YASMEEN.

By JannatMN

1.2K 63 13

Labari ne da ya k'unshi abubuwan ban mamaki kama daga kan:-Hak'uri, juriyar, tausayi, soyayya, yaudara, cin... More

Page 2✍️
Page 3✍️
Page 4&5✍🏻
Page 6&7✍🏻
Page 8&9✍🏻
Page 10&11✍🏻
Page 12&13✍🏻
Page 14&15✍🏻
Page 16&17✍🏻
Page 18&19✍🏻
Page 20&21✍🏻
Page 22&23✍🏻
Page 24&25✍🏻
Page 26&27✍🏻
Page 27&28✍🏻
Page 29-30✍🏼
Page 31-32✍🏼

Page 1 ✍🏻

429 14 2
By JannatMN

YASMEEN.



*_Story & writing_*
          *_by_*
*_Jannat mn(Real takowah)_*

*Wattpad_@Realtakowa*

*_Dedicated to my sister_*
     

________________________________

*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________

https://www.facebook.com/104534761033461/posts/119016616251942/?app=fbl

   _*Alhamdullilah Allah na gode maka daka bini ikon rubuta wannan littafin nawa, mai cike da dunbin darusa a cikisa, wanda inhar kuna tare dani xaku tsinci darusa da ke tattare da wannan littafin nawa . Kafin mu tsinduma a cikin wannan littafin ina son ku san mai wannan littafin KOMAI NISAN JIFA...! ya kunshi, toh dai wannan littafin KOMAI NISAN JIFA....! ya kunshi abubuwa kama daga kan:- HAKURI,  JURIYAH, TAUSAYI,  SOYAYYAH,  YAUDARA, CIN  AMANAH, SAN  XUCIYAH, GA UWA UBA MAKIRCI  DA DANA SANI, dadai sauransu inhar kuna biye dani xaku jisu yadda wannan ruguntsumin ya faru. Ina rokan  Allah ya bani ikon gama wannan littafin kamar yadda na fara lafiya👏🏻.*_

_*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM*_

       *1st January, 2020😍*

           
_*Page 1 ✍🏻*_

____Cikin fushi ta d'aga hannunta ta wanke yarinyar da zafafan mari har guda biyu, wanda k'arfin marin saida yasa ta duka bakinta ya fashe jini yafara fita daga....,

Yarinya ce k'arama wanda bazata hauwara shekara goma ba, kyakyawa ta ajin k'arshe, farace sosai amma ba irin marar kyan nan ba, dan wani lokacin har wani ja zakaga tanayi soboda tsabar fari, fuskan nan tata daidai da ita tanada manyan idanuwa irin basu jan hankalin mai kallansu, daka ganta kaga jini fulanice.

"Ke wace iriyar jakace dan ubanki a garinku haka ake wanki ko haka uwarki ta koya miki kafin ta gudu ta shiga yawan duniyar.....?, maxa ki tashi kije ki cire wannan uniform din dake jikinki ki sake wanke min kayan nan, sannan saiki xo ki tafi yawon iskancin da kika saba."

"Dan ni wallahi banga amfanin zuwanki wannan makarantar ba, banda iskanci babu abinda kike koda yake bazanyi mamaki ba tunda gado kukayi keda dan uwanki wajen shegiyar uwarku, gashi yanxu daga uwar taku har d'an uwan naki ba'asan ida suka shiga ba,  sun shiga xuciya  ni wallahi har k'okwanto nake anya ku 'ya'yan malamne ma kuwa,"

"bazaki tashi ba saina sa k'afa na tattakaki, kika tsaya kina sauraron abinda nake fad'a wato ga mahaukaciya ko...., "  

D'agowa tayi tare da dafe bakinta da kuncinta, hawaye ke bin kuncinnata d'aya bayan d'aya bude baki tayi ta fara magana bakinta na rawa cikin murya kuka tace "d'an Allah Mama kiyi hakuri wallahi ba...."

bata karasa ba taji an buge mata baki sai da ta saki wata irin gigitaciyar kara, tsaye yake akanta ya dunk'ule hannunsa wada ya buge mata baki dashi,

"Zaki bar wajen nan ko sai nasa kafa nayi boll dake.....indan kika sake kika kara kallona da wadannan gwandara² idanun nan naki saina kwak'ule miki su mujiya kawai...."

