YASMEEN.

By JannatMN

1.2K 63 13

Labari ne da ya k'unshi abubuwan ban mamaki kama daga kan:-Hak'uri, juriyar, tausayi, soyayya, yaudara, cin... More

Page 1 ✍🏻
Page 2✍️
Page 3✍️
Page 4&5✍🏻
Page 6&7✍🏻
Page 8&9✍🏻
Page 10&11✍🏻
Page 12&13✍🏻
Page 16&17✍🏻
Page 18&19✍🏻
Page 20&21✍🏻
Page 22&23✍🏻
Page 24&25✍🏻
Page 26&27✍🏻
Page 27&28✍🏻
Page 29-30✍🏼
Page 31-32✍🏼

Page 14&15✍🏻

30 1 2
By JannatMN

*°🔘°YASMEEN°🔘°* 
   *1442H/2020M.*



®☄
*GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍*
_{Gaskiya ɗaya ce daga ƙinta sai ɓata, burinmu mu faɗakar da al'umma domin ribantar duniya da kuma lahira.}_

         '''🎐G•W•A🎐'''
*_GASKIYA DOKIN ƘARFE•_*🏇🏼


*NA MARUBUCIYA:-*
*JANNAT M. NASIR✍🏼*
*Wattpad_@JannatMN*

*SADAUKARWA GA:-*
*MY BLOOD SISTER*
*MARYAM M. NASIR (MANAB ƳAR BABA)*

Wattpad:- *GaskiyaWritersAsso.*
Gmail:-gakiyawritersassociation@gmail.com
Youtube Channel:- *GASKIYA 24TV.*
Facebook page:- https://www.facebook.com/Dokinkarfe2019/
Bakandamiya:-
*GASKIYA WRITER'S ASSOCIATION.*

   
         *😭KUKAN KURCIYA.....🕊 (1)*

      _*Ƴan uwa sau da yawa masoyinka ke cutar ka, maƙiyinka ya taimake ka. Ka ga mai kuɗi yana sata, talaka yana sadaka, makaɗi ya faɗi gaskiya, malami yayi ƙarya. Wannan shi ya sa aka kira ta duniya. Allah yasa mu dace. Ameen Ya Allah 👏🏻*_


*SHAFI NA 14-15📑*

*__________📖* "Assalamu Alaykum, ƴar tsohuwancy kina nan kuwa?"

      "Ka ci gidanku Audu, nice tsohuwar? To yaro ko ubanka na fi shi ƙwari da lafiya ballantana ma a gangaro gareka kai yaro."

    "Hhhh! Lallai ma wannan tsohuwar da tsaurin ido da yawa kike, yanzu dan Allah baki ji nauyin maganar da kika faɗa ba? ki dube ki fa ki ga duk kin gama cin zamanin ki kinyi laushi, amma kike haɗa kanki da irin mu masu jini a jika, to yasin ki sake...." Bai ƙarasa maganar da yake yi ba ta ƙatse shi da cewa,
   
    "Ka ji ni da ja'irin yaro to duk waye yasa ni na yi laushi ban da gyatuminka, ai da ban kawo shi duniya ba da babu abinda zai sa nayi laushi, domin shi ya fara sauya min halittuna daga zuƙeƙiyar mace, duk da har yanzu a zuƙekiyar nake duk da laushin da gyatuminka yasa nayi, kuma a hakan ma ko yanzu nace zan yi aure, sai ka ga ana bin layi domin cike form ɗin fitowa takarar aurena."
   
    "Caɓ! Wai akan wa za'a cike fom ɗin ne? ni ban gane zancenki ba, dan ni a iya sanina baki da wata buɗurwar ƴa da za'ayi layi akanta, dan ke nasan ko a sadaka zamu bayar da ke babu wanda zai ɗauke ki, ƙarshe ma guduwa za'a rinƙa yi idan akayi tozali dake tsohuwancy."
   
    "Audu wallahi zan ci mutuncinka, ka dube ni da kyau daga sama har ƙasa, ka ga ni na wuce duk irin lomamun ƴan matan nan naka, wanda duk ƙwailaye ne irinka ko irgan ɗangi ba su fara ba ballantana ma....."
   
