🍒🍒SOYAYYA MAI GARƊI🍒🍒

By SiyamaIbrahim

39.1K 2.4K 94

It's all about love betrayal of trust and bargaining More

Page 1
Page 2
Page 3
Page 4
Page 5
Page 6
Page 7
Page 8
Page 9-10
Page 11
Page 12-14
Page 15-16
Page 17-18
Page 19-20
Page 21-22
Page 23-24
Page 25-26
Page 27-28
Page 29-30
Page 31-32
Page 33-34
Page 35-36
Page 37-38
Page 39-40
Page 41-42
Page 43-44
Page 45-46
Page 47-48
Part 49-50
Page 51-52
Page 53-54
Page 55-56
Page 57-58
Page 59-60
Page 61-62
Page 63-64
Page 63-64
Page 61-62
Page 65-66
Page 67-68
Page 69-70
Page 71-72
Page 73-74
Page 75-76
Page 77-78
Page 79-80

Page 11

4.6K 113 5
By SiyamaIbrahim

🍒SOYAYYA MAI GARƊI🍒🍒*
       _(Pure Love, Revenge and bargaining)_

  By
   *Siyama ibraheem🍒*
Wattpad@siyama Ibrahim

'''DEDICATED TO SURAYYAHMS'''🐈

1⃣1⃣

Da zuwa na ajin mu na fara shiga na zauna har lokacin yin assembly ya kai na fito ban ga su salma ba abin ya dame ni matuka duk a zato na koh latti suka yi nai ta saka ido amma shiru har muka gama muka koma ajin mu class teacher din mu ce ke fada mana wai ai an yi rasuwa gidan su falmata wani kanin ta ne ya rasu jiya da dare shi yasa basu zo makarantar ba yau

Kawayen su na ta jin tausayin su ciki har da ni da muka hadu jiya

Class teacher ce ta ce mana kawayen su uku su shirya in an tashi break za'a je gidan su da malaman makarantar domin yi musu ta'aziya

Biyu sun fito safiya hafiz da precious Matthew aka rasa wa zai cike na ukun kowa a zaton shi ni zan fito in cike su nikuma gaskiya Abbu ya hana ni zuwa koh nan da chan in ba a cikin makaranta bane

Tunohaka haka ya sa nace musu ni bazan je ba in an tashi zamu tafi ni da baba na sun ji mamaki ganin yanda muka saba sosai a jiyan amma in ki zuwa gidan su gaisuwar rasuwa a karshe dai da su su biyun aka yi tafiyan dan babu wanda ke son zuwa saboda bala'i irin na su salma da falmata (yarinta kenan a ce an rasa rai ana son ayi aikin lada amma kowa ki yake yi wai saboda wani kankanin dalili Allah ya sa mu dace)

Ana tashi break suka tafi ni dai Allah ya sani naso tafiya amma ina tsoron Abbu ya zo ya ji cewa na bar makaranta ba tare da izinin shi ba

Da suka dawo ne safiya ke gaya min wai ai sun ce a ce min sun yi fushi ban je gidan su tsakani na da Allah sai na fara kuka sabbin kawaye na sun yi fushi da ni toh nikuwa yau sai na tayar ma Abbu da rigima mun tafi gidan rasuwar in ya so na sami hanyar kubuta daga zuwa makaranta

Tunowa da nayi da wannan idea din ne ya sa na yi murmushi nace ma safiya
"Ai zan tafi gidan su in an tashi daga makaranta"ta ce toh

"Amma kin san gidan"
Na ce a'a ki gaya min sai ta ce min a ta federal housing gidan yake kenan kusan wuri daya muke tunda mu a 2/1 market muke su kuma kafin a zo nan anguwar mu suke

Malaman mu sun shishigo kuma duk wanda ya shigo sai ya kira attendance wanda ya sa duk wanda aka kira sunan shi sai ya tashi ya amsa toh ta nan na kalle yan ajin namu daya bayan daya ban dai rike sunayen da fuskokin duka ba amma na san wasu

Mun tashi a makaranta kamar jiya muka fito bakin gate in da muka jira Abbu jiya yau ma a nan muka jira shi da ya zo sai na gaishe shi na gaya mishi abin da ya faru yau wanda aka gaya mana a makaranta

Sai yace
"Toh mama na ya za'a yi yanzu kin ga anjima akwai Islamiya"

Ai tunowa da nayi da yaran nan sai kawai na hau dadaga Kafa akan ni dai mu tafi gidan su salma saboda suna so na

Kallo na Abbu yayi shi dai ya san ban da rigima bayan surutun tsiyan da nake da shi sai gashi yau ina gwada mishi rigima karara
sai ya ce mama na toh na ji zamu tafi amma ke kin san gidan ne?

