🍒🍒SOYAYYA MAI GARƊI🍒🍒

By SiyamaIbrahim

39.1K 2.4K 94

It's all about love betrayal of trust and bargaining More

Page 11
Page 1
Page 2
Page 3
Page 4
Page 5
Page 6
Page 7
Page 8
Page 9-10
Page 11
Page 12-14
Page 17-18
Page 19-20
Page 21-22
Page 23-24
Page 25-26
Page 27-28
Page 29-30
Page 31-32
Page 33-34
Page 35-36
Page 37-38
Page 39-40
Page 41-42
Page 43-44
Page 45-46
Page 47-48
Part 49-50
Page 51-52
Page 53-54
Page 55-56
Page 57-58
Page 59-60
Page 61-62
Page 63-64
Page 63-64
Page 61-62
Page 65-66
Page 67-68
Page 69-70
Page 71-72
Page 73-74
Page 75-76
Page 77-78
Page 79-80

Page 15-16

580 45 0
By SiyamaIbrahim

🍒🍒SOYAYYA MAI GARƊI🍒🍒*
_(Pure Love, Revenge and bargaining)_

By
*Siyama ibraheem🍒*
Wattpad@siyama Ibrahim

'''DEDICATED TO SURAYYAHMS'''🐈

1⃣5⃣➖1⃣6⃣

  Da saurin mu muka karasa shiga dakin da zuwan mu abu na farko da muka fara kokarin yi shi ne ja mata skirt din ta da muka fara kokuwar yi amma ya ki fita saboda wani shegen kiba ta kara a cikin wadannan watannin da muka yi a gida tunda babu abin yi makaranta ne kuma yanzu babu shi..ai da sauri ta ce mana

"Ku menene haka kuma ya kuke abu kamar wasu kananan yara ne koh baku san cewa kun girma ba ne ha'an" ta ida maganar tana wani cicin magani ita a dole an ce mata girma ya zo mata

Da mamaki muka tsaya cak kamar ruwa ya cinye mu ganin haka sai kuma ta ga kamar tayi overreacting sai ta riko hannun mu gabadaya tana kallon mu da dan damuwa ta fara cewa

"Kun ga umma ce ta ce min na girma saboda na fara ganin jinin haila na ba ciwo na ji ba ashe ta kuma ce min dole in kara kama kaina dan yanzu da da ba daya bane in nayi kuskuren barin wani namiji ya taba min koh da hijabi na ne sai na dau ciki tace min daga yanzu zan daina rashin hankalin da nake yi dole in rinka kama kai na in rage yawan wasa da wawan zama har fah ce min tayi yanzu zan fara ramukon azumi da fashin sallah toh fah abin da tace min kenan shi yasa ma kuka ga na hana ku ja min skirt dina amma in kun yi fushi ku yi hakuri  ta ce zata zo ta mana nasiha gabadayan mu anjima in zata kawo min pad din da zan saka dan kar in bata kayana da jini""

Jin haka ya sa duk muka saka mata dariya muna ce mata Ayyah yanzu shikenan babu ita babu wasa kuma ga fashin sallah da azumi ga shi in ta bari ta kuma hada kafada da maza shikenan ciki zata dauka tunda ita dai har ranar graduation din mu sai da tayi rigima da adebola saboda ya mata dariya wai graduation gown din ya mata kadan shine fah ta ce da wa Allah ya hada ta in ba shi ba sai da aka rabasu kafin a sami salama

Kuka ta saka mana sosai dan dama can aikin ta kenan abu kadan kuka har ta sa yaya aqeeb saka mata suna wato "Idon kuka" tana cikin yin kukan ne umma ta shigo tana mana fada akan me zai sa mu rinka tsorata ta bayan muma nan kusa muna gab da farawa ai da jin haka sai muka natsu muka daina mata dariya

