RAYUWAR JIDDAH ✔

Per DielaIbrahim

10.3K 856 277

RAYUWAR JIDDAH Labari ne akan rayuwar wata ya' mace mai suna Hauwa'u Jiddah. Let embark on the journey togeth... Més

01
02
03
04
05
06
07
08
09
10
11
12
13
14
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
37
38
AL'ADARMU
UMMI KWARAS
AL'ADARMU
AL'ADARMU

15

192 26 19
Per DielaIbrahim

RAYUWAR JIDDAH
Part 1/15
Mallakin DielaIbrahim
Am so sorry for keeping you guys so long, bani da lafiya ne, but alhamdulillah sauki ya samu.
Thank you for waiting!!!!

__________________Barhim Estate
Katsina state
8:30am

Ammi,Mama,Abba,Ummi and Momma,Dukkansu zaune suke a katafaren falon Ammi,ayayinda Momma tace Ammi kin taramu anan, Allah yasa dai lafiya?
Ammi tayi gyaran murya kasancewar ta mace mai dan kasaita kadan, tace
Assalamualaikum
Suka amsa da Wa'alaikumus salam

Ammi tace na tara ku anan ne don muyi magana ta fahimta a tsakanin mu, ta dubi Mama kasancewar itace abokiyar shawarar ta, tace Mama wato observation dina da duk wani tunani na daya karkata akan Jiddah da Faisal, shakka babu na hango tsananin shakuwa da sukai da juna, sannan alokaci daya kuma naga tunda yan uwan juna ne mezai hana ahada su aure don anawa tunanin nasan baza su ki son junansu ba moreover auran zumunci na da dadi ko ba komai environment daya suka taso, ga kuma tsantsar kulawa da suke bama junansu,
Ko ya kikace Mama?
Mama da take sauraran Ammi tace Ammi kinsan one thing da auran zumunci shine idan yara basa son junansu to kada ayi forcing dinsu, kina da gaskiya da kikace a hadasu  aure Amma Ni abinda nake dubawa shine why not a tuntube su ko suna da ra'ayin juna aji ta bakinsu.

Ammi tace No bazamu sako yara a maganar mu ba,haba Mama, kina nufin mubi ra'ayin yara, kenan mu bamu isa mu ce masu ga abinda muke so ba, gaskiya wannan ba solution bane....adai canja wata.
ke Momma ke kike zaune dasu Kuma kinsan irin shakuwar dasukayi me zaki iya cewa akan hakan tunda wajan ki Jiddah take bazaiyu na fara da Ummi ba.
Momma tace wato Ammi maganar ki gaskiyace akwai tsananin shakuwa atareda da su, lallai shakuwar da Jiddah da Faisal sukayi ni kaina ina mamakinta.....kallo daya zakai masu kayi zaton soyayyah suke yi while deep inside it su ba ita bace sukeyi, kawai so ne na yan uwan taka, amma ni anawa view din Ammi,
Shakuwa daban haka zalika Soyayyah na aure daban....Ammi bana tunanin suna son junansu, kamar yadda Mama tace a tuntube su toh nima ina bayanta saboda kada ayi forcing dinsu.

Ammi tace auuuu kema hakan zakice....to ina daidai daku ta waiga wajan Abba tace Kai Kuma miye naka opinion din?
Abba yayi gyaran murya sannan ya dukar da kanshi saboda tsananin Jin kunyar Ammi da yakeyi,Yace Ammi duk yadda kuka yi ai daidai ne matukar yaran suna son junansu to ai babu wata matsala.
Ummi tace nikam dama na dade Ina yi ma Jiddah kamum Dana,na dade Ina mata sha'awar auran Faisal, jira nake kawai lokaci yayi, Ammi Ina bayan ki dari bisa dari, nikam ma ba sai an tsaya tuntubar ko suna son juna ba, ni agani na kawai asanya masu rana yau, ayi auran idan taje gidan mijinta ta karasa karatunta tunda shekara dayace ta rage.
(Niko DielaIbrahim gyan gyadi😴 nakeyi sanda Mama, Momma da Abba suke magana, Amma Ummi na fara magana na farka jin ta amshi maganar da hannu bibbiyu na gyara zaman alkalami na nace Yaaaayyyyy Ammi da Ummi kanku naja aradu nima Ina bayanku😉😜)