    Saurin dakatar da ita yayi bata ƙarasa amayar da abinda ke bakinta ba, dan yasan halinta yanzu zata kwaɓomasa zancen da zai sashi jin kunya bai shirya ba yace, "Haba ƴar tsohuwancy tamu ke daɗi na da ke baki san wasa ba, ai ni tuni na san cewa kaf ƴan matan da nake gani babu wacce takai ki haɗuwa, gaskiya kakan mu ba ƙaramin dace yayi ba da ya samu zuƙeƙiyar mace irinki hanci har baka tsohuwancy tamu, amma dai nasan ba'a ƙaramin artabu ya sha ba, wajen ganin ya zama tauraronki mafi haske a  cikin buyagin da suke zuwa neman soyayyarki, ƴar ƙyaƙyawar tsohuwar mu?"
   
    "Artabu ma babba aka sha Audu, domin kaf ƴan matan ƙauyen mu a lokacin babu wacce ta kai ni kyau da iya ɗaukar wanka, ina gaya maka Audu ai mun sha gayu ada."
   
    "Hhhh! A hakan? Caɓ! Gaskiya an yiwa ƙyau yankan baya, kice kawai tsohuwancy kun sha kwalabo da yawa? To amma mai yasa yanzu bana gani kina gayu ko dan ƙara'in nan da ƙyawawa ƴan matan masu jini a jika suke yi?"
   
     "Eh! Mana a hakan, baka ga yadda gyatuminka yake da kyau ba? Ai ni ya kwaso gaba ɗaya, shiyasa yake da kyau kamar yadda nima nake da shi ba, ƙara'i kuma ai gyatuminka ne yake hanani yi, shi ya je yana yi shiyasa ka ganin haka."
   
      "Allah sarki tsohuwancy, kice shiyasa na gani gaki nan kin koma kamar wata juji, har ki ɗan ban tausayi fa sosai."
   
       "Ai kuwa dai shiyasa ka ganin kamar juji, shi kuma gyatumin ya zama kamar kwatamai, saboda tsabar ƙara'in da yake yi, ai dole na baka tausayi."
   
    Ganin yadda take wankesa a fakaice kamar yadda shima yake mata ne,  "Hmm!"  murmushi yayi ya dakatar da ita da cewa, "Ni ba ma wannan ba ga saƙon ki inji Ummana tace a kawo miki."
   
    Karɓa tayi tace, "Allah sarki Khadijatu bata gajiya, na gode sosai Allah yayi mata albarka ya raya mata zuri'atar baki daya, fatan dai tana nan lafiya ƙalau? Dan na ɗan jima rabon da na ganta."
   
    "Ameen Ya Allah tsohuwancy, Lafiya ƙalau take, tace ma tana gaishe da ke, kuma tace kiyi haƙuri da jinta da kika yi shiru kwana biyu, ta nan zuwa insha Allah."
   
    "Bakomai wallahi ai ba sai ma ta takura kanta da yawa ba, ni a hakan ma na gode sosai. Wai ina mutumina ne Aymanu? Bai biyo ku bane?"
   
    Aymana ce tace, "Yana gida laifi yayi wa Umma, shine tace ba za'a zo dashi ba."
   
    "Ai ta kyauta dan ice tun yana ɗanye ake tankwarasa, in ya bushe ba zai tankwafi ba, ka ga ai gobe ba zai ƙara aikata abinda yayi ba."
   
    "Haka ne tsohuwancy ashe dai har yanzu kan yana ja da yawa."
   
    "To..! Da ce maka aka yi irin kan gyatuminka ne da ni da zai dai ja tun yanzu."
   
    "Ke daɗi na da ke a fakaice sai kita ciwa mutum cin mutunci ba ruwanki."
   
    "Hhhh! Au! Wai dama kai kana jin haushi."
   
    "A'a! Bana ji, saboda zuciyar dutse gare ni kamar yadda taki take."
   