Nasiha da fadakarwa sosai umma ta mana musamman saboda ni ta yi wannan fadakarwar saboda nice ban da uwan da zata koya min in lokacin koyawar ya iso falmata na da uwa haka salma so da dama takan kira mu kitchen in tana girki ta ce mu rinka kama wasu abubuwan mu yi koh kuma in zata yi aike zuwa kasuwa sai ta ce mu tafi tare da driver sai a bamu list din abubuwan da za'a siya mu mu siyo duk saboda ni take yin hakan dan tausaya min take yi ba na wasa ba ganin rainon mahaifina ne kawai sai yaya ibrahim wanda duk da hakan tana ganin bazai ishe ni gudanar da rayuwana ba ga shi ina da kanwa mace duk wani abin da zata yi nan gaba a rayuwar ta zai kasance rainon da na mata  ne  toh idan nima ban sami isashiyar rainon ba ta yaya har zan koyawa kanwata wadannan dalilan ya sa ta kan zage ta koya mana abubuwa sosai a fannin mama wato maman su falmata ma ba'a bar ta a baya ba in har muna sashen su toh bata barin mu haka kawai dan jajjage yankan albasa goge wurin d aka bata yayin da ake girki da dai sauran kayan aiki da ya shafi ƴa mace a rayuwar ta saboda itama kallon tausayi take min kuma tana jana a jiki hakan ya sa bana shiga kadaici ga hasinah da ta zamewa ummi kamar ƴar uwarta ta jini komai za'a siya mata sai ta ce ina na farida dan ita da faridar take kiranta wai ya fi dadi ba kasafai take kiran ta da ummin ba sai dai in ta yi laifi za'a hukuntata sai ta fara cewa ummi ki taimake ni umma zata min duka toh hakan da take yi sai ya rinka sanyaya jikin umma ganin in ta dake ta toh lallai ummi zata na mata kallon marar imani shi yasa da zaran hasina ta yi laifi in ta gudo zuwa gun ummi toh umma bata iya hukuntata sai dai in ummin bata nan toh koh shi yaya aqeeb din bai isa ya hana a daketa ba

Bayan ta mana nasihar ne ta fiddo da pad din ta mikawa salma hannun ta akan ta bata pant din ta ta mika mata itakuma umma ta bude ledan pad din ta cire ta fara sakawa tana mana bayani dalla dalla har ta gama ta mikawa salma pant din akan ta je ta yo wanka sai ta saka tana shiga bayin umma ta kara ja mana kunne ta kuma jadada mana akan dole sai mun kara hakuri da salma dan zamu fuskanci changi daga gareta kafin muma mu kai matakin da ta ke ciki amsawa muka yi muna jimami da haka ta bar mu muna ta maganar abin da falmata

Lokaci na dada ja abubuwa na ta sauyawa a rayuwar mu changi kam daga wun salma mun ganshi har mun saba ko dan kuwa ji take yi kamar ita ce babba da mu ko ma kamar uwar mu ta manta cewa shekarun mu daya dan yanzu muna neman cika shekaru shadaya(11)  cikin abubuwan da suka faru har da cigaban Abbu dan kuwa bayan aikin da ya ke yi da kamfani shagon sa na kasuwa ya hayayyafa ya karu har zuwa shaguna hudu manyan gaske masu zaman shagon Abb na tun asalin wato yahaya da zakir sun rike amana gaskiya a halin yanzu daya daga cikin shagunan Abbu shi ke kula da shi dayan kuma yahaya ga karin masu aiki da aka samu lokaci lokaci in yaya ibrahim ya dawo hutu yakan zauna a shagon Abbu wanda yake cikin wuse zone 2 in kuma ya koma sai isma'il ya cigaba da aikin dan yanzu shekaru sa goma sha shida wanda yayi daidai da shigar sa ajin karshe a makarantar sakandire mu kuma har mun sami makarantar gaba da primary muna matakin ajin farko a wani makaranta mai suna *NEW HORIZON*  da ke garin Minna Niger state makaranta ne na ƴaƴan masu da akwai dan a lokaci nima ba laifi Abbu na ya fara zama hamshakin kanshi toh dama chan Hamshakin ne yanayin rayuwa ne ya maida shi haka

