K'AREENATEEY

By 13deeja

31K 1K 114

It's All about friendship More

001-005
006-010
011-015
016-020
21-25
26-30
31-35
8
9
10
11
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
23
24
25
26
27
22
23
25
28
29
30
31
32
33
34
35
36
38

37

931 23 2
By 13deeja


    
    ♥ ❤
           
         ♥♥❤
*~K'AREENATEEY~*
(K'AWATA)

(It's all about friendship)

الدعاء اذا تقلب ليلا

Addaua iza takallaba lailan

                           ADDUAR YAYINDA MUTUN YA FARKA MAANA YAJUYA ACIKIN BARCINSA

لا إله إلا الله الواحد القهار رب السموات والأرض وما بينهما العزيز الغفار

La iha illahul wahidul kahhar rabbussamawati wama baynahuma alazizulgaffar

                              BABU ABUN BAUTAWA DAGASKIYA SE ALLAH MAKADAICI MARINJAYI UBANGIJIN SAMMAI DA QASSAI DA ABINDA KE TSAKANINSU MABUWAYI ME YAWAN GAFARA

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

*~✍🏽✍🏽GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION✍🏽✍🏽~*

*~We are bearer's of so golden pen🖊~*

*~we write assidiously perceive no pain~.*

*~So magical,Our creative golden pen✍,behold our words.~*

*~A product of our pen🖊,savour our words, for it will cause you no pain.~*

*written *✍
       -by-
         *Deeja one love*

Wattpad 13deeja.

Daga wannan page d'in har zuwa k'arshe sadaukarwa ne gare ki *AISHATU BABAYO* saboda kaunar da kike wa *GOLDEN PEN WRITERS* ba muda abinda zamu biya ki dashi, dan haka *K'AREENATEEY* har zuwa k'arshe ya zama naki sis kiyi yadda kike so dashi, *ONE LOVE* ta baki wannan yan shafukan har zuwa karshe,  muna godiya sosai da irin kaunar da kike mana.

*_37_*

  Kamar wanda aka tsikara sai kuma Yaya Al'ameen ya nufi wajen Yaya Khaleel,ɗago shi yake ƙoƙarin yi amma ya kasa hakan yasa ya nemi taimako daga Yaya Abdus-samad,shima sai lokacin ya iya nufar ɗan uwan nashi da sauri suka ɗauke shi sai asobiti,dan ma tsakanin su babu nisa sosai.

    Be wani jima ba ya farfaɗo,ai fa nan ya sake haukace musu,Yaya Al'ameen yace"ka kwantar da hankalin ka mana".
   
  Idanu jajur ya kalle shi yace"in kwantar da hankali na fa kace?,mata ta da wani ƙaton",Yaya Al'ameen yace"haba K.A kada ka bari zargi ya shiga tsakanin ku mana".

   Maida idanun shi yayi ya lumshe cikin kunar rai yace"karuwa ce dama!",Yaya Abdus-samad ya buɗe baki a karo na farko yace"haba my man ba dai karuwa ba ni ina ganin da wani abu a ƙasa".

   "babu wani kare ta da zaka yi Abdus-samad domin kuwa kai kanka kasan a ɗan kwanakin nan ta canza da yawa".

   Sosai suka dinga tattaunawa akan matsalar har likitocin suka sallame shi,babu yadda Abdus-samad be yi dashi ba amma yaƙi yarda hakan yasa kawai ya ƙyale shi.

****   ******   ******
Ni kuwa ina can gida ina faman jiran kiran nashi,haka har barci ya ɗauke ni,sosai na dinga mamakin yadda be kira ɗin ba da safe.

  Har na shirya na tafi makaranta yau 12-2 sai 4-6 haka muka fito duka amma ina tunanin meya hana shi kira gashi ban san me yasa yanzu na damu dashi ɗin sosai harma ya zarce shirin mu na farko.

   "Buddy kina jina kuwa",cewar Jabeer kenan a lokacin da zai maida ni gida,"me kace ne?",na tambaya.