    "Hhhh! Ai kyan ɗan ya ga ji ubansa, kaga baka gada a banza ba hhh." Ta ƙarashe maganar tana masa dariya, don tasan iya ƙularwa ta ƙular da shi sosai, dama haka take so domin in ba haka take masa ba wata rana zai iya ɗaura mata hawan ruwa.
   
    "Aymana tashi mu tafi, ni dama in dai dan ta wannan tsohuwancy zan zo gidan nan, to yasin sai ta yi shekara da shekaru bata ganin ba."
   
     "Umma ta gaida ashsha Audu, ni dama ban gayyace ka ba, inka ga dama kada ka ƙara zuwa ida nake ni bai dame ni ba."
   
    "Haka kika ce ko? Ai na kusa na tafi na bar miki ƙasar gaba ɗaya, kin ga ina tafi sai ki zuba ruwa a kasa kisha."
   
    "Eh! Haka nace, a sauka lafiya duk inda zaka ka je, ruwa kuma zan zuba a ƙasa na sha har da suɗi."
   
    Bai ce mata komai ba ya kama hannun Aymana suka fice a gidan, ita kuma dariya kawai take masa tace, "Bishiyar giginya, na nesa, yaro sha inuwarka kawai." Tana gama faɗin haka ta cigaba da abinda take yi kafin su zo.
   
   
                    _*(•)(•)(•)(•)(•)*_
   
   
    Da sallama a bakinta ta tura ƙofar ɗakin, hannuta ɗauke da farantin ta shiga cikin ɗakin. Kwance yake ya kalli bango yana wasa da shi, bai ji shigowarta ba har ta zauna gefensa ta shafa kansa, jiyowa yayi ya ga wane ne yake shafa masa kai, Umma ya gani ya tashi zaune ya buɗe baki zai yi magana ta ɗaura yatsanta a kan bakinsa alamun yayi shiru, shiru yayi bai ƙara yin yunƙurin cewa kala ba. Farantin da ke hannuta ta aje a gefen gadon ta ɗauki ƙaramin plate dake rufe ta buɗe ta, lafiyayen abinci ne a ciki ta ɗauki cokali ta fara basa abincin a baki yana ci, sai da ta tabbatar ya ƙoshi, sannan ta aje plate ɗin ta ɗauko lemo ta zuba masa a kofi ta ba sa ya sha ya koshi, tashi tayi ta haɗa kayan ta ɗauka zata fita yace, "Umma ki yi haƙuri wallahi na daina ba zan ƙara ba." Jiyuwa ta yi tana murmushi tace, " Na haƙura Ayaman, kada ka ƙara rashin kunya ba kyau, ka ji ko?" Taso wa ya yi da gudu ya ƙarasa gareta ya rugumeta yace, "Eh! Ummana na ji bazan ƙara ba insha Allah." Itama rugumesa ta yi ta ce, "Yauwa yaron kirki Allah ya yi muku albarka."
    
     "Ameen Ya Allah, Umma yanzu zan iya fita?"
   
    "Eh! Zaka iya fita amma kada kayi rashin ji."
   
    "Ba zaki ji ba Umma."
   
    Yana gama faɗin haka ya fice a ɗakin da gudu yana murna. Murmushi kawai tayi a cikin ranta tace,  _Allah ya shirya mana ku._
   
        Yana sauka yaci karo da su zasu shigo falon, da mamaki suka tsaya suna kallansa, murmushi yayi musu yace, "Oyoyo! Yaya an dawo lafiya?"

             "Lafiya ƙalau Ayman."

           "Yaya ina tsarabata?"
   
          Miƙa masa laida ya yi yace, "Gata."
   
           "Na gode sosai Yayan mu."
   
       Shigo suka yi shima ya biyo bayansu, yana cewa, "Umma kinga tsarabata da Yaya ya bani min."
   
    "Inyye! Na tayaka murna."
   
    "Fatan dai ka yi masa godiya?"
   
    "Eh! Na yi masa."
   
    "Anya! Ka yi masa kuwa"
   
    "Allah na yi masa, Yaya ai dai na yi maka haka ko?"
   
       "Eh! Ka yi min."
   