Ammi ta dade tana tunani, tsahon minti biyar sannan tace agaskiya bazan iya tuntubar Yara ko suna son juna ba, lokacin abu kawai ayi shi, saboda haka kawai nan da sati biyu zamu sa rana Abba take note of this a gidan ka za'ayi komai, ni na gama maganata sauran magana kwa samesu ku basu shawara inma basu fara son juna na aure ba toh su ci dammara su fara don kuwa aure babu fashi (ban dai rantse ba amma fah babu fashi )ta tashi tana tafiyar ta cikin kasaita don dama Ammi haka take, saboda ta hada jini da sarauta ta wajan mahaifiya dukdama ba daga uba bane amma abin yabi jinin jikinta, moreover magana daya takeyi kuma ya zauna ko Mama ta sani shiyasa take bin ka'idojin ta badan tana tsoronta ba sai don Mama tafi Ammi hakuri da juriya kuma tun fil azal zamansu yayi dadi basa fada ko kadan.
Ammi na tashi ta shige bedroom tabarsu zaune sunyi jugum.
Momma nata faman bankawa Ummi harara tace dama na gano ki so kike aiwa Jiddah aure,
Ummi tayi dariya playfully tace Ammi babu ruwana aciki yanzu dai kisamu diyarki ki Bata shawara gwanda dai ayi musha gagarumin biki.
Momma tadau throw pillow ta jefi Ummi tana cewa ai sai kuyi, Ni dauke diyata zanyi ma mubar garin tunda daga zuwanmu kun fara kawo mana kabli da ba'adi🤨
Mama ta amshe da cewa tohhh ya dai isa Ammi ta rigada ta gama maganarta yanzu kamata yayi ku fadi yadda za'a bullo wa al'amarin.
Abba yace mama abu me sauki, ashaida masu don susan halin da suke ciki kamar yadda Ammi ta fadi............
Momma ta katse su tace toh ni dai bari kuji koda kun fada masu ban goyi bayan aiwa diyata aure,bata gama makaranta ba, don haka dole ajira ta gama ehhheee ta tashi ta fice adakin,...Ummi na ce mata, Momma ahuce haka mana 😝 sai kace mu ne muka kawo shawarar, auren zumunci fah akwai dadi Momma......
Amma Ina momma ko waigowa batayi ba ta wuce dakin Jiddah.
Abba yace Ummi kije ki bawa Yar uwarki hakuri, ni yanzu wajan aiki zani anjima saif zaizo ya dauke ki, "Ummi tace toh Abba Allah ya tsare.
Ummi tace Mama bari na shiga ciki.
Mama tace Nima zan shiga na dan kwanta Ammi ta katse min baccin safe yau.
Ummi tace lallai kam yakamata arama baccin nan don itama yanzu haka baccin ta koma.
Mama tace kwarai kaman kinsani, bari na shiga ciki,"To Mama.

Ranar Momma bata kula Ummi da Ammi ba har Ummi ta gama zaman ta Saif yazo ya dauke ta suka koma gida.
After 2days
Jiddah na kwance a cinyar Momma tana kallon T.V, afalon Ammi,
Saiga Ammi ta fito daga daki ta iske su zaune a palour tace ahhh Yar lelen Momma dadin cinya ake sha yau?
Jiddah ta tashi da murna ta nufi wajan Ammi tana cewa Ammi dama ke nake jira wlhy.
Toh gani Jiddodooo yar Momma ya akayi ne?
Ammi fura nake so na dakan hannu irin wanda kikeyi dinnan.
Ammi tace tohhhhh yau kuma rigimar ta wajan fura ya nufa.
Jiddah ta gyada kai kaman wata karamar yarinya.
Ammi tace toh bari sai na shirya zan miki saboda na dade banyi daka ba.
Jiddah ta daka tsalle tace yaaaayyyyy my best granny harda rungume ta.....sai taji Ammi tace
Jiddah ya kamata kema ki koya dakan furar ki ringa yiwa mijinki tunda ankusan maki aure.
" Jiddah ta tashi daga rungumar datai wa Ammi tace Aure kuma Ammi....wa zan aura?ni da ma nake karatu yanzu wani aure zanyi!
Ammi tace au wai Momma kuna nufin har yanzu baku sanar da yaran nan ba, ke Jiddah ance maki aure yana hana karatu ne kajimin iyayi irin naku na yan boko""and ke kuma Momma kun dauki magana ta da wasa kenan shiyasa baku sanar dasu ba koh" ta dubi Jiddah tace ke je kira min Yayanki Faisal.
Jiddah ta tafi zata kira faisal, dukdama ta kasa kwantar da hankalinta akan maganar data ji, bata jima ba suka dawo da Faisal.
Ammi tace zauna Faisal, kema Jiddah zauna.
Momma na kallon ta batace mata komai ba sanin halin Ammi idan ta kafe akan abu to babu wanda ya isa ya canja.

