"Iya Abu kin ga Hussaina tana ƙaton loma ko"

"Wallahi ban yi ba, ƙarya take" Hussaina ta faɗa tana sake kai ƙaton loman tuwo bakinta.

"Ban hana ku magana idan ana cin abinci ba"

"Iya Abu ita ta fara" Hussaina ta faɗa tana nuna Hassana.

"To ya isa"

Yaran suka cigaba da cin abinci suna magana ƙasa-ƙasa.

Lokacin da Iya Abu ta miƙe za ta shiga ɗaki  ɗan cikinta ya wani juya.
Ta ɗan tsaya kaɗan kafin ta shiga ɗakin. Ita kam kunyar cikin take ji.
Yo abun kunya ne ace ita da 'yarta Indo suna da ciki lokaci guda.
Tun lokacin da ta haifi 'yan biyunta ta sawa ranta ta gama haihuwa. Musamman da Maimuna ta haifa musu jikan fari shekara ɗaya bayan haihuwar 'yan biyunta.
Sai gashi shekara bakwai, bayan ta gama cire rai da sake haihuwa sai ga ciki da rana tsaka. Ita kanta sai da cikin ya shiga wata na uku ta tabbatar ciki gareta. Ko Malam ɓoye masa ta yi sai da cikin ya girma sosai ya lura da cikin.
Wani abu da idan ta tuna yake ɗan sanyaya mata rai shine yiwuwar sake haihuwar ɗa namiji. Har cikin sallolinta addu'ar da take kenan Allah yasa wannan abinda ke cikinta ya kasance namiji.

Haihuwa goma amma dukkansu mata sai guda ɗaya tal, shi kaɗai namiji cikin mata tara.
Tun tana haihuwa tana tunanin namiji har ta cire rai da sake haihuwar namiji. Ɗayan dai da Allah ya bata kenan Muhammadu Nasiru. Amma bayan shekaru  wannan cikin ya sake sa mata kwaɗayin haihuwar namiji.

Kusan ƙarfe goma saura na dare Malam ya shigo gida bayan ya gama hira da abokansa a ƙofar gida.

Kafin su kwanta Iya Abu ke labarta masa cewa ta ji a labarai ana cewa an kusa gama jarrabawar Sakandare dan haka Nasiru ya kusa dawowa gida. Haka dai suka ɗan taɓa hira kafin suka kwanta.

***

Malam Muhammad Zaki ɗan Asalin garin Zaki ne wanda kasuwanci ya dawo da shi cikin garin Azare da zama.

Mahaifinsa babban Malami ne a garinsu.  Su shida Babansu ya haifa, biyu mata, huɗu maza.
Tun yana yaro da yai karatu a hannun Mahaifinsa sai da ya kai shekara goma shauku aka tura shi gaban wani Malami wai shi Malam Yusufa a garin Chinade. A nan ya shekara bakwai yana karatu kafin ya dawo gida bayan Malaminsa Malam Yusufa ya bashi 'yarsa ta uku mai suna Zainabu da suke kira da Abu.

Malam Muhammad na da shekara ishirin da ɗaya yayinda Abu ke da shekara shahuɗu aka ɗaura musu aure.
Lokacin da suka dawo Zaki abubuwa babu sauƙi dan kuwa Mahaifinsa ke ciyar da su. Da wannan Muhammad ya shiga garin Azare ya fara zama wajen wani ɗalibin Babansa yana koyon kasuwanci.
Haka dai har ya tara jari shima ya zo ya zauna zaman kansa.
Daga haka da abubuwa suka fara kyau sai ya ɗauko ƙaninsa Basiru, suka fara kasuwancin tare.
Allah kuwa ya yiwa kasuwar Albarka dan kuwa har fili ya siya ya gina gida shima Basiru da yai aure ya gina gidansa a filin da yayansa ya bashi kyauta.

