TAFARU TA K'ARE......Anyiwa m...

By 68Billygaladanchi

172K 15.1K 1K

"Mesa kake ambatar mutuwar nan wai, idan akan nace banasan kane kayi hakuri ina sonka wlhy, fiye ma da tunani... More

page 1
page 2
page 3
page 4
page 5
page 6
page 7
page 8
page 9
page 10
page 11
page 12
page 13
page 14
page 15
page 16
page 17
page 18
page 19
page 20
page 21
page 22
page 23
page 24
page 25
page 26
27
page 28
page 29
page 30
page 31
page 32
page 33
page 34
35
page 37
38
39
page 40
page 41
page 42
43
page 44
page 45
page 46
page 47
page 48
49
page 50
page 51
52

page 36

3.8K 304 13
By 68Billygaladanchi

*🙆🏻🙅🏻TAFARU TA KARE🙆🏻‍♂🙅🏻‍♂....Anyiwa me dami d'aya sata.....*

*Billy Galadanchi*

*Haske writer's Association*

*Sadaukarwa ga Ameena jibril muh'd(Slimxy).*

  Wattpad 68billygaladanchi.

                36

---------------------
       Zainab ce ta fara zuwa akai mata gwajin DNA d'in, ta dawo ta kafe kaman ba komai ta adana result d'inta ta kuma barwa asibiti nasu ta dawo abinta, daganan sarki ya shirya ya shirya tafiyar sa da matarsa da uwarsa da harma da waziri aciki, haka sukaje binciken lafiyar su haka kurun se jikin gimbiya ke bata akwai wani abu amma ya zatayi batada zab'in daya wuce ta kame  bakinta tunda yake inma akwai wani abun itadai batasan ko meye ba, tunda yake sharrin dasuke k'ullawa mafiya yawan Abdurra'uf be san dashiba, haka dai akai kusu gwajin harna ciwon sugar da komai ma kan daga bisani su juya masauki.

   Tun shigarsu hotel d'in nan idan khamal system yana kansu, burinshi haris yae dabarar dayace komai ya kammala, yana nan tsaye a harabar hotel d'in har k'arfe goman dare harma ya sare seya tsinkayo su susu biyu wato waziri da haris driver, komawa yae kusada motar su ya watsa wannan powder aciki dama haris ya barmasa ita abud'e ne akan da zaran sunzo shiga kurun zasuyi zuwa time d'in shi kuma seya d'an tsagaita basaso shi powder ta kamashi, Suna zuwa ya bud'ewa waziri gidan baya ya shiga tsaigon zagowa seda aka d'anyi some seconds koda ya zago ya bud'e gaban motar seya toshe hancinsa da hanky, ya lek'o gani yae wazirin sharkaf yae bacci, fita yae ya d'aure fuskar sa ta wurin hanci yanda abin baze buge shiba sannan ya shiga ya tashi motar direct zuwa inda aka umarcesa yakai shi, kusan time d'aya suka isa da khamal system, tare suka kwashe da Haris zuwa cikin gidan, seda sarki ya zauna sosai sannan suka tashi waziri da abin tayar da mutane idan an shaqa musu wancen abun tare da sanya haris baccin k'arya dankar a zargeshi akan wani abu. A razane ya farka ya soma kame kame beko kula da sarkin ba seda Kamal ya sanya rufaffun takalminsa ya murje masa yatsunsa k'ara ya k'wallah don azaba ya janye hannun ya kalli inda haris yake kwance sannan ya soma rarraba idanshi zuwaga mutanen dake palor d'in d'aya bayan d'aya cikeda tashin hankali idanshi na sauka akan SARKI JALAL ya zabura ya mike ya soma salallami, k'afarshi kamal ya bige ya fad'i agun ya wankesa da lafiyayyen mari

"Kai ka nutsu agaban sarkin gaskia kake tsohon munafukin Allah" khamal ya fad'a yana me k'ara murza manya manyan takalmin sa akan yatsun k'afar ta waziri, rasa me zeyi yayi yahau kiran sunan Allah murmushi irin na manya Sarki jalal yae kanyace