Da murna nace ai safiya ta ce min a federal housing su ke

Ya dan tsaya na wasu yan mintoci yana nazari idan dai bai manta ba toh federal housing angwar masu hannu da shuni ne toh ita wannan a ina ta samo kawaye masu kudi haka

Da naga shirun yayi yawa na dauka fasawa yayi sai kawai na saka kuka

Ya yi saurin dago kan shi yana tambaya na lafiya

Na ce "Abbu ba ka fasa zuwa da mu bane kuma ka ga hasina kanwar salma kawar ummi ce toh kuma Abbu sai ka ce baza mu tafi ba" na cigaba da kuka

Abin ma mamaki yake ba Abbu sai ya ce

"Mamana taho kumu tafi gida in kun ci abinci sai mu tafi koh da zuwa karfe biyar ne na yamma

Tsabar rashin hakuri irin nawa sai na tare shi ta hanyar cewa
"Abbu har sai dare yayi kafin mu tafi ni ni nidai"

Na bashi dariya sai yace mamana ai saboda bana son kuyi fashin islamiyar ku ne yau kinga in na kai ku sai in yiwa malamin ku magana koh da 4:30 pm ne sai mu tafi chan gidan nasu koh ya kika gani??

Nikam tsoron zuwa islamiyar nake ji amma na san idan zan fada cewa zai yi saboda zuwa gidan nake karya alhalin ba hali na bane haka dai na yi gumm ban kuma cewa Komai ba har muka kai gida ni da ummi mun gama komai muka kama hanyar zuwa Islamiya a daidai gate din makarantar nafara tsorata amma na yi shiru har dai na shige ajin ina dar dar

Inda Allah ya taimake ni shine yau basu zo ba dama wai sai an kawo su makarantar in ba haka ba ba zuwa suke yi da kansu ba toh da naga basu zo ba sai na sake jiki na nayi bitar karatun da aka min jiya malamin ya kara min

Ana tashin mu sallar la'asar Abbu ya zo daukan mu dama ya ma malamin makarantar bayani da zuwan shi da kawai muka wuce

Da zuwan mu gida na yi sallah na chanza kaya na duk sai doki nake faman yi

Abbu na ta farinciki na fara walwala na sami kawaye
Muka fito muka tafi bakin titi inda muka tsare a taxi ni na gaya ma mai taxin inda zamu tafi ya fadi kudin kafin ya ja mu muka tafi sai federal housing a daidai nan ya sauke mu yace mana mun kai muka firfito Abbu ya biya shi kudin shi

Sai kuma aka bar mu da kame kame saboda wurin dai kusan zan iya cewa shiru yake da kyar muka sami wani yana tafiya a hanya muka tambaye shi gidan da akayi rasuwa jiya sai ya ce mana mu yi tafiya zuwa karshen layin sai mu yi kwana toh akwai gidaje a wurin sai mu duba gida mai lamba 44 a nan aka yi rasuwar

Muka mai godiya muka tafi da kwatancen shi muka iso gidan wanda yake gida ne na masu kudi dan babba ne ga kyau mun bata lokaci sosai kafin a bar mu mu shiga gidan har mun cire ran za'a bar mu mu shiga

Ko da muka shiga sai muka ga fanni biyu mun rasa wanne ne zamu shiga aiko sai ga hasina kanwar salma ta fito daga daya fannin tana hango ummi ta zo tana ta kiran sunan ta wai tazo su tafi kafin su bar wurin sai ga wasu maza sun fito kusan su biyar suma din ta'aziya suka zo yi a nan ne Abbu ya tsaya suka gaisa da su ya musu ta'aziya sai  ya ce musu ai yar shi ce ta ke gaya mai rasuwar da mamaki suka ce wacce a ciki sai ya nuna musu ni yace ai makarantar mu daya da su

  Sai daya a cikin su yake cewa
"Ai jiya da yaran suka dawo basu bar su sun huta ba sai labari suke yi wai sun yi kawa a makaranta jiya sunan ta Aisha Murad"

