ALMAJIRA Babi na uku

316 6 0
                                    

dahtulkhair*😘
[9/9, 9:11 PM] It B Y Ebrerheem: 🍆🍆🍆🍆🍆🍆🍆🍆🍆🍆
    *AL-MAJIRA*
🍆🍆🍆🍆🍆🍆🍆🍆🍆🍆
          *NA*

*JEEDDAH TIJJANI*
        *ADAM*
           *(jeeddahtulkhair)*

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM*

🍆🍆🍆🍆🍆🍆🍆🍆🍆🍆

*Sadaukarwa gare Ku 'yan uwa rabin jiki NADEEYA BABA IBRAHIM, AISHA BALA ILU & AISHA ISMA'IL ISAH, Allah ya bar xumunci da kaunarka juna*

2⃣1⃣

Tunda Ammi ta koma d'aki ta rasa abinda yake mata dad'i, duk tunanin duniya ya mamaye mata xuciya, tsoro da firgici ne fal xuciyarta, sai ta kasa fad'awa su Hamdan abinda innah karime ta fad'a mata. nan da nan xaxxabi ya rufeta, gumi ne yake ta yanko mata, saboda ta san sharri da makircin innah karime, tasan ko kad'an ba 'kaunarta suke yi ba ita da iyalanta.
Alwala ta d'auro ta fara jera salloli tana ro'kon Allah ya bata kariya ita da abinda ta Haifa. Bayan ta idar ne Hamdan ya lura da yanayin tashin hankalin da take ciki,tambayarta yayi
" Khalaty me yasa naga yanayin ki ya canja gaba daya? kada fa ki sa damuwar wannan mahaukaciyar matar a ranki, har hakan ya cutar da ke, ki sa a ranki baxa ta miki abinda Allah bai 'kaddara miki ba. ke da ki ke da Allah wace damuwa ce xata dame ki, shiru tayi har sai da Hamdan ya gama nasihohinshi gareta.

"Hankalina ya tashi da maganar da ta fad'a min lokacin da xata shiga mota ne Hamdan"
Me tace miki? Ya tambayeta
Xan gani tace min, kuma kasan sharrinta.
"Au don. Wannan maganar ma ai ba abar d'aga hankali ba ce, alheri xa ki gani insha Allah, ki manta da ita kawai".
Amsawa tayi da ameen suka shiga hirar duniya.

Tunda su innah karime suka hau mota suke ta tsine wa Ammin Nauwar a tunanin su, ita ce ta bada umarnin a fitar da su daga gidan.
"Innah wlh dole mu d'auki mataki a kan shegiyar matar nan, saboda na fuskanci ta gama shanye min 'kanin mahaifi ta gama mallake shi , ni fa innah so nake yi ma gaba daya rayuwata ta dawo gidan, don naga wata yarinya mau kyau ta min a gidan, kin ga Idan na dawo sai ki bani ita na aura, komai na ubanta ya dawo hannuna,kuma ita ma fa innah baxa mu barta haka ba, dole sai mun mallaketa.

"Dadina da kai kaifin hankali Magaji, ashe kaima ka fara fuskantar halin da ake ciki, wannan matar da kake gani ba karamar shu'uma bace, dole mu tashi tsaye a kan d'an nan Idan ba haka ba xa mu ga ana yi babu mu, ga shi har d'an uwanta ta kawo ya ci arxi'ki mu kuma ko oho, Wai a ce har ya samu damar yin dambe da kai, saboda yana  da d'aurin gindi, to wlh baxa ta sa6u ba, dole mu tashi tsaye.

"To ai duk laifin ku ne innah, inji Magaji da kun fara yun'kurin yadda xa mu yi mu koma birni da rayuwa, amma kamar Wad'anda aka yi wa d'aurin baki ku ka yi Watsi da abin, Ku ka ma daina  xancen fada d'aya"

"Idan d'aurin bakin aka yi abin mamaki ne? Matar nan fa matsafiya ce na dad'e da sanin haka, a haka ne dai xaka ganta kamar mumina, tana rero xance wai ita ta Allah. Ai mun gamu tunda tayi mana haka, mu xuba mu gani.
Hirar da suka yi ta yi kenan har suka isa 'Dan batta.

Suna huci suka fito daga motar, ko sallama basu yi wa Wad'anda suka kawo su ba suka fito.

Cikin gida suka shige ran su yana ta musu xafi saboda abinda suka je nema basu samu ba, kuma bu'katar su bata biya ba. Habi suka tarar tana ta faman surfe, yadda taga yanayin su ta tabbatar da cewa, ha'kar su bata cimma ruwa ba, ga shi kuma ta ga Magaji ri'ke da hannun shi yana d'ingishi, sakin tabaryar ta yi ta 'karaso gurin da suke.

"Ya na ganku haka da wuri, kuma babu alamar Walwala a tattare da Ku?"

"Ta Yaya xaki ganmu da Walwala an mallake min jika ya xama na wata daban, kalli hannun Magaji ki ga aika-aikar da wani shegen yaro yayi masa"

AL-MAJIRA CompleteUnde poveștirile trăiesc. Descoperă acum