Ammi tace Faisal kana da wacce kake so ne?
Faisal yayi mamakin tambayar Ammi, wanda yaji tambayar kaman daga sama lokaci daya ya dago kai ya dubi Ammi,
Ammi tace yas tell me, kana da wacce kake so ne?
Faisal ya girgiza kai saboda ya rasa me zai ce lallai yana da wacce yake so, bakowa bace illah Jiddah kuma ita bata sonsa, beside shi son maso wani yakeyi tunda yaji kishin kishin awajan momma cewa Jiddah tana son wani dukdama baiyi wani bincike akan maganar ba....."Ammi ta katse shi da cewa, toh tunda baka da wacce kake so, Ni amatsayi na na kakarka wacce na isa dakai nayi maka mata kuma matar nan ba kowa bace illah Jiddah kanwarka.

Kut!!!ai karku so kuka yadda Jiddah take zaro idanu jin maganar Ammi, to which brain dinta ma ya kasa daukar maganar, bin Faisal kawai takeyi da kallo at thesame time Hafiz na fado mata arai tana tuna irin son da take mashi, sannan tayi alkawarin zata jira har zuwa lokacin dazai neme ta.....Amma all of the sudden Ammi ta shigo da wata magana, Wai Yaya Faisal zata aura.........
Faisal kuwa Jin maganar yayi kaman saukar aradu acikin kwanyarsa, ya kalli Ammi aranshi yace lallai idan dagaske kunnuwanshi sun jiyo abinda Ammi tace toh cewa tayi taba shi mata, kuma matar nan ba kowa bace illah Jiddansa, kanwarsa, abin qaunarsa.......Lallai ya rasa farin ciki zaiyi ko bakin ciki saboda yasan dai yana matukar son Jiddah amma ita ba sonsa takeyi ba and zaisha wahala ne kawai.. (niko nace har kayi concluding zaka sha wahala kenan)
Ammi ta cigaba dacewa, Jiddah na zaba maki Yayanki amatsayin mijinki, ku daidaita kanku, nan da sati biyu masu zuwa za'a sanya maku rana.

Jiddah ta kama kanta wanda take Jin kaman zai fita tsabagen Sara mata da ciwo dayake mata lokaci daya taji wani abu a saman forehead dinta kasan idanunta ji tayi kaman anzare wani abu awajan......and at thesame time tayi kara mai karfi sannan ta fadi kasa alamar suma tayi,.
Tashin hankali, Momma ta rugo da gudu ta kamata, haka zalika Faisal ma, Ammi ko tunani takeyi wai ko Jiddah nason tai masu na yan boko ne hakan yasa ta tashi tai shigewarta daka tana cewa aure dai babu fashi....Jin kukan Momma yayi  yawa saboda sun watsa mata ruwa taki farfadowa, Wanda har Mama taji ita da jikokinta suka taho falon da gudu, bashiri itama Ammi ta fito tana cewa wai dagaske Bata motsi Maryama, matsamin nagani,Faisal yace let's take her to the hospital please.
Momma tana kuka tace dauketa Faisal muje.
Haka suka kwasheta sai hospital
K/dara
Suna Isa nurses suka taimaka masu aka shigar da ita emergency room.
Likita mai suna Dr.Majdeed ya duba ta,ya yi iya bakin kokarinshi ganin ta farfado Amma abin yaci tura hakan yasa yai mata pain relief kawai sannan aka canja mata daki domin akwai wasu bincike dayake sonyi don ya lura condition dinta yayi high hakan yasa ko da yafito ya iske su Momma sunyi jugum, kwantar masu da hankali yayi sannan yace kada su shiga su jira ta farfado tukunna.
Suna nan zaune har dare misalin karfe goma, Nurse din da take dakin Jiddah ta fito da sauri ta nufi office din doctor, su Ammi suka mike tsaye hankali tashe suna ta faman leka dakin da Jiddah take ciki,suna nan tsaye sai ga doctor da nurse sun dawo suka shiga dakin hade da rufe kofa.
Tsahon minti ashirin suna cikin dakin kafin Dr.majdeed ya leko yace su shigo jiki asanyaye ya koma gefe ya tsaya yana son fada masu wani abu amma ya kasa,yana cikin tunanin ne yaji suna ma patient din magana.