   Cikin kulawa nace"kaga Yaya Khaleel ne yace zai kira ni tun jiya har yau kuma shiru",wani yawu me ɗaci ya haɗiya sannan yace"hmmm!may be aiki ne yayi mishi yawa har ya manta".

   "amma duk wani aiki baya mantar da Yaya Khaleel wani abu daya shafe ni haka ya faɗa mini kuma nima naga hakan",a ɗan hasale yace"to yau ya nuna miki halin maza",shiru nayi bance komai ba domin maganar ta bani haushi shima kuma na san haushi yake ji.

   Koda ya sauke ni be tsaya ba ya juya nima kuma taɓe baki nayi sannan na shige gidan,Ummi tana shara da sauri na amsa na ƙarasa mata.

   "ah yau Mama hankalin ya dawo kenan",ta tsokane ni,ni kuwa murmushi kawai nayi bance komai ba.

   Abdul'azeez ya shigo hannun shi riƙe da takarda,cikin sauri na miƙe na tare shi ina faɗin"Sweet me yake faruwa ne?".

   A ɗan tsorace yake dani dan akwai ranar dana kusa marin shi tun daga nan ya fita daga harka ta.

  Miƙo mini yayi yace"appeal ne tare da addmission letter,kallon saman takardar nayi nace" BUK! zaka tafi kai kuma?".

  Ɗaga mini kai yayi domin tabbatarwa,aikuwa na fashe da dariya sannan nace"kai Sweet mu da muke da sardauna amma shine zaka tsallake ka tafi wani uwa garin?".

   "to sardaunan ya ƙi ni ba sai inje inda aka so ni ba",girgiza kai kawai nayi sannan nace"lallai Ammie tana da baƙo".

   Ummi tace"abinda nake fama dashi kenan yaje wajen ta ya zauna amma yace wai shi yafi son ya samu hostel".

   "to meye aibun wajen ta Sweet kaji kawai kaje wajen ta tunda babu nisa sosai kuma kaga hakan yafi maka rufin asiri".

   Sun yi mamaki na sosai domin yadda a ɗan kwanakin baya na zubar da komai na gida amma yanzu wai nice harda yiwa wani nasiha.

  Haka kuwa nayi ta rarrashin shi har ya yarda zai zauna a gidan,nan kuma na koma tsokanar shi ina ce mishi bakano.

   Ranar dai da farin ciki suka kwana yayin da ni kuma da akasin haka dan kuwa har lokacin Yaya Khaleel be kira ba kuma na kira wayar shi a kashe.

  Washe gari ma haka na shirya na tafi makaranta,koda naje ban kula Jabeer ba haka shima har sai da muka gama yau ƙarfe ɗaya muka gama hakan yasa kawai na hau mota.

   Har bakin motar ya biyo ni yace"haba Buddy meye na shariya" ban tanka mishi ba,"haba ke kuwa ƴar ƙawa ta fito na sauke ki".

  Ƙin fita nayi,haka ya gaji da magiyar shi ya haƙura ya tafi,mun kusa tashi kenan Zuby suka ƙaraso wajen.

   "ji waccen mutuniyar taki",Zuly ta faɗa,Zuby ta kalle ni sannan tace"ban yi tunanin ganin ta haka ba ai,amma zo muje sai mu sami dama na biyu a kan ta".

   Zuby ce tazo ta mini daɗin baki har na sauka na bita,gaba na shiga ita kuma Zuby ta shiga baya.

   Haka muka fara tafiya hira muke jefi-jefi har muka iso Queen Hotel dake Kwangila,a nan naga sun karya kwana sun shiga.

   "me kuma zamu yi a ciki,Zuly tace"sorry yanzu zamu fito ba daɗewa zamu yi ba saƙo kawai zamu amsa".

   "ni dai gaskiya sai dai ku shiga ku fito amma ba zan bi ku cikin hotel ba mutanen mu basa ɗaukar hotel a inda mutanen kirki suke zuwa gashi baba na babban malami kuje kawai ku dawo".

   Zuby tace"insha Allah kuwa zamu dawo da wuri kada ki damu",ina zaune suka fice suka bar ni a ciki.

