Page 27&28✍🏻

26 1 2
                                    

*༺•⚘🌺YᎪᏚᎷᎬᎬN🌺⚘•༻*
             *1442H/2020M.*

   
 

®☄
*GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍*
_{Gaskiya ɗaya ce daga ƙinta sai ɓata, burinmu mu faɗakar da al'umma domin ribantar duniya da kuma lahira.}_

         '''🎐G•W•A🎐'''
*_GASKIYA DOKIN ƘARFE•_*🏇🏼


*NA MARUBUCIYA:-*
*JANNAT M. NASIR✍🏼*
*Wattpad_@JannatMN*

*SADAUKARWA GA:-*
*MY BLOOD SISTER*
*MARYAM M. NASIR (MANAB ƳAR BABA)*

Wattpad:- *GaskiyaWritersAsso.*
Gmail:-gakiyawritersassociation@gmail.com
Youtube Channel:- *GASKIYA 24TV.*
Facebook page:- https://www.facebook.com/Dokinkarfe2019/
Bakandamiya:-
*GASKIYA WRITER'S ASSOCIATION.*

   
           *😭KUKAN KURCIYA.....🕊(8)* 

        _*Ƴan uwa ni'ima tana buƙatar godiya. Musiba tana buƙatar haƙuri. Zunubi yana buƙatar Tuba (Istigfari). Duk wanda ya yi godiya, ya yi haƙuri ya kuma tuba haƙiƙa ya samu jin daɗi....Allah ya jiyar damu daɗi duniya da lahira...Allahumma Amin. Allah yasa mu dace. Ameen Ya Allah 👏🏻*_

      _Wannan shafi tukwici ne a gareki Ummu Haidar fan's ɗin ƙwarai. Ina godiya da kulawarki ga novel ɗin Yasmeen. Ki yi komai ba komai bane a wajena, wannan shafin naki ne halak malak gaba ɗaya shi._

*SHAFI NA 27-28📑*

    
*__________📖* Da biyu Fadwa ta yiwa Safrat haka tunda ta hanata bin Safnat ta tsokaneta, shiyasa ta yi mata haka dan ta tada mata da hankali. Tana shiga gidanta ta kulle ƙofar da mukulli ta hayewarta sama tayi kwanciyarta.
  
    
        Da saurinta ta ƙara so gidan Fadwa ta kama kofa zata buɗe ta shiga ta ji ƙofa a garƙame, hankalin Safrat in yayi dubu ya tashi da kulle ƙofar da Fadwa ta yi, dafe kanta tayi a ranta ta rinƙa cewa, _Na tabbata Fadwa fushi tayi, yau naga ta kaina, ta ya zan fahimtar da ita ba haka nake nufi ba._ Safnat ce ta faɗo mata a rai aiko da sauri ta kuma juyawa inda ta fito.

        Ɗakinta ta nufa ta tura ƙofar bakinta ɗauke da sallama ta shiga, bata ɗaugo ta kalleta ba ta amsa mata sallama, ƙarasowa tayi har inda take kwance ta zaune gefen gadon tace,

        "Sister ki taimaka min Fadwa tayi min bahuguwar fahimta, ranta ya ɓaci ta fita tana fushi na bi bayanta na fahimtar da ita, sai na tarar da ta kulle gidanta."

        Tashi tayi daga kwancen da tayi ta kalli Safrat fuskarta ɗauke da murmushi ta ce,

       "Haba! Safrat kamar baki san wacece Fadwa ba, amma gaskiya kin ban mamaki da kika manta wacece Fadwa, sanin kanki ne ba'a ɓatawa Fadwa rai, ballantana ma tayi fushi, sai dai ta ɓata ran wasu tasa wasu yin fushi, yanzu me kika yi mata har ranta ya ɓaci tayi fushi?"

    
     Nan ta kwashe duk abinda ya faru a tsakaninsu ta gaya mata, dariya sosai Safnat tayi har sai da taga Safrat ta fara ƙulewa sannan ta daina dariyar tace,   
  

       "Wallahi Safrat har yanzu baki gama sanin wacece Fadwa ba duk shirin da kuke yi da ita, ba fushi take ba kuma ranta bai ɓaci ba sam, ta gaya miki haka ne dan ta ɗaga miki hankali, tunda kin hanata yin abinda tayi niyya da biyu ta gaya miki haka, inda har ranta ya ɓaci da gaske ba zata kulle ƙofar gidanta ba, ta san dole zaki biyo bayanta ki bata haƙuri, shiyasa ta ƙulle ƙofa dan ta ƙara tayar miki da hankali, yanzu haka tana can tayi kwanciyarta ko tana karance-karancenta ke kuma ta barki cikin damuwa, ki rabu da ita kawai, da kanta zaki ga ta fito tazo har nan, kuma ta tsokaneki."  
   
     
      Ran Safrat ne ya ɓaci da ta tuna ko wacece Fadwa tace, "Amma gaskiya Sister Fadwa ta cini wannan wasa kuma wallahi ba zan haƙura ba sai na rama."   
   

YASMEEN.Where stories live. Discover now