Suna shiga suka iske Jiddah kwance idanunta abude tana kallon ceiling sai da Momma ta karasa wajan da sauri ta kama hannunta tana cewa Daughter kin farfado sannu Jiddah!
"Me zai faru sai taga Jiddah na hawaye tana jujjuya kai kaman makauniya tana cewa Momma, Momma bana gani idanuwana zafi suke min.
Faisal ya nufo wajan su da sauri yana cewa"Jiddah me idon ke maki ba gashi kina kallon mu ba!
Jiddah da dafe kanta tana kuma jin wani zafi da ciwo tace na shiga uku Yaya , Momma kaina ciwo ido na ciwo, ku tai make ni!
Dr majdeed yace uhmm Hajiya please ku dan je waje akwai analysis din dazan dauka, condition dinta is very critical, excuse me please.
Hakanan su Momma suka fita sukayi cirko cirko suna jiran Dr. Ya fito, sai ga su Ummi sun iso.
suma dai joining saukayi suna jiran fitowar Dr. Majdeed.

Misalin karfe 11:20pm Dr.Majdeed ya fito yace su sameshi a office." Suna shiga yace su zauna, sannan shima ya dade yana ta bincike a laptop dinsa kafin ya dago kai ya kalle su daya bayan daya" sai daya sauke ajiyar zuciya sannan yace ina jin tsoron fada maku abinda ya samu yar ku by seeing your faces nasan zaku shiga tashin hankali babba amma da fari Ina so ku kwantar da hankalinku, dukkan abinda ya samu bawa toh daga Allah ne,sai kuyi tawakkali,kuma ku sani komai yayi farko zaiyi karshe.
"Faisal yayi saurin katse shi da cewa look Dr.majdeed please ka fada mana abinda ya sameta"
Abba "yace yes Dr.majdeed fada mana kawai mu musulmai ne kuma munyi imani da kaddara mai kyau da mara kyau"
Zuwa wannan lokacin Momma Bata iya cewa komai hawaye ne ke Shirin zuba a idanuwanta, ita ko wani irin abu ne ya samu Jiddarhn ta,tun kafin likita ya fadi tafara ambaton "Allahumma ajirni fi musibati wa aklifni khairun minha"Kalu inna lillahi wa'inna illaihir raji'un"
Sosai Dr.majdeed ya tausaya wa Momma ahankali yace kece mahaifiyar ta koh?
Momma ta daga kai itama idanuwanta duk sun ciko da kwalla.
Dr.majdeed ya fara magana.

***********
Tohhh ghost readers ba'a magana, yakamata kuzo kuyi comment fah.
Ina team Hafiz
Ina team Faisal
Kuma kuyi naku comments din via comment box,ko advice ku bani eheen inajira kuma.
Happy reading 👏
*************

Vote
Comment

Continua llegint

You'll Also Like

2.3K 231 15
Saboda yadda mahaifin mu ya din ga saka Mana suna Fatima, har se da nayi tunanin ko Muna da alaka da shi'a ne, saboda Naga yawancin sune mutanen da k...
2.9K 241 29
The story is a long journey of twisted fate, humiliation, sacrifice, betrayal, victory, Epilogize...INFERTILITY gajeriyar kalma ce me ƙunshe da ma'an...
185K 3.6K 15
"Darling, you're the one I want." ranked #3: beckoliver (3/7/2022)
1.4M 117K 110
Kalmar QADDARA kalma ce dake rataye bisa wuyan kowanne bawa,haka rayuwa ta gada,tafe take da QADDARORI kala kala,masu zaqi da akasin haka...