    "Kin ji ko Umma? Na yi masa."
   
      "Na yarda yanzu."
   
    Dariya suka yiwa Ayman ganin yadda ya canja lokaci ɗaya, zama suka yi take tambayarsa ya Hajiya yake, ya shaida mata tana lafiya ƙalau da sakon godiya da  gaisuwa da ta ba da, ta ji daɗi sosai har sai da farin cikin ya bayyana.
   
    Kamar daga sama suka ji Aymana na cewa, "Umma ina Yaya zai je?"
   
    "Tambayesa kiji Aymana tun da gashi nan a kusa dake."
   
    Juyawa ta yi ta kalle sa tace, "Yaya ina zaka ka bar mu?"
   
     "Aymanata karatu zan tafi yi."
   
      "A ina Yaya?"
   
       "Wajen."
  
      "Waje kamar ya Yaya?"

     "Ƙasar wajen nake nufi."
   
    "Amma Yaya me yasa ba zaka zauna ka yi nan ba?"
   
          "Aymanata can sai yafi yi min sauƙi, inna zauna a nan zan ɗauki dogon lokacin kafin na cika burina."

       "Yaya menene burinka?"

        "Na zama litita."

    Zato ido tayi tace, "Amma dai ba zaka ringa yi mana allura ba ko?"
   
     "Hhhh!" Dariya ya yi sosai dan tambayarta ta bashi dariya yace, "Eh! Ba zan ringa yi muku ba."
   
    "To..! Yaushe zaka tafi?"
   
    "Juma'a ta sama insha Allah."
   
    "To..! Yaya wace ƙasa zaka tafi?"
   
     "Indiya Insha Allah."
   
      "Kuma Yaya...."
   
    Dakarar da ita yayi yace, "Dan Allah Aymana kiyi haƙuri da wannan tambayo yin naki, bari Daddy ya dawo sai ki tambayesa shi yasa komai ni ban sani ba."
   
    Dariya sosai Umma ke musu, sanin halin Aymana da tayi da ƴar banzar tambayar da bata da ƙarshe, yasa ta dakatar da ita tun da farko.

      Shima dariyar yayi, ita kuwa gwanar bata so haka ba kawai tayi shirune dan ba yadda zata yi, kamota yayi yace, "Ƴar ƙanwata amman dai ƴar jarida zaki zama ko?"

      Dariya tayi sobada an taɓo mata inda yake mata ƙaiƙayi tace, "Eh! Yaya ina san na zama ƴar jarina ina girma."

        "To..! Shikenan sai ki maida hankali a karatunki, indai kina son zama cikakkiyar ƴar jarida."

       "Insha Allah! Yaya zan dage don nima na cika burina, kamar yadda kaima zaka cika naka a yanzu."

        "Yauwa! Aymanata Allah ya taimaka."

       Su duka suka amsa da, "Ameen Ya Allah."

      "Kai Ayman me kake zan zama?"

      "Yaya nima ban sani ba yanzu sai na ƙara girma zan zaɓa."

     "To..! Ayman ɗin na Allah ya raya mana ku."

    Suka kuma amsawa da, "Ameen Ya Allah."
   
        Hira suka shiga yi cikin nishaɗi da annashuwa, sai da suka jima suna hira sannan aka kira sallar magriba kowa ya tashi yaje ya gabatar da sallah. Abdallah yayiwa Umma sallama dan daga masallaci zai wuce wani wajen, tayi masa fatan alkhairi  ya fice yana jin daɗi a ransa.
   
   
   
   
              _*<<<<<~•~>>>>>*_
    
   
         Safa da marwa kawai yake yi, duk hankalinsa yabi ya tashi gumine keta tsatsafo masa, idan ya gaji sai ya haɗa kansa da bango yayi shiru, lokaci ɗaya ya fita a hayyacinsa.
   
       Kallansa kawai Safna take yi, gaba ɗaya kanta ya ɗaure, ta kasa gane ainahin abinda ke faruwa, tambayoyine barkatai dake yawo a cikin kanta game da Yassar da yarinyar da suka taikamawa, ko tantama babu akwai wata alaƙa a tsakanin, dan duk kan alamu sun bayyar da haka, gani ba damar da zata tambayesa ko ya san yarinyar, yasa ta kama bakinta tayi shiru dan ta san halin kayanta.
   
