Page 10&11✍🏻

105 5 0
                                    

YASMEEN.



*_Story & writing_*
*_by_*
*_Jannat mn(Real takowah)_*

*Wattpad_@Realtakowa*

*_Dedicated to my sister_*

________________________________

*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com

_*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM*_


_*01 March , 2020😍*_

_*RIBACI RAYUWARKA DA AYYUKAN ALKHAIRI*_

_*•Ka k'ara zage damtse wajen ganin ka ninninka ayyukan alkhairi a wannan rayuwa ta duniya, domin itace kad'ai mafita ga rayuwar tabbas ta gobe alk'iyama.*_

_*•Kasancewa cikin ayyukan alkhairi da wuraren da ake aikata alkhairi, tare kuma da aikata alkhairin gami da yi don Allah shine ke datar da bawa duniya da lahira.*_

_*•Don haka kada ka raina aikin alkhairi komi k'ank'antarsa ribace shi kaga ka fa'idantu da shi, sai ka samu guzuri mai tsoka da zai taimake ka ranar da zinari da azurfa ba sa anfani, sai wannan kyawawan ayyukan ne kad'ai zasu yi anfani.*_

_*•Allah ya ba mu ikon aikata alkhairi a dukkan tsawon rayuwar mu ta wannan duniya, ya ba mu ikon tuba daga zunubanmu, ya kuma sanya mu daga cikin bayin sa nagari.*_

*ALLAH YASA MU DACE. AMEEN YA ALLA👏🏻*

_*Page 10&11✍*_

_________Bud'a baki sukayi da niyar zasuyi magana amma ya dagatar dasu ya hade fuska yace,

"Kada kuce zaku yi min godiya inba haka yanzun nan rayukanku zasu b'aci......"

"Toh..! Ayi mana afuwa Dady insha Allah bazamuyi maka godiya ba"

"Yauwa Allah yayi muku albarka"

"Ameen ya Allah"

"Abu na biyu da zan fad'a muku shine, yanzu nasan kun mallaki hankalin kanku kunsan maike muku ciwo da kuma abinda ya kamata, dan haka nake so nan da wani lokaci kuma ku aje naku iyalan, nima naga 'yan jikina.........."

Murmushi suka yi gaba d'ayansu harda shi daddyn Nabil ne yace,

"Insha Allah daddy sai ma ka aurar da su bama ganinsu ba."

Wannan karon dariya daddy yayi saboda maganar Nabil ta bashi dariya, suma su Yassar sai da suka dara.

"Allah yasa to, amma ni ai bani da matsala da Kabir da Yassar, saboda su ina so na had'asu da k'annensu, amma bazan takura muku ba in kuna da wad'anda kuke so sai ku fad'amin."

Batare da wata gardama ba suka nuna amincewarsu akan zancen cikin farin ciki, gaba d'aya sunyi farin ciki da wannan had'in da daddy yake so yayi.

"Gaskiya nayi farin ciki da amincewarku, insha Allah su Safrat da Safnat suna kammala karatu sai ayi auran, kai kuma Nabil sai je ka dai daita da Fadwa 'yar wajen gwaggonka."

Shima amsawa yayi cikin fari cikin da girmamawa ya amince da had'inshi da Fadwa 'yar gidan gwaggonsa.

Abinda Dady bai sani ba shine, tun Nabil na secondary school a lokacin tana yarinya yake san Fadwa,

Amma bai tab'amin nunawa ba koda da wasane, ya binne san da yake mata a cikin zuciyashi, yanzu da yaji Dadyn shi ya zama mishi ita a matsyi matar aurenѕa har akace yaje su daidaita,

YASMEEN.Место, где живут истории. Откройте их для себя