page 6

74 4 0
                                    

*THIS NOVEL IS DEDICATED TO BARRISTER BILKISU GARBA*

*GABA KURAA*

     *NA SADNAF*


*Page 6*

           Balaraba jikinta har rawa yake wajen sunkuyawa dan ba wani bacci take ba saboda masifar da ta dora wa ranta na san ganin bayan kudirat.

Kamar a mafarki taji kukan Ishama da sallatin kudirat.

Inda ta juya ta Kalli Jafar dake ta sharar bacci duk da tasan ta shiga tsakanin su gani take kamar har yanzu Yana Santa tunda har ya kasa sakinta.

Baya ga haka ma tunda ya juyawa kudirat baya ya Wani susuce Sam Babu wani walwala a tare dashi.

Wani zubin haka zai ta kallon dakin kudirat.

Da dukan alamu aikin bai kama shi yadda take so ba dan ita burinta ya saki kudirat ta tafi da yaran ta zauna daga ita sai shi.

Tunanin ko dai nakuda kudirat din keyi yasa ta tashi da sauri ta nufi dakin kudirat din dan zata je ne kamar taimaka mata take so tayi amma ba taimakon za tayi ba tunda ba Wanda zai ganta sai ta shake kudirat da bbyn sun koma.

Dan gani take idan har ta bari kudirat din ta sake haifar bbyn rabuwarta da Jafar zai Kara mata wahala.

"Ki bari na taimaka miki ga kan bbyn ki nan"

Balaraba tace cikin san hana bbyn fitowa matse ma bbyn take so tayi.

Kudirat da ke nishi da k'arfi da hawaye dake zubo mata na ganin malaikar mutuwarta.

Ta kama hannun balaraba biyun da k'arfi ta saki nishi da k'arfi sai ga jaririya ta fado.

Balaraba kuwa sai k'ok'arin kwace hannunta take amma kudirat ta tattara duk wani karfinta ta riketa gam.

Kudirat cikin harshen turanci tace " I will not allow you hurt my bby"

Balaraba kuwa da ta fara tsorata da irin rukon da kudirat ta mata idonta a warwaje ta fara k'ok'arin fusge hannunta tana "taimaka miki zanyi ki cikani kinga jaririyarki a cikin jini"?

Kudirat kuwa kamar Kara mata k'arfi ake dan gani take tana cika balaraba zata shake jaririyar.

Ga Ishama dake ta tsalla ihu ga kukan jaririya

Jafar a hankali ya bud'e idonsa kamar Wanda aka tashe shi daga bacci.

Ba abinda ya sauka a kunnensa sai kukan Ishama da jaririya.

Kudirat ce ta fado masa a rai dan yasan itace Mai ciki.

Bai tsaya dogon tunanin ba ya mik'e da gudunsa yayi waje.

(Haihuwar da kudirat tayi da jinin da ta zubar ya karya asirin da Balaraba ta masa hakan na nufin ya dawo hayyacinsa")

Bankada k'ofar yayi dan rufewa balaraba tayi.

Inda yayi tozali da Balaraba dake ta kokawa da kudirat nasan kwace hannunta.

Ga Mahaifiya bata fado ba ga jaririya a cikin jini.

Wani irin sallati ya saki yayi wajen su da gudu dan take ya gane mai ke Shirin faruwa dan da  dukan alamu Balaraba zuwa tayi dan ta cutar da  kudirat.

Kudirat kuwa shigowar Jafar ya sa ta saki hannun balaraba ta zube a kasa dan bata da kwari ko kadan jiri ma ke dibarta.

Yadda Taga Jafar ya shigo tasan zuwa yayi ya taimaka mata.

Balaraba kuwa da hankalinta ya tashi da taji sallatin Jafar a bayanta ta wayance da "Zuwa nayi na taimaka mata ka ka Nemo Reza a yanke cibiyar dan Kudirat ta zaro Mahaifiyar da kanta.

GABA KURAA Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang