Chapter 29-30

15 1 0
                                    

*FALAK🍒*

Mom Islam

E.O.W

Free

Page 29-30
_Ada nace zancigaba a paid yanzu nabarshi a free comments da tayani sharing shine zai nunamin muna tare_

Mutane da dama suna cewa wai meyasa Arif yayi galaba akan beauty?

Hankali a tashe tayi toilet tana kuka, bayan ta tsarkake jikinta da ruwan d'umi ta fito har yanzun tana d'ingisawa ba kamar d'azu ba, ta zauna bakin gado, abubuwan da sukayi ya dinga dawo mata kamar a faifen sidi.
Haka ta wuni jiki babu dad'i.
Germany
Falak ta kawo wa d'akin sirrin dad tsaro Wanda duk inda kakai da iya lissafi bazaka iya gano komai akai ba, yau kwanan dad biyu a Nigeria, a Rana ta uku ne ta samu nutsuwa harma ta samu tayi waya dasu, sukayi video call, Hibba ta dinga yi mata tsiya Falak na dariya,
Yau ta kasance Juma'a gobe bazataje office ba, ta fita da wuri dan tana son ta dawo da wurin taje siyayyar abubuwan da suka k'are mata, bayan driver yayi parking d'inta ta fito cikin sauri ta k'arasa masu tsaron gurin sunata gaisheta, a nitse take amsawa har ta shige ciki, sai data zauna ta tuna ko breakfast batayi ba, ta dafe goshinta tare da janyo system d'inta da ta shigo da ita mak'ale a kafad'arta, ta fara bincike game da wani abu daya shige mata duhu jiya, ikon Allah Abu kamar almara, hotonsu Manaf tagani harda boka da d'aya abokin tafiyar nasu, cikin mamaki tace "sukuma waye ya shigo dasu?, ta Kara da cewa "inaga kamar nasan wannan" ta nuna Manaf" amma koba komai zan bibiyesu kosu d'in meye manufarsu da zasu shigewa dad har ya amince ya d'aukesu aiki?"
Ta mik'e da sauri ta nufi na'u rar ma'aikatar, dawo da abubuwan da akayi kusan sati guda ta dingayi baya, har ta hango shigar mutane ta duhun wani guri, cikin nazari da dogon tunani ta fara tunanin lokacin da suka fito, ita duk ba wannan bama, burinta shine tasan suwaye suka turo su? tayi iya bincikenta har yanzu bata gano hakan ba, yau k'arfe 5:pm tabar gurin aiki, a gajiye ta fito hannunta rik'e da system, tana sauri taje parking space tad'au mota ta buge wani mutumi bature wanda batasan ko shid'in waye ba, da sauri tace "sannu" dan bata da burin wulakanta d'an adam, sunkuyawa yayi zai d'auki paper d'in da suka zube, tayi saurin durk'usawa ta kwaso masa, idanunta suka sark'e a nashi, wani irin kallo sukewa junansu daga k'arshe Falak tabar gurin da gudu, saurayin data cikaro dashi, yakai 35yrs fari ne tasss daka gansa kasan ba d'an Nigeria bane, gashin kansa  baƙi ne wulik yayinda ƙwayar idonsa ta kasance baƙa amma ba sosai ba, hancinsa dogo bakinsa madai-daici, cigaba yayi da kallonta tana tafiya cikin sauri, ya kalli papers d'in data miƙa masa ya rungume tare da sakin murmishi, ya fice.
Kai tsaye ta wuce mota tana tuna Meta mance can wanda bata ɗauka ba?,
Ta shiga mota ta wuce gida, kasancewar sai tayi sallolinta sanan take fitowa ya rage yanzu sallahr magrib kawai take jira, da sallama ta shiga parlon daya kasance babu kowa sai ita kad'ai,masu aiki ma da part d'insu sai time d'in aikin yayi suke shigowa, ta zauna tare da ɗora ƙafarta kan table, a hankali ta fara tuno wannan saurayin da ta buge,  a hanya, ta dafe kanta cikin k'an-k'anin lokaci ta tuno abubuwan da suke faruwa da ita na rayuwa, a fili tace "har yanzu inada tambayoyi akan rayuwata duk da cewar ni ma'aikaciyar Dss ce meyasa ake yawan kidnapping d'ina shin me na tarewa mutane?"
A hankali ta runtse idanunta tare da tuno kalmar da dad ya gaya mata,
Wato "karki dinga damuwa da kidnapping d'inki da akeyi zan dinga amfani dake gurin farauto masu aikata lefuka musamman masu kidnapping mutane"
Ta mik'e tsaye tare da fara Zagaye d'akin tana had'e hannayenta.
Nigeria
Yau kwanan dad biyu, kwanansa d'aya a garin yaje ofishinsu suka gabatar da meeting d'in da yazo yi, sosai suka tattauna game da abubuwan da zasu kawo musu sauye-sauye a aikin nasu,
Gidan Saudart•
Cikinta ya shiga wata na takwas, hamma Aliyu ya kammala siyayyar twins d'insu da aka sanar musu a asibiti, suna zaune a parlo shida Saudart hannunsa rik'e da remote ita kuma tana can gefe a zaune kan kafet ta jingina da kujera ya d'auketa photo, ta harareshi cikin sigar wasa tace "haba dan Allah meyasa zaka dinga d'aukata hoto bayan kasan nayi wani iri?"
Yayi dariya ya taso daga inda yake ya zauna kusa da ita a k'asan kafin yace "ni kyau kike yimin inason in dinga ganinki kina tafiya har wani dad'i nakeji"
Saudart ta wurgesa da small pillow tana turo baki,
Daga bakin k'ofar aka fara nocking,  Hamma Aliyu ya mik'e yana yi mata gwalo, yana bud'e k'ofar ya washe baki sakamakon ganin dad da yayi tsaye a bakin k'ofa hannunsa rik'e da wata babbar leda,
Hamma Aliyu ya durk'usa har k'asa ya kar6i ledar yana yiwa dad sannu da zuwa, Saudart na ganin dad ta fashe da kuka zata taho da gudu ya dakatar da ita,
Bayan dad ya zauna sun gaisa Saudart tace "dad dan Allah ka kaini gurin Ummu"
Dad yayi murmishi kafin yace "Saudart kenan akwai gatan daya wuce d'akin mijinki?"
Daga 6angaren Hamma Aliyu kuwa sai gwalo yakeyi mata tana sake turo baki, dad yace "wannan tsaraba ce na kawo muku, Aliyu ka biyoni gida zuwa anjima kamar da yamma"
Hamma Aliyu yace "to" cikin ladabi.
Dad yayi musu sallama ya wuce.
Egypt
Yau su momy suketa shirye-shiryen komawa Switzerland kasancewar sammako zasuyi sukahau jirgin safiya.
A fannin Fadwa da Abdul-Naseer soyayyarsu suke Sha  abin gunin ban sha'awa yayinda granny tasa musu ido duk wani motsi nasu tana kallo akan idonta sukeyi, yau kwanansu biyar da aure, rabon Abdul-Naseer da fita wani guri mai nisa tun bayan auransu,
Yau an tashi da zafi sosai, dan neman magana Abdul-Naseer da Fadwa suka dawo parlo cikin dare, kasancewar kujerar mai zaman mutum Uku tanada fad'i sosai, suka kwanta akan kujerar rungume da juna, hannun Abdul-Naseer a cikin rigar Fadwa haka sukayi bacci, granny ta fito tana haske-haske da fitila ta haskosu ta rafka salati tare da ajiye fitilar a gefe tana tafa hannu, duk basu jita ba bacci ya kwashesu, tace "yo ni zainabu naga fitsara k'iri-k'iri kodai basu cikin hankalinsu ne? tsabar ruwan iskanci hannu a rigar mace kamar tsohon bunsuru?"
Abdul-Naseer ya d'an motsa sbda jiyo magana da yayi, a hankali ya d'ago ya kalleta, kafin yace "kekuma me ya kawoki nan?"
Granny ta ta6e baki kafin tace "ni ban tambayi meya kawoku nan ba ga d'akinku can sai ni zaka tambaya"
Cikin bacci Fadwa ta janyo hannun Abdul-Naseer ta rik'e ya kwanto a hankali, granny ta rushe da ihu tana cewa "wayoo nashiga uku zasu koreni dan wannan kora da hali ne"
Fadwa ta mik'e da gudu ta rungume Abdul-Naseer cikin firgici, granny tace "wato ke ko sadakar kunya baki da ita, lokacin da akayi rabon kunya kinyi bacci niyau naga ta kaina"
Ta shige d'akinta tana sababi,
Abdul-Naseer yace "nifa jinayi A.c d'in d'akin baya bada iska sosai zomu koma"
Daga can granny data jiyosu tace "munafukai, shiyasa ka mak'ale mata kak'i fita aiki sai kace kana wani abun mtswww"
Switzerland
Momy sun sauka lafiya, taje ta samu beauty tana zaune ta rame sosai, cikin rashin hankali ko hutawa momy batayi ba ta fara tambayarta shin lafiya kuwa meya faru, kodai baban nata yayi mata wani abu ne?,
Beauty ta fashe da matsanancin kuka mai tsuma zuciya kafin tace "momy ke kika haifeni? baba shine mahaifina?"