   Gajiya nayi da jiran nasu hakan yasa na fito na ɗan jingi na da motar,wani saurayi ne yazo kamar zai faɗo jiki na,cikin sauri na kauce.

   "ayya dan Allah kiyi haƙuri wallahi matsala aka samu",Murmushi nayi nace"babu komai",kallo na ya kuma yi sannan yace"kamar ƴar gidan Malam Mukhtar".

   Fuska a sake nace"nice",ayya amma me kike a hotel bakya ganin hakan kamar zubar da mutuncin mahaifin ki bane",ya faɗi hakan.

   "ayya kada damu ƙawaye na nake jira yanzu zasu fito",kan na rufe baki sai gasu Zuly dan haka cikin farin ciki nace mishi"to ka gan su nan".

   Sallama muka yi dashi sannan muka shiga mota muka tafi,har layin mu suka ajiye ni sannan suka juya ni kuma na ƙarasa a ƙafa.

    A haka har muka fara jarabawar ƙarshen semester wato daf da zamu shiga 400 level kenan,har lokacin Yaya Khaleel be kira ba sai dai zuwa lokacin mun dawo dai-dai da Jabeer.

   Yanzu tsakani na dasu Zuby sai dai gaisuwa kawai da kuma fira kaɗan,dan Jabeer yana zuwa zasu matsa daga inda nake.

*****    ******    *******

"Na yadda muje ayi bincike inda har ka gano akasin haka to na yarda ka ɗauki mataki"Yaya Abdus-samad ya faɗa.

   "Abdus-samad ba zan ɓatawa kaina lokaci akan abinda nake da shaida ba,jifa Juwairiyya ce a hotel!",cewar Yaya Khaleel cikin jin zafin hakan.

    "me yasa kake yanke hukunci akan abinda baka yi bincike akai ba",Yaya Khaleel yayi ƙwafa yace"nufa na lura kamar ganin laifi na kake wajen lalacewar ƴar uwar ka".
   
  "Khaleel yau kai ke faɗin haka?",ɗaga kai yayi yace"tabbas abinda kake nunawa kenan ai ƴar uwar kace".

   "kada kayi mini wata fassara daban",ya faɗa yana dafa shi,Yaya Khaleel yace"za mu tafi gobe amma ka sani inda har naga akasin hakan to baka da bakin tuhuma ta a gaba".

   Jinjina kai Yaya Abdus-samad yayi cikin tabbatarwa,Yaya Khaleel kuwa juyawa yayi kawai ya fice daga gidan.

   Khairiyya dake laɓe tana ji ta buga tsalle tana faɗin"Alhamdulillah ashe ka gano ta kai ma yaya".

   Ganin Yaya Abdus-samad yana tahowa yasa tayi saurin barin wajen ta nufi kan dinning ɗin.

   Zama yayi yana huci,kamar munafika ta ɗauko cup ta zubo mishi ruwa a ciki ta miƙo mishi,wata uwar harara ya jefa maka kan ya amshi ruwan ya watsa mata a jiki.

   "wallahi ki sani matuƙar kika sake naji maganar nan a gida ko na lahira sai ya fiki jin daɗi",jiki na rawa ta amsa da to.

  Dogon tsaki yaja sannan ya fice,zama tayi a kan kujera ta zuba uban tagumi wai dama haka auren yake?,babu wani annashuwa da farin ciki.

   Kullum cikin ƙuntata mata yake wai yace ba zai taɓa kula ta ba har sai lokacin da komai ya dai-dai ta tsakanin Yaya Khaleel da waccen shagiyar.

   To ita ina ruwan ta da wani shiryawar su(kasancewar bata san an ɗaura musu aure ba),murmushi tayi a ranta ta kuma cewa"ai dai ko babu komai yadda nake cikin baƙin ciki haka itama zata kasance kuma wallahi sai na faɗawa Momma".

   Da gudu tayi ɗaki ta ɗauko waya,kasa kira tayi domin Allah ya sani tana tsoron abinda Yaya Abdus-samad ɗin zai yi mata dan koda baya nan ta san akwai shi da saurin ankarar abu kamar Omer😉.

