Da Ameen suka amsa, ya kalli hidayat yace
"princess Allah ya miki albarka, Allah yasa iya wahalar kenan lallai kin kasance cikin masu hakuri da juriya, Allah yasa kin tsallake taki kaddarar rayuwar kenan farin ciki ya dawwama a rayuwarki har gaban Abada"

Da Ameen suka sake amsawa, Aisha ta kalli hamza da gabaɗaya kamanninshi sun sauya sbd tashin hankalin da be taɓa Tunanin riskan kanshi ciki ba, kunya da nauyin mutanen parlorn duk ya rufeshi, kwarai maganan Mahaifinshi ya shige shi hajiya yanzu bata da wani gata se nashi, tunda har ta haifeshi shi kuma ita ce jarabawar shi...
"Hamza! Bana so ka hukunta kanka da abunda ba kai ka aikata ba, ka daukeni a matsayin mahaifiya kaman yadda nima zan zame maka gurbin hajiyarka, don Allah ka fawallawa Allah lamuranka shi kuma ze jiɓancesu ya wanke maka zuciyarka kaji? I will be always and forever be there for u!"

Sheshekar kuka ya fara ya kasa ɗaga idanu yana ji hajiyar shi na dariya wadda ze tabbatar maka da kanta fa ya kunce, ji waenda hajiyarshi ta zalunta masu kyaun zuciya da dabi'u, me yasa mahaifiyarshi bata fita kaman na Hidayat ba! Gabaɗaya tsoron rayuwa ya kama shi, kowa seda ya bashi baki a parlorn har hidayat hakan ya taimaka sossai wurin hana shi collapsing don dama ji yake kaman baze kara awa a wannan duniya ba.

Aisha ta sake kallon Raed tace
"Son! Kai kuma Allah ya saka maka da alkhairansa..."

Murmushi me kyau yayi yace
"ya riga ya saka min ma MAAMI tunda ya bani autar mata..."

Yadda yayi maganan yana kallon hidayat duk parlorn seda suka murmusa ita kuma tayi saurin sadda kanta ƙasa tana masifa chan ƙasa
'kaiii rayuwar Turai ma bata yi ba, ji ko a jikinshi' amma sunan da ya kira mahaifiyarta yayi mata sossai itama hakan zata ke kiranta.

"Lallai kam Naga alama, ya jikin yaya Buba mama?"
Daadida tace
"da sauƙi Dukda dai kam yana fama"

Tace
"Allah ya bashi lafiya"

Hidayat tace
"Maami!"

Se Aisha ta kalleta tayi murmushi, hidayat ta cigaba
"Don Allah Maami ki yafewa Baba Buba na san be kyauta ba, da a sadda Kika koma garesu da mugun ranunin hajiya da ya karɓe ki da ban yi irin rayuwar da nayi ba, da kuma kema baki sha wahalar da kika sha ba sede ɗan Adam ajizi ne kuma kinga ta sanadinshi Allah ya tsaga min farin ciki na, ya bani Norah da Farrah..."

Maman Rashida tace
"A'a daughter faɗi gaskiya dae, ya baki baban su Norah da Farrah kike son cewa kaman.."

Duk dariya suka yi ita dae kunya ya kusa kashe ta, wani irin murmushi Raed yayi yana kallon kunyar ta dake matukar burge shi, Maami tayi murmushi tace
"Hidayat dukkaninmu muna kuskure, dukkanninmu tara muke bamu cika goma ba babu wadda yafi karfin duk waennan abubuwan da suka faru ya faru dashi, wallahi ko don saboda kyaun zuciyar Raed na yafewa Yaya Buba, har Hajiya Balaraba na yafe mata saboda Hamza, Sauran abunda ta shuka wannan tsakanin ta da mahaliccinta ne, amma ba zan taɓa iya yafewa Amina cutar min dake da tayi ba don Allah Alhj a yau nake so a shigar da ƙarar Usman bisa Assault da kuma kisan kai da yayi.... Abinda ya miki ko a hikaya ban taɓa ji ba kuma kwarai yayi min mugun rauni a zuciyata basu chanchanci yafiya ba, don baka da gata se aka ce a wulakantaka a tozarta ka yadda aka ga dama?"

A nan kam bacin ranta ya fita, don abun yayi mata ciwo sossai da sossai.. Yau ko ɗiyar kishiya hidayat take iyaka kenan bare babu hadi ko na sisin kobo, ta kara da
"Na san Zaku yi tunanin me yasa basu ci darajar Abban su ba, Abban su mutumin kirki ne kwarai halinshi na gari ya bishi, shi sakayyarshi gudana nake so yayi har cikin kabarinshi so nake ya isar mishi har ya mishi sanadiyar shiga aljanna madaukakiya in har ina da rai da numfashi"

Duk gyaɗa kai suka yi, kiran sallar magrib ne ya ɗaga su suka fice, ana dawowa kuma aka fara shigo da abinciccika da Mahaifin Rashida ya bada order a kawo, bayan an ci an sha ya karkace ya fiddo dubu ɗari biyar ya ajiye yana kallon Maami yace
"Ga sadakinki again, yanzu da aka yi sallar magrib Alhj Usman ya sake biya aka maida aurenku"

Duk murmushi suke yi ita kam ta kasa ɗagowa sbd kunya Dukda Daadida na ɗaki, Hidayat ce ta ɗauko tana Adu'ar alkhairi zuciyarta fal farin ciki.