Momy tayi shiru, kamar wacce ruwa ya cinye jikinta yayi mugun sanyi kafin tace "my beauty meyasa zaki yimin wannan tambayar?"
Beauty ta Kuma fashewa da kuka tace "momy akwai wani abu da nake tantama shin kud'in iyayena ne?"
Momy taja Jakarta gefe kafin tace "ba nice mahaifiyarki ba, haka Maleek ba shine mahaifinki ba"
Beauty ta zaro ido cikin tashin hankali tace "suwaye iyayena shin Arif d'anki ne?"
"Eh Arif yaronmu ne"
Momy ta fad'a cikin gasgatawa,
Beauty tace "momy ki bani labarin asalina ko hankalina zai kwanta momy ki sanar dani' dangina domin in samu nutsuwa in sassauta hukuncin dana yankewa kaina domin in samawa zuciyata salama"
Momy ta fashe da kuka harda share hawaye tace "beauty zan baki labarin komai dangane dake da rayuwarki ke harma da ahalinmu shin kin fara tantamar ke ba jininmu bace?"
Beauty ta fice da gudu ta fad'a kan gadonta tare da sakin kuka mai ban tausayi,
Arif, sosai yakejin nutsuwa a ransa yanajin tsantsar kasancewa da ita, sbda tsananin sha'awarta da yakeji, ya rungume hannayensa yana wani lumshe ido,
A fili ya furta "kai naso sake kasancewa da waccar yarinyar, gashi momy ta kirani Ina tunanin ma ta dawo"
Washe gari da asbha, bayan anyi sallah sam beauty ta kasa koda sake runtsawa saboda kuka da tunanin tanada gata ko bata dashi, meyasa Arif yayi mata fyad'e meyasa-meyasa"
Tana tsaka da kuka Maleek ya lek'o, da sauri ta share hawaye kafin tace "baba barka da safiya"
Maleek yace "yauwa y'ata ya kika kwana?"
Beauty tace lafiya, "baba kawu Manaf fa?"
Maleek ya zaro ido alamun rashin gaskiya kafin yace "Manaf ai yana can ma'aikatarmu yana kula da safarar kayayyaki"
Beauty tace "Allah ya taimaka"
Maleek ya amsa da amen fuska a yamutse"
Bayan tafiyarsa Arif ya shigo yana sanye da blue jeans da t-shirt fara daga bakin k'ofa yace "hii my beauty"
Beauty ta wurga masa harara kafin tace "karka sake shiga rayuwata zanyi maka illa illar da baka ta6a tunanin samun irinta ba"
Arif yayi murmishi kafin yace "haba k'anwata nid'in yayanki ne danme zaki so illatani?"
Beauty ta juya masa baya, momy ta shigo, Arif yad'an risina kafin yace "momy sannu da dawowa"
Momyn ta harareshi kana tace "wato kafi k'arfin kace kazo kayimin sannu da zuwa sai yanzu dana shigo gurin k'anwarka?"
"Kiyi hakuri momy"
Arif ya fad'a yana had'e hannayensa.
Germany
Yau ma kamar kullum Falak ta kammala duk wani shiri nata, da wuri ta fita lokacin k'arfe 8:am, bata d'auki komai ba sai system d'inta da foodflaks d'an madai-daici, tana sanye da Pakistan na riga da wando, rigar bak'a ce, anyi mata ado da milk d'in zare yayinda wandon ya kasance milk color, haka ma d'ankwalin, yau dai abin mamaki hijab tasa iya guwaiwarta, ta fito ta shiga mota securities d'in gurin sunata d'aga mata hannu, driver ya shiga suka wuce, suna isowa ma'aikatar driver yayi parking, mutane da dama sai kallonta sukeyi, rabonta da sanya hijabi, a tak'aice ma babu wanda zaice ga ranar da tasa hijab sai yau, sosai hijabin mai ruwan k'wai yayi mata kyau, yasha guga sai shek'i yakeyi,
Ta k'arasa ciki hankalinta nakan takardun, daga can bakin k'ofar akayi nocking,
Cikin bada umarni tace "yes com in"
Saurayin jiya ya turo k'ofar ya tsaya tana jiran izinin zama, a hankali tace "ka zauna"
Ya zauna yana k'arewa halittar fuskarta kallo, kafin yace "ma'am barka da safiya"
"Falak tace barka meke tafe dakai"
"Nazo neman aiki ne"
"Falak ta kalleshi kallon tsanaki kafin tace "kodai kazo ka rama bigekan da nayi ne?..."

Afuwan fans nayi tafiya ne, kuma gurin Babu network shiyasa kuka jini shiru.

*Mom Islam*

FALAKWhere stories live. Discover now