Tashi tayi dana kuka fuskar nan tata duk tayi ja saboda tsabar kuka, shiga d'aki tayi ta nufi wata tabar ma wanda duk ta zazzare da ita da babu duk d'aya.

Tana kuka ta fara cire uniform din dake jikina,

bakomai ne yake sata kuka ba face rashin zuwa ta tahfiz din daxatayi yau gashi harda za'a karbar musu.

Dan zagin da duka da Mama take mata da cin mutunci harta saba dasu tun tanaji haushi da takaici harta daina.....,

Kuma gashi malaminsu Malam Rabi'u bashi da mutunci kokad'an, zane ta zaiyi babu ruwansa da tsayawa jin wani uzurinta.

Dan baxata tab'a mantawa da wata rana da Mama ta tsaida ita tayi shara ta makara ba karamin duka yayi mata ba har sai da takaiga da kyar take iya d'aga hannunta,

sannan yace mata "duk ranar da tasan ta makara kada ta kara zuwa tayi zamanta," duk da shiyasace ta zauna amma intaje washegari sai yayi mata dukan fashi saboda....., 

Shiyasa ma yanxu inta makara sai dai ta tafi wajen Yayah Ahmad ya koya mata karatun...., 

Jawo wata bako tayi ta zaro wata shegiyar riga duk tayi wani fari tsabar kodewar da tayi ta saka,

sannan ta d'auki kayan ta fita tana kuka ta fara wanke wa kamar yadda Mama ta umarceta......

"yauwa Jafar Allah yayi maka albarka kayi min daidai, inajin da baka buge mata wancen shegen bakinnata ba da zagina xatayi...." 

"Dallah Mama kiyi shiru wallahi duk laifinki ne ai sai da nace miki a koreta itama daga gidan man, amma kika wani ce aa toh ai gashinan na tabbata kika cigaba da zama da ita wata rana sai tasa wuka tayankaki kowa ya huta kuma wallahi ni babu ruwana...."

"haba d'an albarka kayi hakuri komai ya kusa zuwa k'arshe kada ranka ya b'aci ka saki ranka kaji ko yaron kirki, akwai abinda nake jirane sai munbi komai a hankali ita wannan ba kamar sauran bace shiyasa....kaji ko yarona."

"Ba wani nan Mama kedai kawai kice kina santa ne, ai tunda muka iya cin nasara akan uwarta Kubrah tofa wannan yarinyar baxata gagaremu ba, kodai Mama harkin manta wacece Kubarah ne?  ita kumafa yarinyace sosai duk² bata wuce shekara 10 bafa wai kice tagagaremu gaskiya bazaiyu, yakamata ki d'auki mataki akai dani wallahi bazan zauna ina had'a inuwa d'aya da wannan yarinyar ba nima tafiyata zanyi na barki kamar yanda kanina yayi....."

dum² taji gabanta ya fadi zuciyarta ta fara bugawa da k'arfi takiyanke ta riga tuno d'anta abin santa Kabeer duk son da takeyi yiwa Jafar da Adam baikai wanda takewa Kabeer,

kuma takasa sanar dasu gaskiyar lamari  akan d'an uwansu....,

Wallahi boka ka cuceni daka rabani d'ana yanzu yazanyi idan narasa Jafar shima.

Kai wlh bazai yuba dole ki bar gidan nan Yasmeen,

koda xanyi yawo tsirara saina rabaki da gidan nan wallahi wannan alkawar na dauka....

dole gobe naje na samin jummai akan wannan maganar musan ya zamu b'ulo mata....,

Murmushi yak'e ta saki sannan tace "yanzu Jafar harkana iya tunani tafiya kabarni? haba yarona kasan bazan iya rabuwa dakai ba, amma gashi kai kana tunani rabuwa dani ko, kayi hakuri indai akan waccen shegiyar yarinyar ce nayi maka alkawarin saita bar gidan nan kusa bada jimawa ba, kuma bazata tab'a dawowa ba kaji yarona ka kwantar da hankalinka, ai kasan koh wacece Mamaka?"