"Waziri gani kuke kamar kullum duniyar a hannunku take ko? Gani kuke kamar Allah baze tab'a kub'utar dani ba ko? Gani kuke kamar kunshige agabana kummun zarrah ko, to kunyi kuskure kaida Gimbiyar Rusau kun tsokalo tsuliyar dodo, shekaru 33 dakuka azabatar dani kai sena azabtar dakai acikin kwanaki uku kacal, ko yanzu sak'o ne zan baka idan kaje masarauta ka gayawa sarauniya hassy nace Ina gaisheta itada gimbiyar Rusau ka kuma sanar musu cewar nace Nanda d'an lokaci k'ank'ani zanzo domin na karb'i mulkina, bokan su dasuke cewa zezo ya kasheni ka sanar dasu nace sun manta da littafin Allah ne? Dashi nake tak'ama kuma duk dare bacci na nake shak'a sabida nakanyi adu'oin tsari ubangijina yana tare dani daga k'arshe ka sani wlhy ka kawomu  zobuna na!!! Idan har ka bari kwana uku tacika bakaje ka kaisu wurin hajiyar kilisa ba sena kashe ka, kayi wani yunk'uri akaina kasha wahala mahaifiyata ma tana k'ark'ashin kulawa me yawa krkace zakayi wani garaje" Murya na rawa waziri yace

"Base naje cen ba kullum suna hannuna gasu nan ranka ya dad'e bari in cire maka su in bayar yanzu dan Allah karka kasheni" Murmushin yak'e Sarki Jalal yae

"Cire ka ajiye, sannan idan kaje gida ka sanarwa Sarki Abdulra'uf ina gaisheshi" Da sauri ya kalleshi cikin tashin hankali dariya yae

"Bazaka iya fad'aba? Sabida kasan zece ka kawoshi nan kuma kaima bakasan ina ne nan ba" Waige waige ya shigayi kan yae wata magana har kamal ya shak'a masa hanky atake ya k'ara zubewa wurin a sume, zobunan sarki suka cire suka caje aljihunsa kai tsaye suka zare wayoyin sa da wani tsohon carbi da sarki yasanshi dashi tun suna yara yana mamakin waziri me yake da wannan carbin ta mugun ta..haka suka kwashesu shida driver khamal ne yaja motar duk suna baya yakaisu harabar hotel d'in ya ajiye motar yae tahowar sa.

    Haka Haris yae taku ya shafawa waziri abinda ze dawo dashi hayyacinsa shi kuma yae saurin lafewa koda waziri ya farka ya ganshi amota shida haris seya kid'ime ya kwashe shi zuwa masaukin su dama kowa da nashi abokin kwanan, tunda yake sarki yana tare da sarauniya shi kuma yana tare da haris koda haris a parlor yake shi yana kurya se mahaifiyar sarki da kuyangarta itama. Haris ya seda ya nak'alci anyi fin awa sannan ya motsa da waziri ya fara cin karo yanata faman had'a gumi ya mik'e cikeda tsoro

"Ranka ya dad'e wazirin wazirai, ya akayi muka dawo d'akin? Mun fasa tafiyar ne?" Girgiza kai waziri yae

"Baccine ya kwasheka sena hak'ura kawai,ganin baze yiyu muje kana baccin ba,ka manta dana tasheka mukazo d'akin,ai kana shiga motar se bacci shine na tasheka mukazo d'aki" Jinjina kanshi yae yana me zubewa a k'asa

"Ka gafarceni Shugabana ban kyauta ba wataqil faruwar hakan baya rasa nasaba da tsantsar gajiyar dake jikina ina neman afuwa" Murmushin yak'e yar

"Ba komai haris ka kwanta abunka ai kanama k'ok'ari" godiya yae yaci gaba da kwanciyar sa, ya gano waziri so yake ya adana wannan sirrin sabida yasan sarki Abdura'uf besan da zancen b'oye d'an uwan saba sam!