  Yaya aqeeb shi ne da na biyu a ahalin su daga babban yayan su mai suna kabeer wanda yake kasar china yake karantar gynaecology Wato likitan mata

Yana ajin shi na karshe kenan ban san shi ba ban taba ganin shi ba dan ba kasafai muke hirar shi ba ita kanta salma ba wani sanin shi tayi sosai ba sai dai a hoto kokuma in ya zo hutu su hadu a wun cin abinci yadan yi mata wasan da zai yi wanda baya wuce yar lukuta da yake ce mata bayan wannan bata wani san abu mai zurfi game da yayan nata ba

Daga shi sai yaya Aqeeb wanda a yanzu shima yake matakin karshe a makarantar sakandire da ke chan cikin garin Abuja dama dama shi in ya dawo hutu mukan hadu dan har mun saba sosai saboda kallon dan uwa na nake mai shima kuma ba laifi baya duba cewa ni din ba yar gidan su bane yanda yake yi da kannen shi haka nima yake min

Yaya umar yayan falmata kuwa yanzu ne ya ke shiga matakin farko a jami'an Abuja wato University of Abuja wanda ya kasance babu ruwan shi shiru shiru kuma bai cika son hayaniya ba koh da ya kammala secondary school din shi Abba ya so ya tura shi china wai ya hadu da yaya kabeer amma ya ce a'a nan ma Abuja ya ishe shi ya yi karatun shi ya suka iya haka suka bar shi aka samo mai Admission ya fara zuwa sati sati yakan dawo gidan dan ya kasance ne kamar ustazu yanayin shi da rike mutuncin shi ya banbanta da yanayin samari ƴaƴan masu da shi na zamanin nan Law yake karantawa kuma yana da buri babba akan ganin ya cimma kudirin shi a rayuwa(koh menene wannan kudiri oho)

Ummi da hasina kawance ya musu dadi girman jiki kamar hura su ake yi suturu iri kala daban daban su ke sakawa suma yanzu shekarun su shida shida kuma suna aji na biyu a matakin primary basu yarda sun kulla kawance da wata ba daga su sai su ga wani irin jiji da kan da suke fama da shi Abbu yana kokarin shi sosai wurin ganin ya tankwasa ummi amma ina jin kan nan sai hakuri

Abbu a ko da yaushe in Abba ya mai maganar yin aure toh bai cika dawowa gida cikin walwala ba dan shi gudun muguntar mata yake yi ace yayi aure amma wata macen ta yi kokarin shiga tsakanin shi da ƴaƴan shi koh ma ta cutar da su shi kuma bazai dauka ba shiyasa ma baya maganar kara yin wani aure saidai yace mai Alhaji zan duba koh da kuwa baban su falmata ne ya mai tambayar amsar daya ce dai

Ana haka ne muka tsunduma tsundum a karatu babu ji babu gani dan kuwa kowa dan jin kai ne a makarantar dalilin da ya sa bamuyi kawa koh daya ba kenan sai dai yan mutuncin da za'a gaisa sama sama lokaci zuwa lokaci 

Mukan dawo hutun rabin zango in mun samu(mid time break)toh duk lokacin da muka dawo ba'a rasa abin fada game da yanayin girman mu a wata dawowar ce falmata ta fara al'adar ta (period) ba ma ta gayawa maman ta ba kawai cewa ta yi ta bata kudi tana so ta sayi wani abu yin duniyar nan mama ta yi don ta gaya mata amma ta ki haka kuwa ta hana ta da kukan ta ta tafi sashen su salma ta kai kara inda umma ta kirawo maman falmata tana ce mata

"Haba hajiya yanzu yarinya budurwa da ita tana makarantar manya ba kananan yara ba ta ce ki bata kudi tana bukata amma ki ce sai ta gaya miki me zata yi da shi uhum"

