🍒SOYAYYA MAI GARƊI🍒🍒*
_(Pure Love, Revenge and bargaining)_
By
*Siyama ibraheem🍒*
Wattpad@siyama Ibrahim
'''DEDICATED TO SURAYYAHMS'''🐈
1⃣1⃣
Da zuwa na ajin mu na fara shiga na zauna har lokacin yin assembly ya kai na fito ban ga su salma ba abin ya dame ni matuka duk a zato na koh latti suka yi nai ta saka ido amma shiru har muka gama muka koma ajin mu class teacher din mu ce ke fada mana wai ai an yi rasuwa gidan su falmata wani kanin ta ne ya rasu jiya da dare shi yasa basu zo makarantar ba yau
Kawayen su na ta jin tausayin su ciki har da ni da muka hadu jiya
Class teacher ce ta ce mana kawayen su uku su shirya in an tashi break za'a je gidan su da malaman makarantar domin yi musu ta'aziya
Biyu sun fito safiya hafiz da precious Matthew aka rasa wa zai cike na ukun kowa a zaton shi ni zan fito in cike su nikuma gaskiya Abbu ya hana ni zuwa koh nan da chan in ba a cikin makaranta bane
Tunohaka haka ya sa nace musu ni bazan je ba in an tashi zamu tafi ni da baba na sun ji mamaki ganin yanda muka saba sosai a jiyan amma in ki zuwa gidan su gaisuwar rasuwa a karshe dai da su su biyun aka yi tafiyan dan babu wanda ke son zuwa saboda bala'i irin na su salma da falmata (yarinta kenan a ce an rasa rai ana son ayi aikin lada amma kowa ki yake yi wai saboda wani kankanin dalili Allah ya sa mu dace)
Ana tashi break suka tafi ni dai Allah ya sani naso tafiya amma ina tsoron Abbu ya zo ya ji cewa na bar makaranta ba tare da izinin shi ba
Da suka dawo ne safiya ke gaya min wai ai sun ce a ce min sun yi fushi ban je gidan su tsakani na da Allah sai na fara kuka sabbin kawaye na sun yi fushi da ni toh nikuwa yau sai na tayar ma Abbu da rigima mun tafi gidan rasuwar in ya so na sami hanyar kubuta daga zuwa makaranta
Tunowa da nayi da wannan idea din ne ya sa na yi murmushi nace ma safiya
"Ai zan tafi gidan su in an tashi daga makaranta"ta ce toh
"Amma kin san gidan"
Na ce a'a ki gaya min sai ta ce min a ta federal housing gidan yake kenan kusan wuri daya muke tunda mu a 2/1 market muke su kuma kafin a zo nan anguwar mu suke
Malaman mu sun shishigo kuma duk wanda ya shigo sai ya kira attendance wanda ya sa duk wanda aka kira sunan shi sai ya tashi ya amsa toh ta nan na kalle yan ajin namu daya bayan daya ban dai rike sunayen da fuskokin duka ba amma na san wasu
Mun tashi a makaranta kamar jiya muka fito bakin gate in da muka jira Abbu jiya yau ma a nan muka jira shi da ya zo sai na gaishe shi na gaya mishi abin da ya faru yau wanda aka gaya mana a makaranta
Sai yace
"Toh mama na ya za'a yi yanzu kin ga anjima akwai Islamiya"
Ai tunowa da nayi da yaran nan sai kawai na hau dadaga Kafa akan ni dai mu tafi gidan su salma saboda suna so na
Kallo na Abbu yayi shi dai ya san ban da rigima bayan surutun tsiyan da nake da shi sai gashi yau ina gwada mishi rigima karara
sai ya ce mama na toh na ji zamu tafi amma ke kin san gidan ne?
Da murna nace ai safiya ta ce min a federal housing su ke
Ya dan tsaya na wasu yan mintoci yana nazari idan dai bai manta ba toh federal housing angwar masu hannu da shuni ne toh ita wannan a ina ta samo kawaye masu kudi haka
Da naga shirun yayi yawa na dauka fasawa yayi sai kawai na saka kuka
Ya yi saurin dago kan shi yana tambaya na lafiya
Na ce "Abbu ba ka fasa zuwa da mu bane kuma ka ga hasina kanwar salma kawar ummi ce toh kuma Abbu sai ka ce baza mu tafi ba" na cigaba da kuka
Abin ma mamaki yake ba Abbu sai ya ce
"Mamana taho kumu tafi gida in kun ci abinci sai mu tafi koh da zuwa karfe biyar ne na yamma
Tsabar rashin hakuri irin nawa sai na tare shi ta hanyar cewa
"Abbu har sai dare yayi kafin mu tafi ni ni nidai"
Na bashi dariya sai yace mamana ai saboda bana son kuyi fashin islamiyar ku ne yau kinga in na kai ku sai in yiwa malamin ku magana koh da 4:30 pm ne sai mu tafi chan gidan nasu koh ya kika gani??