************
   Meenal se zagayen gidanta takeyi tana neman abinda zataci kafirar yunwa takeji, Malmo ta gani a  kitchen

"Malmo me kikeyi ne?" Kallonta tae sekuma ta zube ta sani yanada wahala ka ganta a kitchen d'in

"Ranki ya dad'e Sawun Takawa, Takawa ne ya buk'aci in Masa farfesun naman kai  kafin ya dawo, tona idar shine kuma nake kwashewa" Washe baki tae

"Zubomun me yawa a bowl ki had'o da fresh milk a fridge" juyawa tae batare data jira amsawar malmo be, zuciyarta ke tashi warin abincin ne duk taji bataso amma tana kwad'ayin abincin. Haka taje bed room ta baje a k'asa tana jiran akawo mata hadda ajiye tissue da tsinken sakace, da sallama malmo ta shigo ta dire  mata farantin agaban ta komai yana kai da sauri ta toshe hancinta

"Malmo dandai inajin wata uwar yinwa ne dabazanci abincin nan ba, kinsaka masa wannan spice d'in na indiyawa dayake nacewa ni bason warinsu nake ba wlhy" cikin girmamawa tace

"Babu abinda na saka daya dangancesu se kayan mu na gargajiya" Nisawa tae tana toshe da hancinta ta d'auki d'aya ta soma ci haka ta dinga cn abincin hancinta a toshe malmo ta tasata a gaba se mufmushi takeyi dankuwa ta soma hasaso wani abu daga wurin uwargijiyar ta in haka ne tana murna matuk'a

Takawa ne ya shigo d'akin da sallamar sa fuskar nan a matuk'ar d'aure yau sarautar yakeji bako k'arya, kallo d'aya malmo ta masa ya wurga mata mugun kallo

"So nawa zanyi hani akan kallo na? E ban gaya muku ba karna kuma ganin idan ku a nawa ba?" Ban Hakuri tashiga yi amma ko k'ala be sake ce mata ba seda Meenal ta sauke d'ankwalin dake hancinta tace

"Ke tashi kije" sumsum tabar d'akin k'irjin ta yana dokawa rabon dataga uban gidansu a irin wannan yanayin harta manta sam! Halin ya motsa kenan, zama yae kusa da ita amma akan gado ya d'aura k'afar sa d'aya akan d'aya yana wani k'ara had'e fuska k'ala bece mata ba itama kuma ko kallon inda yake batayi na, seda ta cinye naman kan tatas sannan ta k'wallawa malmo kira, tazo ta tattre kayan

"Ki tabbatar kin sanya turarukan wuta masu k'amshi agidan nan banason warin wannan farfesun dakikayi" Kanta a k'asa ta amsa da

"An gama Sawun Takawa" ta juya ta fice toilet taje ta wanke hannunta da Abin wanke hannu ta wanke bakinta ta fesheshi da mouth freshner ta dawo d'akin, k'amshin farfesun ya daki hancinta da sauri ta toshe da hannunta sannan ta kai hannunta kan mirro tashiga feshe d'akin da freshner har kala kusan 5 ta saka sannan ta sauke hannunta har yanzu akwai alamun k'anshin, tsaki taja tana mamakin wannan abin, idan ba barin d'akin tae ba tabbas seta amaye 'ya'yayen hanjinta, Anan ta barshi zaune zuwa d'ayan d'akin dayake mallakin sa ta shige abinta... Haushinta dukya isheshi wato bazata iya gayar dashiba kenan? Yayi saken da Meenal ta gama rainashi mik'ewa yae ya nufi d'akin yana tunanin cen ta tafi, kwance ya taradda da ita da remote control guda biyu, na farko dai AC ne tana rage k'arfinsa sabida yana mata yawa na biyu kuma na reviever ne tana k'ok'arin tsayar da channel d'aya na india ta kalla, zama yae ya k'ara hard'e k'afafuwan sa wuri d'aya yana kallonta amma ko gezau yima tae tamkar bata tab'a ganin saba

"Me kenan kikeyi Haka Ameena? Kina ganin nashigo cikin d'akin bazaki gayar dani ba?"