Jin haka sai mama ta ce "hmm umma kece baki lura da halayar ta ba tun da ta tafi makarantar nan ta kara koyon banzan halin miskilanci da rashin son a takura mata wanda a da ba haka bane"

Dariyar manya umma ta yi kafin ta ce "ai ba ita kadai bacw dukkan su ne suka koma haka girman kenan ai da changin wurin zama kuma kin ga yanzu sun fara dogara da kansu ba bu mai saka musu ido sun fara sabawa da rayuwar sirri shi yasa zaki ga bata cika son sanar da ke matsalarta ba yanzu dai shiga ciki ki ce ma salma ta baki kudin sai ki sayi abin da kike son sayan(ita umma ta gane me falmata ke bukata tunda ita ta koyar da su akan ilimin wannan abin)

Da mamaki mama ta ce hajiya ba dai yar yarinyar nan ta fara ganin jinin haila ba kike nufi??

Itama umma da mamakin ta ce "tohh dama matsala ne dan yar shekaru 11 zuwa 12 ta yi haila"??
A tsorace mama ta ce da gaske falmata al'ada take yi"?

Murmushi umma ta yi kafin ta ce "kwarai kuwa Hajiya falmata al'ada take yi ai ba abin mamaki ba ne salma tun suna shekara goma ta fara yanayin jiki daban daban ne kin ga ita Aisha har yanzu bata fara ba ina ganin ita sai ta kai shabiyar kafin ta fara toh ai ba abin mamaki bane koh ba haka ba"

Jijiga kai mama tayi cikin gamsuwa tana mai yiwa umma godiyan abin da ita ta kasa yiwa ƴarta wato koyar da ita tun kafin hakan ta faru da haka suka rabu

Satin mu daya muka koma makaranta a chan salma ke min gulman ai falamata ta fara period da mamaki na kalle ta na ce haba da gaske shine bata gaya min ba sai tace bar munafuka wai ita nan kunya take ji sai muka yi dariya a daidai lokacin da ta shigo dakin ta gan mu ashe ta ji abin da muke fada sai t ce mall dai ya ce mai gulma dan wuta ne in kun fa dama kuyi ta yi munafukai kawai tayi tsaki ta zauna dariya muka saka mata kawai muka share ta

Tun daga nan salma da falmata ke yin monthly period din su yayin da nikuma har lokacin ban fara ba kuma abin bai wani dami na dan har seniors din mu da ke final year wasu basu fara ba ko kadan bai dami na

Wani abu da na fara lura da shi tattare da su falamata da salma shi ne yanzu sun fara maganganu marasa ma'ana da ɗa'a wanda hakan kan dame ni dan kuwa akwai wata isashiyar yarinyar da ke kawo musu litattafan hausa a boye suna karantawa in na musu magana sai su ce ai dan ni ban gama girma bane toh hakan na ɓata min rai sosai sai in fita a harkar su dan ƙashin kansu sai suka fara ragewa ganin kamar nuna banbancin da suke min ya na yawa kuma suna tsoron kar in mun koma gida in faɗa a musu faɗa da kyar suka rabu da wannan litattafan dan sai da na ma yarinyar tass na ce in ta yi wasa toh wallahi sai na kai kararta hukumar makarantar kuma ta san kora ne za'a mata dan dama scholarship ne take amfani da shi daga wun kawayen ta muke ji ai tana jin haka ta fara kama kan ta yawan karatun har yasa abin da ya kaimu makarantar ya fara tangarda a wurin su salma da falmata dan kuwa sun fara wasa performance din su ya fara raguwa koh a test ne makin su baya kaiwa kamar da ganin haka yasa suma suka fara kama kansu sai daga baya suka yi dana sanin abubuwan da sukayi a term din suka bani hakuri muka koma kamar da