Lokaci guda kuwa karayar arziƙi ta faɗa kan Malam Muhammadu. Daga nan kuma ya hau jinya. Mutane dayawa na faɗin wani abokinsa mai suna Malam Hamisu ne ya masa asiri, amma bai taɓa yarda da hakan ba duk da akwai alamu da suke nuna yiwuwar hakan. Dan kuwa tunda ya fara jinyar Malam Hamisu ya ɗage ƙafa daga gidansa. Wasu kuɗaɗensa da ya bashi aro duka babu su, kuma Malam Muhammadun ya kasa tambayarsa ina kuɗin.

Sai da Malam yai jinyar sama da shekara biyu kafin Allah ya tashi kafaɗarsa.

Bayan ya samu lafiya sai ya koma harkan noma gadan-gadan. Akwai rufin asiri kam, amma ba kamar da ba. Musamman ma da iyali suka fara yawa gashi mahaifinsa ya rasu shi ke kula da mahaifiyarsu da ƙannensa.

Wannan rufin asiri shi ya kawo su ga wannan lokaci, babu arziƙin amma akwai wadata da kwanciyar hankali.
Yanzu haka yana taɓa noma da kasuwanci kuma Alhamdulillahi ya fi ƙarfin roƙo.

Allah ya Azurta Malam Muhammadu da 'ya'ya goma. 'Ya'ya huɗu Abu ta haiho duka mata kafin aka samu namiji.
Sai da aka samu Maimuna, Aisha (Indo), Mariya, da Bintu kafin aka samu Muhammadu Naseer. Daga shi kuma aka sake haifo wasu biyar ɗin duka mata. Hadiza, Hauwa'u, Amina, da kuma 'yan biyu Hassana da Hussaina.

Yayyen Naseer duka an aurar da su. Maimuna aka fara yiwa aure tana gama makarantar Firamare. Daga baya aka haɗa Indo da Mariya aka musu aure, dama shekara ɗaya ne tazarar dake tsakaninsu.
Ita Bintu shekara biyu kenan da aka aurar da ita. Cikin 'ya'yan da aka aurar Bintu ce ba a aurar da ita da wuri ba, dan sai da ta kai shekara shashida kafin aka mata aure.
Ta gama Primary ta yi Form 1-3 kafin Malam yace bokon ya isa haka.

Hadiza da ke bin Naseer ma sai da aka shigo da maganar aurar da ita Naseer yace fau fau a barta ta kammala Sakandare tunda tana son karatu. Dama wani ɗan Baffansu ne ya fito wai yana sonta. Malam da Iya Abu kuwa dama basa iya yiwa Naseer musu saboda yadda suke son ɗan nasu. Har gara ma Malam ya kan ɗauke ido ya masa faɗa wani lokaci, amma Iya Abu sam duk abinda Nasirunta yayi dai-dai ne bata iya masa faɗa.
Kafin ta haifi Naseer, har gorin haihuwar 'ya'ya mata ake mata da aka ga ta haifi huɗu a jere duka mata. Bayan haihuwarsa kuma sauran ma matan ne dan haka shi take gani ta ji cewa yanzu babu mai mata gori. Bata haifi maza dayawa ba, amma Nasirunta ma NAMIJI ne kamar kowanne ɗa namiji...


***

Top-Notch season 3 wannan karan sun zo muku da daɗaɗan labarai guda uku.

NAZNEEN...exquisitely beautiful (Mai Dambu).
BINTUN BATUL (Shatuu).
GENERAL NASEER ZAKI (Azizat)

Za ku samu labarai ukun ta whatsapp a farashin 1300
Ɗaya #500
Biyu #900

Ku tuntuɓe ni ta whatsapp 08137311900.

*Account Details*

0008219237
Jaiz Bank
Azizat Hamza
08137311900

Ko kuma ku bibiyesu a manhajar Arewabooks.

@ Azizat
@Shatuuu095
@maidambu41




GENERAL NASEER  ZAKI (Book 1)जहाँ कहानियाँ रहती हैं। अभी खोजें