Se bayan isha Daadida ta fito da shirin tafiya, maman Rashida ta mata bayanin maida auren kuma tayi farin ciki ta zauna da Aisha sun sake tattaunawa inda tayi mata nasiha, Seda ta gama kan tace
"Mama hidayat fa? A yadda nake ganin Raed Please ku bashi matarshi hakanan mana? Babu anfanin cigaba da zaman"

Daadida tace
"nima na ga dacewar hakan, na so a kaita ne kaman yadda ake yiwa kowacce mace ƴar gata, gyaranta kuma be kamallu ba ke na ma fa ga kokarin wannan me dabi'un turawan da be shafawa idanunshi toka ya ɗauke ta ba, da sede in shafa in ji wayam"

Dariya Maami tayi tace
"Ai Raed baze taɓa wulakanta hidayat ba tunda har ya ɗauke ta da mutunci tun be san alakar dake tsakaninsu me karfi bane, na tabbatar duk abunda ya mallaka nata ne, zuciyarshi bashi da maraba da na Mairamu Allah ya ji kanta ya gafarta mata"

Daadida ta amsa da
"Ameen ya rabbi"

Maami ta cigaba da
"sannan gyara tunda an yi me yawan ko daga baya a hankali za'a karasa sauran please ku tafi da ita daga asibiti da Zaku duba Baba Buba se ya ajiye ki gida su wuce"

Mikewa Daadida tayi tana murmushi tace
"wannan fa son kai kike nunawa karara! Yaron ki kawai kika sani"

Dariya Maami tayi kan ta mike suka fito, tuni hamza ya ɗauki Hajiya sun fice tana ta maganganu, hidayat da Rashida suka samu a dining suna ta kuskus Daadida tace
"to in gulmata ake ma gani na fito se a ɗaga murya"

Dariya suka yi Rashida tace
"Daadida muyi gulmarki akan wani dalili? Ke da ba kwace mana samari da miji zaki iya ba?"

Itama dariya tayi harda tafi tace
"sa wasa kina zaune sede kiji nayi wufff da saurayin karki ganni haka a yarantata seda na kasa samari na zaɓa na darje!"

Duk dariya suka yi, Raed na shigowa wurin dining ɗin ya bar su Abba a parlor yace
"what's funny?"

Hidayat tace
"Don Allah paapi a baka zaɓi ni ko Daadida?"

Kallon Daadida yayi se ta gyara tsayuwa tana wani gyagyarawa wadda ya saka su kwashewa da dariya har Raed ɗin kan ya ɓata fuska yace
"Haba baby gurl har se kin tambaya? ga ki fresh blood me zan yi da Daadida?"

Wani dariyar suka sake saki, Daadida ta haɗe rai tace
"Dankari! Ni zaka rainawa wayau? Dama yau nayi niyyar baka matarka ku wuce to na fasa.."

Zaro idanu yayi yayi saurin zuwa ya rungumeta yana cewa
"oh my! Am so sorry my love ai daga ke ba ƙari, ke kaɗai ce da gaske a birnin zuciyar Raed"

Dariya sossai Maami ke yi su hidayat na taya ta ganin yadda Daadida ke ture shi irin ita tayi fushin nan.

Daga karshe kuwa haka aka yi Maami ta tattare yaran har junior tace babu me tafiya dasu, shi kam Raed daaɗi yaji daga Daadida se Hidayat suka wuce.

Rashida da iyayenta ma suka wuce, part musamman Abba ya warewa su Laure komai akwai yace su huta sossai, sashensu daga su se su Norah.

Asibiti suka fara zuwa suka duba Baba Buba gashinan dae jikin jiya e yau duk tausayin yadda bakinshi ya zama a bushe ya rufe su, gashi kaunarshi ne ze sa su taya likitoci tsare dokar su don a samu ayi aikin ya samu lafiya daga nan suka wuce gidan Daadida ya sauke ta kan suka fice..

Suna fitowa ya miƙa hannunshi ya sanya ya riko nata tare da matsewa yana sauke ajiyar zuciya, itama ajiyar zuciyar ta saki tare da Kallonshi suka sakarwa juna murmushi, a hankali ta maida idanunta kan hanyar tana kallon daidai inda ya taimake su, anan ta fara sanin shine ya taimake ta a rayuwa, anan ya fara illatar mata da zuciya da ƙaunar shi ba tare da ta sani ba, kirkinshi da irin rawar da ya taka a rayuwarsu ya sa zuciyarta bashi wani matsayin na musamman a ganin farko, suna isa gidan ta lumshe idanunta tana ayyana this is where it all started, gashi ta sake dawowa gidan as matar gidan mammallakiyarta... LALLAI ALLAH ME GIRMA NE!

#Vote
#share
#comment


                  🖤Gureenjo🖤

KOWA YA GA ZABUWA...Onde histórias criam vida. Descubra agora