       Dr. Ne ya fito ya doso ina suke, tun kan ya buɗe baki yace wani abu Yassar yace, "Dr ya take? Fatan dai tana lafiya ƙalau babu abinda ya sameta?"
   
        "Ka kwantar da hankalin zo muje office sai muyi maganar a can."
   
        Bin bayansa suka yi har zuwa office ɗin Dr. Ɗin zama ya yi suma ya yi musu nuni da su zauna, sanna ya fara magana, "Malam wannan yarinyar wacece a wajenka?"
   
        Tafe kansa yayi ya kalli Safna ta ke gefensa, itama kallansa take yi tana jiran jin mai zai ce. Juyowa yayi yace, "Dr. Ban san ta ba." Nan ya kwashe labarin yadda aka yi suka haɗu da yarinyar har suka kawota asibitin ya basa.
   
        "Hmm!" Dogon nufashi Dr. Ya ja sannan yace, "A gaskiya yarinyar nan tana cikin halin ha'ulayi, tana buƙatar taimakon gaggawa, a binciken da mu ka yi mata mun gano an yi mata Fyaɗe, kuma an ji mata ciwo sosai sakamako ƙanƙarar da ta yi da yawa, akwai buƙatar ayi mata aiki, sannan kuma a akwai tsofafin gocewar kashi a gwiwar hannuwanta da targade a yatsun ƙafarta, ga kuma farfashewar da gwiwoyin ƙafafuwanta. Muna buƙatar wani nata ya tsaya mata, sannan sai mu fara mata aiki da dace da ita."
   
        "Dr. Zan tsaya mata, Wallahi ko rayuwata kuka ce na ba da ku dasa mata zan baku a dasa mata."
   
        Girgiza kai Dr. Yayi yace, "Baka tsoron wani abu ya biyo baya a kan haka?"
   
        "Bana tsoro Dr. Dan Allah ku tashi kije ku yi mata duk abinda ya dace a yi mata, komai tsadar sa zan biya."
   
        "To..! Amma yanzu dai kafin mu fara mata wani abu, muna buƙatar sa hannuka dan ka da wani abu ya ɓullo daga baya mu shiga ciki."
   
        "Ba damu bani na sa."
   
      Wata takarda ya miƙo mata da biro yace, "A nan zaka sa hannun."
   
       Karba yayi zai sa hannu Safna da ta gama ruɗewa ta riƙe hannusa tace, "Yanzu ka yarda ka shiga matsalar da baka san menene silar ta ba? Baka tsoron wani abu ya biyo baya ka shiga matsala? Dan Allah ko ba zaka yi tunani akan kowa ba ka yi tunani a kaina da ɗan dake cikina, yanzu idan wani abu ya sameka ya zamu yi?"
   
       "Kiyi haƙuri Safna ba zan iya ƙyale wannan yariyar ba cikin halin da take ba, Wallahi a yadda nake ji a game da ita zan iya rasa komai akanta, dan Allah ki fahimce ni, indai ban taimakawa wannan yarinyar ba, to ba zan taɓa samun nutsuwa ba a cikin raina ba."
   
        Ba yadda ta iya ta saki hannusa ba ta ce masa komai ba, ta share ƙwallar da yake zubowa kawai, dan kalamansa sun girgiza mata zuciya, a cikin ranta take tambayar kanta, _Shin wai wacece wannan yarinyar da har Yassar yake jin zai iya rasa komai akan ta?_ Shi kuma ganin ta sakar masa hannunsa, yasa ya saka hannun da Dr. Ke buƙata ya miƙa masa takarda yace, "Dr. Sai me kuke buƙatar?"
   
       "Ka cike file kawai."
   
        "To..! Miƙo min."
   
       Miƙa masa yayi ya cike ya miƙa masa, dubawa yayi ya ga ya cike komai ban da abu ɗaya yace, "Yassar baka saka sunan yarinyar ba?"
   