Abbu ya yi murmushi sai mutumin ya raka bakin shi kuma ya wa Abbu bismillah zuwa ciki muna shiga ya sa aka kira wata mata wacce da ka ganta ka ga falmata domin kamanin nasu har ya baci da ta iso sai mutumin ya ce

"Hajiya ga baki nan mun yi sun zo ta'aziya ne kuma wannan ita ce kawar su yaran nan da suka ce sun yi jiya a makaranta"

Matuka matar ta ji dadi don har take kara godiya kafin ta ce in zo mu shiga suna ciki

Tafiya muka yi su kuma su Abbu suka cigaba da magana a nan Abbu ke sanin cewa shine mahaifin mai rasuwar kuma baban falmata har yake gaya mishi ai shi dan asalin maiduguri ne a wani yanki mai suna Gonin goza kasuwanci ne ya kawo shi nan shine ya samu uban gida mai mutunci da daraja dan adam har ma ya bashi wani matsayi a ma'aikatar shi ya jawo shi ya hada da iyalin shi ya kuma bashi yarda da aminci

Sai yaba mai yake yi ya dora da cewa ai falmata ce yar shi ta biyu akwai babban yayan ta da ke karatu a wani makarantar kwana na sakandire a cikin Abuja sai falmata da kuma kanin ta da Allah ya ma rasuwa a jiya wanda ba zai wuce shekaru uku ba zuwa hudu

Abbu ya dada yi mai ta'aziya shima ya bashi labarin cewa ai shima dan maiduguri ne ya gaya mai komai da ya faru da shi da yanda ya zo nan ya kafa kasuwancin sa

Shima ya mai jajen abin da ya same shi yake tambayar shi toh ina maman su Aishan

Sai da Abbu ya dan yi shiru kafin yace ai ta rasu tun ranar da ta haifi farida wanda wanda wanda sunan ta aka mayar ma yarinyar

Da tausayi baban falmata yake kallon Abbu ya ce Allah ya jikan ta haka dai suke ta tattaunawa akan sha'anin rayuwa

Mu kuwa da muka shige ciki dakin su direct aka kai ni da shiga na kawai sai suka fasa ihu sun ma manta rasuwa aka yi (yarinta kena)

Muka rungume juna suka fara min surutu wai me zan ci a kawo min na ce ba kai suka bata fuska su a dole sun yi fushi sai na ce toh a kawo min koma menene salma ce ta fita ta dawo da abinci a babban tire da cokula wai mu ci haka muka zauna muka ci tare sai annishuwa muke yi sai suka tambaye ni halan me yasa ban zo ba da yan ajin mu suka zo

Amsa na basu da ai tare da Abbu muka zo kuma shi ya hana ni yawo in ba tare muke ba shiyasa ban zo ba dazu sai na ce ai har da ummi muka zo amma sun shiga wani wuri ita da hasina

sai suka ce ai dakin su suka tafi a nan dai muka sha hirar mu salma ke ce min ai su Abban ta sun yi tafiya tare da umman su kenan ragamar gidan a hanun baban falmata yake muka sha hirar mu kamar kar mu rabu sai ga maman falmata ta shigo kira na wai in zo mu tafi

Suka rako ni har falon inda suka gaida Abbu sai ga su husna ma sun fito haka muka rabu akan zamu hadu gobe a makaranta ni har ma na manta da maganar yaran islamiyar mu da nake so in gaya musu har mun yi nisa na dawo na gaya musu ai ko suka ce in Abban su ya dawo zasu ce mishi ya dawo da ni makarantar su su dai iyayen mu na ta jin mamakin shirmen mu da haka muka tafi gida

Pls manage walahi schedule dina na yau is very tight ne hope zaku karbi uzuri na

_*🍒s,ibraheem🍒*_

Continue Reading

You'll Also Like

441K 24.4K 166
Featured at Wattpad's Editor Picks list. Luna, an overworked Engineer, had an unfortunate end. Her spirit, feeling wronged, fights Death for a second...
541K 17.6K 157
Genre: Space, Doting, Farming, Time travel, Healing Synopsis: Xu Linyue from the 21st century crossing over with the heavenly space soul penetration...
1.4K 423 36
A Koda yaushe muna Jin labaran zama da kishiya Mai ban mamaki da ban al'ajabi....Labarin MAHREEN labari ne na musamman Wanda zai fad'akar, ya nishada...
40.4K 901 9
I am Elizabeth Swann's older sister. I was the only one who ever fell for Norrington. This is the story of how we came to be. Our story is one of lov...