  Maida wayar tayi tana ƙunƙunai,shi wannan yayan kamar me gani har hanji,jifa ɗazu yadda ta maƙale take jin firar su amma wai har ya gane tana wajen.

   Washe gari da wuri suka baro garin maiduguri suka nufo Zaria,su biyu suka taho dan Yaya Al'ameen be biyo su ba.

   Basu iso zaria ba sai bayan isha'i,hakan yasa ba kowa bane ya san da zuwan su,har ni ban san sun iso ba.

   Ranar na gaji sosai domin kuwa a ranar naje kasuwa nida Abdul'azeez muka yi siyayyar tafiyar shi makaranta.

   Haka kuma a ranar muka gama jarabawa,dan haka na kwanta barci da wuri,dan tun ina saka ran zai kira ni har na cire.

   Washe gari da wuri wajen tara na shirya domin kaiwa amare ziyara,dan haka ina gama abinda nake yi na hau shiri.

  Atamfa na saka me kalar blue da kuma pink,tayi mini kyau sosai hijab blue na saka haka taklmin ƙafa ta da jaka.

   Sai da na yiwa Ummi sallama sannan muka fita,domin kuwa shi Abdul'azeez zai je sabon gari ya yiwa su Hajajju sallama.

    Kafin mu ƙarasa pz na sauka motar da zata shigar dani gaskiya na hau,unguwar gonar ganye a nan na sauka sannan na nufi gidan.

   Gida ne babba sosai sai da na fara shiga gidajen sauran sannan naje wajen ƙawa ta kuma ƴar uwa ta,wato Rufaida.

   Ina shiga na tarar dasu a harabar gidan,da gudu ta nufo ni nima kuma na nufe ta da nawa gudun,rungume juna muka yi cikin farin ciki.

   Sai daga baya ta sake ni sannan ta juya mini baya,dariya nayi nace"haba rabin raina,kema kin san wallahi makaranta ita ta hana ni zuwa".

   Harara ta balla mini sannan tace"to naji yanzu sai kizo mu shiga ciki ko",Yaya Khaleed yace"to na tafi tunda an manta dani",dariya muka yi gaba ɗaya.

   Ban san me yasa ko lokacin da aka ce Rufaida zata auri Yaya Khaleed ɗin ba banji haushi ba,sannan kuma ni bana damuwa da wai yadda suke yanzu.

   Abin motsa baki ta kawo mini,ni dai da idanu kawai nake bin ta,tayi ƙiba tayi kyau sosai da sosai.

   Dariya nayi sannan nace"lallai ruwan aure ya amshe ki",itama cikin dariya tace"au har wani ruwan aure ake",dariya kawai nayi.

    Kusa dani tazo ta zauna sannna ta riƙo hannu na tace"rabin raina meke damun ki?",gefe na kalla,ina mamakin yadda Rufaida ke saurin gane ina cikin matsala.
   
   "rabin raina Yaya Khaleel fa ya canza mini gaba ɗaya",na bata amsa,"to ai na ɗauka kun ɓata ba yace kada ki kuma kula shi ba?".

   "rabin raina,maganar da fa kike yi amma yanzu fa da bambanci,sannan kuma komai ya canza fa".

   "ni ina ganin ki ƙyale shi kawai domin takura mishi da zaki yi shi zai saka ya ƙara wulaƙanta ki kawai ki manta dashi".

   Cikin mamaki nace"Rufaida kin san me kike cewa kuwa?,Yaya Khaleel fa *MIJI NA* ne taya zan ƙyale shi idan ban janyo shi jiki na ba yaushe zan ja shi zuwa lokacin da muka tare?".

   "tsaya yaushe aka yi auren ku?",ta tambaya,murmushi nayi sannan nace"lokacin da aka bashi damar ya ɗauki nauyin karatu na kuma na san an ɗaura mana aure ne bayan rashin lafiyar da yayi wanda ban je na gaishe dashi ba,bayan sun tafi shine Yaya Abdus-samad ya kira ni yayi mini faɗa sannan ya kuma fada mini".