        "Ban san sunanta ba."
   
        "To..! Taya zamu tsaya mu jajirce wajen dubata baka ba mu sunanta?"
   
       Ji ya yi kamar ya ɗauke Dr. Da mari a ransa yace, _Kamar ba yanzu nan na gaya masa cewa ban ba taimaka mata kawai na yi, ta ya zai san sunanta bacin ban san ko wacece ita ba._
   
       Karɓar file ɗin ya yi bai ce masa komai ba ya saka suna yace, "Sai ka tashi ka je ku dubata na cike duk wani abinda kuka buƙata, amma kuma Wallahi kuka bari wani abu ya sameta, sai na yi ƙara ku nasa an rufe muku asibitin da kuke takama dashi, kuke yin yadda kuke so."
   
        A je file ɗin Dr. Yayi ya fita cikin gaggawa jin furucin da Yassar yayi masa, dan ya lura da alama babban mutum ne zai iya aikata komai.
   
       "Honey wane suna ka saka mata bacin baka santa ba?"
   
        "Karki damu, sunan mafi soyuwa a wajena na saka mata."
   
        Kin mamaki tace, "Wane suna?"
   
       "Yasmeen Abubukar Ishaq."
   
       A razane ta kallesa ta tace, "Wacece Yasmeen?"
   
       Cikin murya mai kama da ta kuka yace, "Yasmeen itace wacce nafi so a duniyar nan, Yasmeen ƙanwata ce ta jini uwa ɗaya uba ɗaya, Yasmeen rayuwatace, Yasmeen farin cikina ce, Wallahi Safna Yasmeen itace komai nawa." Ya ƙarashe maganar yana goge hawaye.
   
       "Dama kana da ƙanwa baka taɓa gaya min ba?"
   
       "Taya zan faɗa miki bacin nima ban san a inda zan gan su ba ita da Ummana, sun bace min a cikin duniyata..." Ya ƙarashe maganar yana kuka.
   
        "Amma ya yakamata ka gaya min nifa matarka ce."
   
       "Hmm! Ke matatace amma ko da sau ɗaya kin taɓa tambayata, me yasa ba na dariya? Ba na nishaɗi? Ba na walwala da annashuwa a cikin rayuwata? Baki taɓa ba to taya ni zan gaya miki abinda ko a cikin mafarki ba na fatan ya zo min a matsayin tunani, abin baƙin ciki ma ko kammanin Ummata bana iya tunawa ballantana ma na iya tuna a wane wajen suke, soyayyar suce kawai ba ta gushe a ciki cikin zuciyata ba, ta ya kike tunani zan iya fesar da kalaman da suka kasace kamar gubane a gare ni?"
   
   
       Yana gama faɗin haka ya fice a office ɗin ya barta a nan tana kuka, wanda shi a ganinsa na jin daɗi take yi, dama zai samu damar yin kukan da take yi da ya more.....
   
   
   
        _Ku yi haƙuri da wannan ba na  jin daɗi ne daurewa kawai na yi, na yi muku shi ganin kuna nemansa.👏🏻_
   

   
_*See me next page✍🏻*_
_*Share*_
_*Comment*_
_*#JannatMN*_   

 
   
  

*©JANNAT M. NASIR•*

Continue Reading

You'll Also Like

15.6K 609 41
Debut in Interstellar After Retiring as Grim Reaper author: ailespeak genre: BL, Fantasy, Psychological Qin An was a former senior grim reaper who re...
84.9K 8.3K 53
Nandini Verma was 18 when she penned her first story, a tale of passion, betrayal, and revenge. It was a masterpiece, poised for publication. But on...
21.2K 1.6K 33
"Say it. Say you hate me. Say you want to leave. But remember-no one will ever touch you like I do. No one will ever love you the way I do" "I hate y...
166K 1.5K 175
δ½œθ€…οΌšζ‘ι‡Œηš„ε°ε‚²ε¨‡ Chen Xiaolin accidentally bleeds on the bracelet her grandmother left her, and she discovers a space inside. She then fills the space with...