Nikam tsoron zuwa islamiyar nake ji amma na san idan zan fada cewa zai yi saboda zuwa gidan nake karya alhalin ba hali na bane haka dai na yi gumm ban kuma cewa Komai ba har muka kai gida ni da ummi mun gama komai muka kama hanyar zuwa Islamiya a daidai gate din makarantar nafara tsorata amma na yi shiru har dai na shige ajin ina dar dar
Inda Allah ya taimake ni shine yau basu zo ba dama wai sai an kawo su makarantar in ba haka ba ba zuwa suke yi da kansu ba toh da naga basu zo ba sai na sake jiki na nayi bitar karatun da aka min jiya malamin ya kara min
Ana tashin mu sallar la'asar Abbu ya zo daukan mu dama ya ma malamin makarantar bayani da zuwan shi da kawai muka wuce
Da zuwan mu gida na yi sallah na chanza kaya na duk sai doki nake faman yi
Abbu na ta farinciki na fara walwala na sami kawaye
Muka fito muka tafi bakin titi inda muka tsare a taxi ni na gaya ma mai taxin inda zamu tafi ya fadi kudin kafin ya ja mu muka tafi sai federal housing a daidai nan ya sauke mu yace mana mun kai muka firfito Abbu ya biya shi kudin shi
Sai kuma aka bar mu da kame kame saboda wurin dai kusan zan iya cewa shiru yake da kyar muka sami wani yana tafiya a hanya muka tambaye shi gidan da akayi rasuwa jiya sai ya ce mana mu yi tafiya zuwa karshen layin sai mu yi kwana toh akwai gidaje a wurin sai mu duba gida mai lamba 44 a nan aka yi rasuwar
Muka mai godiya muka tafi da kwatancen shi muka iso gidan wanda yake gida ne na masu kudi dan babba ne ga kyau mun bata lokaci sosai kafin a bar mu mu shiga gidan har mun cire ran za'a bar mu mu shiga
Ko da muka shiga sai muka ga fanni biyu mun rasa wanne ne zamu shiga aiko sai ga hasina kanwar salma ta fito daga daya fannin tana hango ummi ta zo tana ta kiran sunan ta wai tazo su tafi kafin su bar wurin sai ga wasu maza sun fito kusan su biyar suma din ta'aziya suka zo yi a nan ne Abbu ya tsaya suka gaisa da su ya musu ta'aziya sai ya ce musu ai yar shi ce ta ke gaya mai rasuwar da mamaki suka ce wacce a ciki sai ya nuna musu ni yace ai makarantar mu daya da su
Sai daya a cikin su yake cewa
"Ai jiya da yaran suka dawo basu bar su sun huta ba sai labari suke yi wai sun yi kawa a makaranta jiya sunan ta Aisha Murad"
Abbu ya yi murmushi sai mutumin ya raka bakin shi kuma ya wa Abbu bismillah zuwa ciki muna shiga ya sa aka kira wata mata wacce da ka ganta ka ga falmata domin kamanin nasu har ya baci da ta iso sai mutumin ya ce
"Hajiya ga baki nan mun yi sun zo ta'aziya ne kuma wannan ita ce kawar su yaran nan da suka ce sun yi jiya a makaranta"
Matuka matar ta ji dadi don har take kara godiya kafin ta ce in zo mu shiga suna ciki
Tafiya muka yi su kuma su Abbu suka cigaba da magana a nan Abbu ke sanin cewa shine mahaifin mai rasuwar kuma baban falmata har yake gaya mishi ai shi dan asalin maiduguri ne a wani yanki mai suna Gonin goza kasuwanci ne ya kawo shi nan shine ya samu uban gida mai mutunci da daraja dan adam har ma ya bashi wani matsayi a ma'aikatar shi ya jawo shi ya hada da iyalin shi ya kuma bashi yarda da aminci
Sai yaba mai yake yi ya dora da cewa ai falmata ce yar shi ta biyu akwai babban yayan ta da ke karatu a wani makarantar kwana na sakandire a cikin Abuja sai falmata da kuma kanin ta da Allah ya ma rasuwa a jiya wanda ba zai wuce shekaru uku ba zuwa hudu
Abbu ya dada yi mai ta'aziya shima ya bashi labarin cewa ai shima dan maiduguri ne ya gaya mai komai da ya faru da shi da yanda ya zo nan ya kafa kasuwancin sa
Shima ya mai jajen abin da ya same shi yake tambayar shi toh ina maman su Aishan
Sai da Abbu ya dan yi shiru kafin yace ai ta rasu tun ranar da ta haifi farida wanda wanda wanda sunan ta aka mayar ma yarinyar
Da tausayi baban falmata yake kallon Abbu ya ce Allah ya jikan ta haka dai suke ta tattaunawa akan sha'anin rayuwa
Mu kuwa da muka shige ciki dakin su direct aka kai ni da shiga na kawai sai suka fasa ihu sun ma manta rasuwa aka yi (yarinta kena)
Muka rungume juna suka fara min surutu wai me zan ci a kawo min na ce ba kai suka bata fuska su a dole sun yi fushi sai na ce toh a kawo min koma menene salma ce ta fita ta dawo da abinci a babban tire da cokula wai mu ci haka muka zauna muka ci tare sai annishuwa muke yi sai suka tambaye ni halan me yasa ban zo ba da yan ajin mu suka zo
Amsa na basu da ai tare da Abbu muka zo kuma shi ya hana ni yawo in ba tare muke ba shiyasa ban zo ba dazu sai na ce ai har da ummi muka zo amma sun shiga wani wuri ita da hasina
sai suka ce ai dakin su suka tafi a nan dai muka sha hirar mu salma ke ce min ai su Abban ta sun yi tafiya tare da umman su kenan ragamar gidan a hanun baban falmata yake muka sha hirar mu kamar kar mu rabu sai ga maman falmata ta shigo kira na wai in zo mu tafi
Suka rako ni har falon inda suka gaida Abbu sai ga su husna ma sun fito haka muka rabu akan zamu hadu gobe a makaranta ni har ma na manta da maganar yaran islamiyar mu da nake so in gaya musu har mun yi nisa na dawo na gaya musu ai ko suka ce in Abban su ya dawo zasu ce mishi ya dawo da ni makarantar su su dai iyayen mu na ta jin mamakin shirmen mu da haka muka tafi gida
Pls manage walahi schedule dina na yau is very tight ne hope zaku karbi uzuri na
_*🍒s,ibraheem🍒*_