ZAZZAFAR KAUNA 131-140

Start from the beginning
                                    

Girgiza kai kawai Najeeb yayi yana kallon Moha cigaba da cewa Moha yayi.

"Wai wata yarinya ce take sonka kuma kawarsu ce mai suna Khadija suna kiranta da suna Baby,tun ganin farko da yarinyar tayi maka taji tana sonka kuma sai ta gaya ma Zulaihat irin son da take maka, darling tace take ya nuna b'acin ranta a jiya kenan har taki yin lecture din da zasuyi bayan taka."

"Yarinyar ganin irin abunda Zulaihat tayi mata sai ta nuna ma Darling rashin jindadi nan darling ke gaya mata ai Kai mijinta ne."

Tsaki yayi yana cewa..."wannan maganar shine yasa ka gane da tana sona?maiye tayi anan da har zaka wani ce tana sona?yarinyar da yau din nan take gaya man bata sona na sake ta,Kai kuma kana man maganar jiya da ta zama past ya wuce ?

Dariya Moha yayi yana cewa..."ai kaji matsalarka saurin fushi ka bari na Kai karshe mana sai ka kwalishe ni yanda kake so,da dai ba sunanka Najeeb ba."

Murmushin gefen baki yayi yana cewa."okay Ina jinka Alhaji Muhammad K Abdullah." Dariya Moha yayi da yaga ya dan fara saukowa tunda har ya kira full name din shi,tabe baki yayi yana cewa..."Okay kana jina ko Alhaji Najeeb H Abdullah." Lumshe Ido kawai yayi yana murmushi dan ya kosa ya karasa jin shirmen Moha ko kuma yace tatsinniya.

Cigaba da cewa Moha yayi. "To da Zubaida ta gaya mata alaqarku sai tace amman ta cigaba da pretending din tana sonka a gabanta,shine fa yau ta Kara yin maganarka a gabanta har tana cewa ita zataje office tace tana sonka,kaga wannan dama ce da zaka gane shin tana sonka ko bata sonka."

Girgiza kai yayi yana cewa..."Taya kenan.?"

"Yauwa nawan yanzun dai Ina son ka fita sabgar Zulaihat ka daina yi mata magana idan ba ta kama dole ba,ka dunga shareta ka nuna baka san tana waje ba,ka daina zama a dunga inda ta zauna idan zaku je makaranta ba ruwanka da yi mata magana iyaka ka dauketa ka ajiye ta kawai."

Ajiyar zuciya yayi yana cigaba da cewa..."Sannan kuma ita wanann yarinyar Baby zaka bata dama kuna gaisawa amman a gaban Zulaihat ku nuna kuna soyayya,har waya ka dunga kiranta idan har Zulaihat tana wajen anan ne kawai zaka gane shin tana sonka ko bata sonka."

"Naji Moha amman kasan ban san raini kuma karda a shiga hakin yarinya daga soyayyar wasa ta maida ta ta gaske kaga kamar an cuceta fa,kuma ya zan gane tana sona idan har akayi abunda kace?Dan ni bukata ta kenan ta soni ta kaunace ni ta kula dani kamar jariri ta nuna man *ZAZZAFIYAR KAUNA* shine kawai bukata ta kasan dai yanda nike son ta wallahi ban iya rayuwa idan ba ta dan da ita nike son nayi rayuwa har *DA'IMAN ABADAN*

"Hakane Najeeb kishi,idan har ta nuna kishinta akan taraiyaika da Baby tabbas tana sonka dan in babu so babu kishi,idan har kuwa akwai so to dole akwai kishi Najeeb tanan ne kawai zaka gane tana sonka idan har tana kishinka and maganar Baby baka da matsala zan mata magana da kaina nasan ba zata yarda ta maida soyayyar ta gaske ba duba da irin son da take ma Zulaihat tana son suyi kawaice sosai da sosai,saboda haka take ta cire sonka a ranta dan ka kasance mijin Zulaihat fa."

Murmushi yayi yana cewa.."shikenan damuwa ta daman karda ta maida abun gaske na yarda da shawararka 100% Moha ,daman na fita a harkarta zan kuma k'ara fita ne duk abunda zai hadamu magana zan kiyaye shi in shaa Allah."
Yauwa Najeeb kayi magana idan har ka daure ka jure wallahi sai kaga riba a wannan plan din namu dan nima ban jindadin irin zaman da kuke yi da juna,kuma Kai ne *SANADIN* duk abunda ya faru ,ba yanda banyi da Kai ba akan ka dunga sakar ma Zulaihat fuska kana janta a jiki amman kak'i wai Kai karda ta rainaka ,ai shi so ba ruwanshi da wani raini a gani na dan haka Ina ji a jikina komai zai zo da sauki ya zama labari in shaa Allah."

"Allah yasa Moha,ai na gane kuskurena wallahi karka so kaji yanda sonta yake wahalar dani ,inasonta inakaunarta sosai da sosai." Bayan sun gama tautaunawa suka tashi duba da har tara na dare ya wuce kowa ya shiga gidan shi.

DA'IMAN ABADAN (ZAZZAFAR KAUNA)Where stories live. Discover now