   Ihu Rufaida tayi sannan ta miƙe ta fara rawa,ni dai dariya kawai nake mata,sai da ta gama sannan ta dawo ta zauna.

   "ah lallai dole na baki sirri ka wallahi amma yanzu lokaci ya ƙure ki bari zan saka Yaya Khaleed ya kawo ni gida gobe sai muyi zama me kyau".

   Haka har muka rabu tana ta jin daɗi sannan kuma tana daɗa yi mini nasiha da kuma dabarun da zan janyo miji na a jiki.

   A ƙofar gida ta tsaya hakan yasa bayan mun yi sallama na tafi,inda nake sauri domin na fita titi na samu mota na hau.

     Ina tsaye a bakin titi suka ƙaraso,parking suka yi sannan Zuly ta leƙo tace"Hey!baby Juuu sai ina",kusa dasu na tsaya sannan nace"wallahi gida nake son tafiya".

   "ayya to kizo mu rage miki hanya mana",ban wani ja sosai ba domin duk wanda ya san gaskiya lay out idan yamma tayi ana wuyar abin hawa saboda unguwa ce ta manya ga kuma poly advance yawanci ɗalibai suke hayewa ragowar.

Ina shiga suka ja motar muka fara tafiya,muna tafe muna fira,Zuby tace"wai dama kina da ɗan uwa soja ne?",ɗaga mata kai nayi nace"eh,har guda biyu ma,da Yaya Khaleel da Yaya Abdus-samad".

"a wane gari suke aikin?",Zuly ta tambaya,ban kawo komai a raina ba nace"Maiduguri",ihu suka yi sannan suka ce"kice a garin mu ma suke".

"oh/! Hakane fa wallahi nama manta kice idan na kai musu ziyara zaku dinga zuwa kenan?",a tare suka amsa da"mai zai hana kuwa?".

  Ruwan dake ajiye na ɗauka,zan buɗe Zuby tace"a'...",hararar ta Zuly tayi sannan tace"babu wani mu ajiye ta a ƙofar doka dan na san haka zaki ce".

   Ɗaga ruwan nayi na shaye tas sannan na ajiye gorar,nima cikin tsiwa nace"ai baku isa ba kullum baku kaini gida dan haka.......",maganar ce ta kara ƙarasuwa saboda wani irin juyawa da kaina yayi.

   Kaina na dafe ina ƙoƙarin buɗe idanu na wanda da ƙarfi da yaji yake son rufe,cikin maye nace"Zuly....wannan wane kalar ruwa ne?",wata shegiyar dariya tayi sannan tace"ruwan daɗi mana".

  Daga nan ban kuma sanin inda kaina yaƙe ba,Zuly ta kalli Zuby sannan suka fashe da dariya,juyawa suka yi suka nufi hanyar fita zaria.

   Can wani pub suka tsaya,diamond shines mine,shiga suka yi ƙida ne ke tashi kamar filin iblis,wasu samari ne guda uku tsaye suna jiran su.

   Fito dani suke ina tafe ina tangaɗi ga wasu kalar surutai da nake yi,tare muka shiga duka.

   Hayaniyar wajen yayi yawa sosai,Zuby ta ja hannu na har gaban wani tebur,zaunar dani tayi akan ɗaya daga cikin kujerun wajen.

   Kwalba ta miƙo mini kasancewar ba'a cikin hayyaci na nake ba yasa na amsa,sauran mazan guda uku kuwa suka zauna kusa dani.

   Ɗaya ya saka hannu ya janyo ni,kaɓe hannun shi nayi sannan na ɗauki kwalbar data faɗi ƙasa,ɗagawa sama nayi.

   Cikin maye na kai baki na,Zuby dake faman ɗaukar video tayi wani shegen murmushi domin dai komai yana tafiyar musu yadda ya kama ta.

   Sai da suka gama ɗauka sannan Zuly ta kuma jan hannu na,wani ɗaki muka shiga wanda iya gado ne sai ƙaramin table.