Gab da exams din mu na third term ne na fara ganin wani muguwar change change a jiki na dan a lokacin daya nawa girman ya zo muna gama exams din mu ana gobe za'a zo daukan mu na fara ganin nawa period din abin mamaki wai nima na yi girma sai  da nayi kukan murna at least nima za'a fara saka ni a layin manya koh da na gaya ma su salma suma murnar suka yi min falmata ce ke bani pad in saka itakuma salma maganin ciwon cikin da su a lokacin sun manyanta a wannan bangaren

Mun dawo gida hutu kenan muka tarar da gidan a cike gidan mu ga su ummi suna hutu yaya ibrahim ya gama makaranta chan gidan su salma ma yaya kabir ya dawo gaba daya yaya Aqeeb ma ya gama makarantar saura na gaba

Murna kan murna haka muka yi hutun mu wanda kusan rabin shi a gidan mu muka yi a lokacin ne kuma yahaya ya bayyanawa Abbu nufin shi akai na da kuma neman alfarmar idan na gama makaranta zai fara zuwa wuri na Abbu ya ji dadin hakan dan har ya bashi tabbaci amma da sharadin in ban amince ba toh bazai min dole ba yayin da wata shakuwa ta shiga tsakanin falmata da yaya ibrahim shi kuma Aqeeb ya fara min wani gani gani tuntuni na harbo jirgin shi amma na yi kamar ban sani ba

  Fannin yaya Kabir kuwa abin ba'a cewa komai dan kuwa haduwar mu sau biyu amma na rasa dalilin da yasa yake min kallon kuril a duk sanda na je gidan su wannan dalilin ya sa bana son zuwa part din su salma in na tafi sai dai part din su falamata shi kuma wai so na yake yi sosai ashe falmata ta gano hakan itakuma tana nan tana fama da ciwon son da take mishi a cikin zuciyar ta amma ganin bai ma san tana yi ba yasa ta bar ma kanta kuma ta ki gayawa kowa dan duk cikin mu ta fi mu tsananin kunya da kawar da kai a abin da take so amma ta sa a ranta duk hanyar da zata bu dan ta same shi zata bi saidai in har bata yi sa'a ba toh sai ta hakura wannan alkawari ta yi wa kanta itakuwa uwar gayyar salma komai da ke faruwa bata da masaniya a kai abin da ta sani shine akwai shakuwa tsakanin ni da yaya Aqeeb falmata da yaya ibrahim bayan wannan bata san cewa yaya kabeer na mutuwar kaunana ba dan shi kanshi baya nunawa kawai dai jiran lokaci yake yi sai ya fallasa min amma a ganin shi har yanzu ni din yarinyace ban kai matsayin da zai fara min zancen soyayya ba

Ana wata ga wata kulawar da yaya ibrahim ke bawa falmata hakan na konawa ummi rai ba kadan ba dan kuwa hae ya kai matakin da in taga falmata a gidan mu ta rinka jan yaya ibrahim da surutun shirme kenan bayan ba haka take ba miskikancin tsiya ne da ita kamar ɗiyar sarki bai dau hakan a matsayin wani abu ba amma abin da ake cema babba babba ne Abbu ya harbo ta tsab dan duk a cikin mu ya fi bada karfi wurin kula da ita dan ya san nan gaba kaɗan wani irin mummunan zuciyan banza zata yi.......

*_🍒s,ibraheem🍒_*

Continue Reading

You'll Also Like

1.4K 423 36
A Koda yaushe muna Jin labaran zama da kishiya Mai ban mamaki da ban al'ajabi....Labarin MAHREEN labari ne na musamman Wanda zai fad'akar, ya nishada...
659K 23.7K 200
[FIXED/FAN TRANSLATION] A student who was preparing for the Civil Service examination for 4th year suddenly found himself in an unfamiliar body 3 yea...
443K 24.5K 166
Featured at Wattpad's Editor Picks list. Luna, an overworked Engineer, had an unfortunate end. Her spirit, feeling wronged, fights Death for a second...
40.4K 901 9
I am Elizabeth Swann's older sister. I was the only one who ever fell for Norrington. This is the story of how we came to be. Our story is one of lov...