda kanta yake ba cikin wannan dajin, tana kwance har zuwa lokacin kamar gawa ko ba numfashi balle Motsi.

Gaba daya jikinta ya kumbura, gashin kanta duk ya hargitse ga uwar dauda da tayi, duk tayi baki in baka sanda ba da yanzu bazakace ita bace.

_________

Bayan an kai Amare, dare Yayi wajan 11pm, har lokacin Dizhwar yana daki a kwance, babu zazzabin yanzu a jikinsa, illah Kasalar jikinsa.

Yana kwance akan sofa, shida Jafar, Anty Amarya ta turo kofar dakin nasa.

Da sallama ta shigo, wata tana biye da bayan ta, sata tayi ta ajje babban tray din daya cika da flasks akansa, ajje shi tasa ayi sannan wacan din ta fita.

Itama zama tayi tare da fadin,
_"Sunna da jiki Dizhwar "_

_"Ywwah"_
ya fada Jafar yana gefansa.

_"Katashi ka dan daure kaci dan farfesun dana sa ayi maka saikasha magani ko kaji kwarin jikinka"_
  Ta fada tana kallansa.

Shiru yayi dan baya bukatar komai, amma jin abunda ta fada yasa ya fara Sha'awarci jin ace Farfesune.
  Amma sai yayi shiru be mata magana bah.

Jin haka yasa tayi murmushi tunda taji yayi shiru tasan zaici,
Dan haka mikewa tayi tare da kallan Jafar,
_"Pls Jafar kasa yaci ko kadanne, Allah ya sauwake"_
Ta fada tare da fita.

Jafar binta yayi da kallo danshi sam!, be yarda da ita bah.

Tana fita Dizhwar din ya mike zaune tare da fadin,
_"Jafar dan zubomin inci dama ina san cin Abu medan yaji yaji"_

Anty Amarya dataki kulle kofa sosai dama dan taji abunda Za'a fada, murna ta kama dan ta saka maganin mallaka aciki, burinta Dizhwar yaci, yana ci kuwa ya dawo a tafin hannunta dan sai abunda tace masa shi zaiyi.

Banza Jafar din yayi dashi, ganin haka yasa ya mike da kansa ya nufi abincin.

Hannu yasa ya bude flask din.

Wani irin kamshine ya daki gancinsa, hannu yasa zai Tun aciki ya fara ci dan baze iya jiran ayi serving dinsa bah.

Turo kofar da Husna tayi yasa yayi saurin dauke hannunsa daga kai tare da mikewa tsaye.

Binshi tayi da kallo, tare da kallan Jafar.

Ganin kallan da takema Dizhwar din yasa, Jafar mikewa yabar wajan.

Da sauri ta karaso tare da rungumeshi, suka koma kan kujera suka xauna.

_"Hubby yaya jikin naka? "_
Shiru yayi mata yana kallan tah.

_"Baka kaunar matar kane, zaka zo na ka zauna bayan kasan wanna shine ranar mu ta farko ranar da ya kasance mu nunawa juna farin ciki da kuma sun da mukewa junan mu, amma shine zaka ki zuwa kayi zaman ka anan?"_
  Bece mata komai ba, illah kallanta da yake yi.

_"Kidan zubomin wacan abun, inaso inci yinwa nake ji"_
Daga shi tayi tare da nufar flask din,  tana budewa taji kamshin maganin, kasancewar suma masu harkanne yasa tayi saurin ganewa.

Da sauri ta kalle shi tare da fadin,
_"Wanene ya kawo wanna abun? "_

_"Ki Zuba min magana ina ruwanki da wanda ya kawo ki kawo Min mana"_

_"Toh wallahi in baka fada min ko waye ya kawo maka ba, bazaka cishi bah"_

Shiru yayi mata yana kallan ta.

Daukar tray din tayi tayi hanyar fita dashi.

_"Husna ki maidomin mana meyasa baki da hankali ne"_

Bata kulashi ba sabo da ita tasan abunda ta gani Ta fita,

Binta yayi da sauri suka fita wajan 12am, tana tafiya yana binta a baya.

Anty Amarya dake kusa dasu, tana jiran DIZWARH ya gama ci ta kirashi, dan yau tana bukatar shi, ganin Husan ta shiga yasa gabanta ya fara faduwa dan tasan wannan jarabarbar bazata barshi ya ci abincibah.

Kamar kuwa ta sani ta hangota da flask din tana faman sauri, shikuma yana binta a baya.

Da sauri ta mike, da kamar bazata fita ba, sai kuma ta tuna irin kudin data kashe kan maganin da kuma tana da hadama gaba daya ta juye.

Da sauri ta fita tare da tarar Husnar, a tunaninta bata san komai bah.

_"Ke Husna meye haka baki da hankaline wai ke"_
Ta fada tare da karasowa wajan.

Dizhwar kuwa bata masa rai tayi, tsaki yayi ya kOma dan baxai iya jurewa binta haka bah.

Gabanta ta tsaya suna kallan juna.

_"Meyasa kike irin wannan, kefa bakuwa ce, nikuma uwar shice, zai iya sakinki kibar gidan nan, nikuma ina nan daram!, akan me nayi masa kirki zaki hana yaci, kuma ma sabo da baki da hankali da tarbiya kika biyo miji sai kace ba mace bah"_
Anty Amarya ta fada ranta a bace.

Tsayiwa Husna ta gyara tare da fadin,
_"Ashe ke babar shice, kina da sanin cewar yau in ubansa ya sakeki baza kibar gidan bah, har zakizo kina min wannan maganar, ko a tunaninki kece surukata, toni ko ita wanda ta haifeshin bata isa ta shiga tsakanina da mijina ba in rabu dashi, balle ke, ko an gaya miki bansan abunda kika zuba acikin abin cin bah, ninan da kika ganina karshece, a cikin tafin hannu na kike,da naga dama Sarkin zan aura gaba daya, amman ni Dizhwar nake so, ke bara ma kiji in gaya miki, tunda har muka kawar da mahaifinmu, toh duk wani dan iska ya kuka ga kashi sabo da haka"_
Tana fadar haka ta saki flask din a kasa ya hude abincin duka ya rube a kasa.

Bate cewa Anty Amarya komai ba ta nufi dakin Dizhwar din.

Binta tayi da kallo tare dayin murmushi itama ta koma dakin ta.



*ZEENASEER*

LAILAH-DIZHWAR Where stories live. Discover now