   Zuby ta miƙo wata leda,kayan ciki Zuly ta ciro sannan ta cire mini na jiki na tsaf ta saka mini wannan.

   Ƙaramar riga ce half wacce ko cibiya bata ƙarasa mini ba da kuma wani ƙaramin skirt iya cinya,kwantar dani tayi sannan suma mazan kowanne ya cire riga ya hayo kan gadon.

   Dariya suke yi,ni kuwa da hankali na ya gushe ganin suna dariya yasa nima na fashe da dariya a haka su Zuby suka ɗauki hotunan sannan mazan suka tashi.

   Ɗaya daga ciki ne yace"gaskiya Zuby babyn nan akwai ƙira haɗaɗɗiya,ya kamata ku bari mu huta da ita kan ku tafi".

   Zuly tace"ba zai yiwu ba ai mun riga da mun biya ku dan haka kawai ku tafi",ba dan sun so ba suka tafi.

   Zuly ta kalle ni yadda nake mayyen ma birge ta yake yi,hannun ta ta saka ta zagayo dashi ta ƙuguna.

   Ta kwantar da kan ta saman baya na tace"Allah sarki My Juuu baki ga yadda mayen ya miki kyau ba".

   Ganin zata shige da yawa ne ya saka Zuby mintsinin ta sannan tace"dan Allah ki sake ta mu tafi".

  "haba Zuby yanzu dama ta same ni amma kike maganar na bar ta pls ki bari ko kaɗan ne na ɗan ɗana ta mana",Zuby tace"ki bari next time mana ina fa kallo lokacin da zaki canza mata kaya kika dinga tattaɓa ta kamar wata mayya".

  Yawu ta haɗiye sannan tace"ki dai bari wallahi fatar ta akwai taushi wayyo baby na",Zuby ta ja tsaki sannan ta ciro wata allura ta sira mini a hannu.

    "duk abinda ya faru ba zata tuna shi ba dan haka taho muje mu kaita kin san Soja na baya sake da ita ga kuma wannan shegen da koda yaushe idanun shi na kan mu".

   Jan hannu na suka yi muka fice,haka suka tura ni mota ina daɗa shirme saboda allurar da suka yi mini.

   Waya ta Zuby ta ciro sannan ta turawa Jabeer saƙo ta goge sannan ta maida wayar,haka muka nufi ƙofar doka kaina a juye.

   Dai dai layin mu suka shiga kaɗan,kan kwanar da zasu karya su isa gidan mu nan suka yi parking.

    Zuly ce ta fito ta leƙa hango Jabeer a tsaye a waje ya saka tayi murmushi sannan ta buɗe motar ta janyo hannu na sai da ta shafa gefen fuska ta sannan ta tura ni dai-dai kwanar.

   A bakin nan suka tsaya suka turawa Yaya Khaleel duka hotunan namu,da video n,sannak suka ja motar su suka tafi.

   Yana zaune a varender ya lumshe idanu a zahirin gaskiya tunanin abubuwa da yawa yake yi sai dai ko meye idan har aka gano cewa tabbas da gaske Juwairiyya tana bin maza to zai sauwaƙe mata ne dan ba zai zauna mazinaciya ba Allah ne shaida be taɓa zina ba dan haka ba zai auri mace mazinaciya ba".
 
  Ƙarar shigowar saƙo ya ji,gani number ɗin sai da ya tsorata,cikin rawar jiki ya buɗe,da sauri Yaya Abdus-samad ya fuzge wayar.

   Yaya Khaleel ya matso kusa dashi,wayar ta suɓuce daga hannun Yaya Abdus-samad,shi kan shi yanzu abin ya fara bashi tsoro domin ya kira Rufaida ya tambaye ta ni tace mishi ai tun ɗazu na taho ya kuma isa ace na iso yaƙi faɗawa ɗan uwan nashi ne gudun tashin ciwon shi.

   Kallon shi ya mayar kan Yaya Khaleel wanda zufa take keto mishi,idanun Yaya Khaleel ɗin yana kan shi hakan yasa kawai ya maida kallon shi kan wayar dake ƙasa.