Dariya yayi "yace gaskiya Mama ba bakida mutunci ko kadan nasan wannan kad'an ne daga cikin abinda zaki iya aikawata, zan baki lokaci amma fa idan kika wuce babu abinda zai hanani tafiyata......"

hhhhhh! itama dariya tayi tace "wallahi kaima Jafar ba k'aramin hatsabibi bane kai, dan kama fini had'a indai wannan ba damuwa gobe zanje gidan jummai mutattauna ta yarda xamu b'ulowa lamarin."

"hhhhhh! wokee Mama zan zauna ina mai tsumayen jin labari mai dadi..."

"Toh..! Mama nidai zan fita"

"Harka fito Adam?"

"Eh! Mama na fito..."

"Toh..! Shikenan saika dawo, amma fa kada ka manta yau duk inda zaka nemo min kud'i ka nemo ka kawo min kaji koh"

Hhhhhhh! "kefa Mama maiyar kud'i ce wato ma duk duk inda xa'a nemo miki kud'i a nemo akawo miki koh tom kada ki damu...., koh kin manta wanene danki koh? Baki san waye Adam ba kenan?"

"Kajini da ja'iri taya zan manta suwaye yarana,  bacin na san Allah ya azurtani da jaruman yara masu nemo nakansu koh ta halin yaya, taya zan manta?"

Hhhhhh! Dariya sukayi tare da tabawa sannan Adam yace "Shiyasa muke sanki Mama ke kadaice kike yaba halinmu, kaf fadin gari nan zagin mu akeyi wai bama da tarbiya"

Jafar ne ya cabe da cewa "ai bama kisan wani abuba Mama, wai naje wajen wata yarinya babanta yace kada na kara zuwa k'ofar gidansa,  wai shi baya gayyar marassa tarbiya gidansa, na kuma komawa washegari daya fito ya gani ya daukeni da mari sannan ya koreni, aikoh ranan yayi hanyar yamma dama kinsan babu mutane a tawajen, nida abokaina muka tare masa hanya mukayi mushi dukan tsiya muka barshi nan a yashe mukayi tafiyarmu abinmu, yanxu haka yana can kwance sai jinya yake ko k'ofar gidannasa dayake tak'ama dashi baya iya zuwa. "

"Allah yayi maka albarka Jafar,  kayi min daidai wallahi ina goyan bayanku duk shegen da ya taka ku kuma ku takasa, kunji ni koh?"

"Eh! Munji"

"Yauwa yaran kirki, ai saika wuce ka tafi bance ka ragama kowa ba, kajini koh?"

"Uhmm naji"

Hanyar waje yayi zai fita yana zuwa gab da k'ofar futa yayi daidai da lokacin data kwaro ruwan da tayi wanki dasu, aiko sai akan k'afarsa sannan ya fallatsar masa akan k'afar wandonsa harya jik'a masa....

A fusace yayi kanta ya d'auke ta da kakkauran mari,  ta tafi zata fadi ya damk'ota  ya had'ata kanta da bango sannan ya damk'i yalwataccen gashin kanata....

_See me next page✍🏻_

*Vote*
*Like*
*Comment*
_*#Realtakowa*_️

Continue Reading

You'll Also Like

69.4K 1.8K 67
"mom, dad, Im married!" lahat ng relatives namin ay nagulat sa announcment ko. Sino ba naman kasi ang mag aakala na ang unica ija ng pamilyang Letpr...
246K 7.3K 59
I could say this is one clichΓ© story. A college girl died and transmigrated into an otome game she once played. Unfortunately she becomes the villain...
1M 42.8K 90
Kenta Bernard, a seventeen-year-old, died of leukemia in the hospital and was reincarnated in a novel that he has yet to finish. He is the ill second...