shafi na daya

523 7 0
                                    

_BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM_

*_A RUBUCE TAKE !!!_*
        (K'addarata)

      *Huguma*
Arewabooks: huguma

Free page 01

     Babban falo ne,wanda yake malale da marron din carfet mai taushi da kuma saitin kujeru kalar labulen wadanda suka yiwa falon qawanya,a tsare falon yake,ta yadda duban farko kuma kai tsaye ba zaka dauka falon tsohuwa bane,saboda ya wadata da kayan alatu na rayuwa bakin gwargwado.

         Daga tsakiyar falon,mamallakiyar falon ce zaune saman carfet din,babbar macace wadda gashinta mai tsaho da kuma santsi ya fara bayyanar da furfura saman sumarta,kana iya hangen hakan sakamakon gocewar daurin dankwalin dake kanta,fara ce sol har yellow takeyi,tsufanta bai boye kyan siffa da take dashi ba,wanda da alamu ta sameshi ne tun daga zamanin quruciya kawo yau,kana kallonta kasan ba cikakkiyar bahaushiya bace,hakanan kammanninta bana fulani bane.

       Daga gabanta kuma wata matar ce da suke diban kamanni da ita,saidai nata shekarun gaba daya ba zasu rufa talatin ba,ita dinma fara ce sol kamar matar dake zaune kusa da ita,wanda kana dubansu zakasan cewa 'ya da uwa ne,yaro ne saman cinyarta tana shayar dashi,dattijuwar mahaifiyar tata kuma tana daga kayan dake gaban nasu

"Duk da kayan sunyi kyau humaira,amma gaskiya nafison wadanda sukafi wadan nan tsada,Banason siyawa widad kaya masu sauqin kudi,gwara masu dan tsada da inganci" mai da dubanta halimatu tayi ga kayan tana sake qare musu kallo duk kuwa da cewa itace ta siyosu da hannunta,kayan irinsu ta siyawa yaranta,ta siyama widad din irinsu ne a nata zaton shine qarshen abinda zatayi ta burge ummu,saita maida dubanta ga dattijuwar

"Ummu,yanzu duk kyan wadan nan kayan basuyi miki ba?" Kai ta girgiza

"Basuyimin ba,kuma tunda nace basuyimin ba ai sai a canzo ko?,tunda dai kudina na saka zan siya,ba kudin wani bane" baki halima ta tabe tana sanya hannunta guda daya tana tattara kayan gefe,zuciyarta cike fal da bacin rai,akwai maganganu da yawa a ranta,amma tasan bata isa ta fadesu ba,yanzu yanzu rai zai iya baci indai akan widad ne

"Kin karba min kudin a wajen yaayan?"

"Yace sai ya dawo zai bayar na ajiye miki" sake baci ranta yayi,wannan karon ta gaza boyewa

"Uhmmm,Allah sarki,to Allah yasa suna da rabon saka ankon" kallonta ummu tayi ba tare da tace mata komai ba,idan da sabo ta saba da irin wadan nan dabi'un,ta rasa me yasa suka gaza fahimtarta,tana ganin son rai ne kawai da son kai irin na dan adam.

          "Latifa!" Ummu ta waiwaya bayanta inda qofar kitchen dinta yake ta qwala kira,daga ciki aka amsa sannan mamallakiyar sunan ta fito,wankan tarwada ce,mai matsakaicin jiki,a nutse ta qaraso

"Gani ummu"

"Shiga dakina saman pillow akwai purse dita ki daukomin" amsawa tayi da to sannan ta juya.

           Saidai bata ko kai ga isa dakin ba,ihu ya karade gidan cikin wata siririyar murya,ihu ne sosai hade da kuka.

          Da sauri Latifa ta dakata da tafiyar,sannan ta waiwayo tana duban ummu,itama ummun ita take kallo,fuskarta cike da tsoro

"Ummu kamar muryar widad fa" kai ta jinjina da sauri

"Haka nake shirin fada nima"

"Yo wace idan ba ita ba?,kaf gidan nan waye yake wannan tabarar idan ba ita ba?" Dauke dubanta ummu tayi daga kan.haliman zuwa ga ladifa,wadda tuni ta fara nufar qofa

"Yawwa,dubamin ita don Allah latifa"

"Yanzu kuwa" ta amsata tana ficewa daga falon.

          Yaronta halima ta kwantar a gefe sannan ta miqe itama tabi bayan latifan tana qunquni cikin ranta.

A RUBUCE TAKE k'addarataWhere stories live. Discover now