   Babu zato ba tsammani suka ga an ɗauki wayar,a tare suka kalli wanda wayar ke hannun shi, *BABA MALAM* bayan shi Abba ne da Baba da kuma Baban gida wato dai duka iyayen su.

   Da alama sallar zasu je yi dan duka da ruwa a fuskar su wanda ke nuni da sunyi alwala kenan.

   "meya faru kuke tsaye haka ?",ya faɗa yana ƙoƙarin miƙawa Yaya abdus-samad wayar,cikin sauri Yaya Abdus-samad ya miƙa hannu zai amsa baba malam yayi saurin janyewa,saboda hotuna daya bayyana a screen din cikin shigar ƙananan kaya hannu na riƙe da kwalbar giya ina tsakiyar maza har guda uku muna dariya.

   Ya kalla tsayin lokaci sannan yace"Yaya duba mini hoton nan kamar Mama na nake gani?",cikin sauri Abba ya amsa.

   Kallo yayi shida Baba domin dai Baban gida ba gani yake yi ba,sosai suka kalli hoton sannan Abba yace"kai anya kuwa Malam wannan ba Mama na bace me dai kama da ita ne".

   Dai dai lokacin dana ƙaraso inda Jabeer yake be shaida ni ba har sai da na wuce dan dai da farko ya tsaya kokwanto ne ganin me kama dani sanye da ƙananan kaya kuma cikin halin maye sai da yaga na nufi get ɗin gidan sannan ya tabbatar.

   Mamaki ya cika shi wanda yasa cikin sauri ya fita ya taro ni,"JUWAIRIYYA!" juyawa nayi na kalle shi sannan na kwashe da dariya nace"au ashe kowa ma a ƙasa na yake ƙafa zan saka na take ku duka ƴan tsaki".

   Girgiza kai yayi yace"amma dai kin ɓata wayon ki,meye wannan irin sakayyar da zaki yiwa iyayen ki kenan",.

   "iyaye na,ai ni bana da wani iyaye wanda ya wuce zakaran daji,kuma gajimare akwai daɗin hawa".

   Hannu na ya riƙe yana faɗin"ba zan iya barin ki ki shiga cikin gidan ku a haka ba",ihu na tsandara me ƙarfin gaske wanda ya zagaya duka gidan mu".

    Cikin sauri ya sake ni sannan ya koma baya,duka ƴan gidan mu sai da suka fito,duka suka tsaya suka zuba mini idanu cike da mamaki.

   Ni kuwa tsalle nake ina faɗin"driver akwai na nan,kada ka wuce dani birnin sin",cikin fusata Baba malam ya wanke ni da marin da sai na jina da gani na ya ɗauke.

 
#LIKE
#SHARE
#COMMENTS

   *Babyn Abdul,Maman Meenal,elham da farouk*

     *ƴAR MUTAN ZAZZAU*

Continue Reading

You'll Also Like

348K 40.1K 74
✦ ᴄᴀɴ ʙᴇ ʀᴇᴀᴅ ᴀs ɢᴇɴᴇʀᴀʟ.ғɪᴄᴛɪᴏɴ ✦ - 𝖒𝖆𝖓𝖎𝖐 𝖝 𝖆𝖓𝖆𝖍𝖎𝖙𝖆 𝖝 𝖓𝖆𝖓𝖉𝖎𝖓𝖎 - --- ♡ --- "𝘔𝘺 𝘩𝘦𝘢𝘳𝘵 𝘴𝘵𝘰𝘱𝘱𝘦𝘥 𝘴𝘦𝘢𝘳𝘤𝘩𝘪𝘯𝘨 𝘧...
19.7K 1.8K 7
Wanna visit rajasthan than read this special book about my love Rajasthan 💗
407K 16.1K 48
Vikram, a senior officer, prioritizes his duty above all else, much like his father, ACP Rajendra. He has three siblings: one is an officer, and the...
Ice Cold By m

General Fiction

2.3M 84.4K 49
[boyxboy] Wren Ridley is always two steps ahead of everyone, or so he thinks. His life seems out of his control when he starts having feelings for so...