"Ina wuni yi hak'uri na manta ne" Shiru be k'ara kulata ba, tace

"Danla d'anzo mana in kwanta a jikinka inyi bacci, kasan baccin zemun wahala idan banji k'amshin jikinkaba" kallonta yae ya k'ara had'e fuska

"Bawan gidanku neni dazan zauna duk zakiyi bacci se'a jikina? Ko an gaya miki banida abinyi ne? Inada sabgogin yi seki zauna ke kitayin baccin" B'ata Fuska tae

"Allah kaima ya d'oro maka sonjin k'amshin jikina yasin wlhy bazan bari kajiba" Yanaso yae murmushi amma yau 'yan mazan zuciyar su batada dad'i, basarwa yae ya d'auke kanshi  gefe d'aya daga bayama seya bar d'akin gaba d'aya, kuka ta saka ganin baze k'areta da komai ba ya sanya ta tashi tashiga toilet d'inshi cikin laundry basketa nashi ta lalubo singet daya cire taje dashi ta rufe fuskar ta ba laifi k'amshin ya rage mata zafi, mamakin takeyi yanda take kasancewa bata son warin komai sena Takawa har akanshi ta kula yana mata wulak'anci.

  Bata farka ba se wuraren biyar na yamma, sallah kurun tae ta sakko neman abinci jikinta har rawa yakeyi, Yanzun ma kitchen taje tuwon miyar kuka akayi da man shanu, haka ta zuba da kanta ta zauna anan parlor toshe da hanci yanzu ma taci abincin se masifa takeyi akam suna saka abinda bataso a binci, da dare wainar fulawa zataci batason tuwon, sunada meeting da Talented Nusy dan haka wanka tae ta shirya sosai taje ta sanya nik'af data danya aka kawo mata da dogon hijab motar da khamal system ya kawo ata ita ta hau tabar masarautar wannan fitar sirri ce dan haka babu wanda yasan da fitar se takawa wanda akan idanshi ta fita kuma tafiyarta kurin ya gane ta, gashi bata sanar masa k'wafa yae yarinyar ta rena shi...

A inda suka zasu had'u anan suka had'u d'in, zama sukai akai system d'aya suna harhad'a wasu abubuwan seda sukaci k'arfin aikin su sannan meenl ta kalli Nuceey

"Talented kinsan wani abu?" Kallonta tayi sosai tana sauraren ta

"Banaso ki k'ara gayawa yusuf idan mun had'u maceceni me yawan son sirri da girmama shi, ban faye son sirri n yana fita ba" jinjina kanta tayi alamar gamsuwa, Meenal taci gaba

"Akwai wasu mutane danake zargi da sanya hannu a kisan Salma, se nake ga kamar ba ka tsaye Sarauniya daurama tayi kisan ba, menene bayanin dazan samu na qarin haske game da wannan? Senake ganin kamar aikin Tarayya ne na had'aka tsakanin wasu miyagun mutanen banda ita, sunyi tunanin cewar baza'ayi Walk'iya kowa ya gansu ba sun yiwa abun Rainuwar kama kuma tana gaf da faruwa kuma ta k'are musu a hannuna" Nisawa Nusy tae

"Kamila da zayyad sune mak'iyan Takawa na b'oye, amma sufa ba takawa kawai ba har yarima fu'ad so sukeyi su kasheshi su kashe sarki inyaso dole shi zayyad shi kad'aine magajin daze na sarki Mu'az wanda dole abashi sarautar garin, sabida shi d'an k'wark'warane matar sace kamila, muguwa irin sa, suna nan masarautar nan, tabbas Sarauniy daurama ta tura akashe mata salma sedai ba kisan d'aukar rai ba, kisa ne ta tura a mata na nak'asa wa, itace ta sanya aka kunce burkin motar ta ai idan zaki kula accident din batada yi nisa da barin gidaba akayishi sabida a abuja suna sakewa sosai, ita so take Takawa ya auri 'yar k'anwar ta, ni aikina kurin na duba musu sanda takawa yake nan da sanda ya bata umarnin fita ne ita kad'ai, kuma kwanansu d'aya jal da dawowa daga london abun ya faru, khamila da zayyad sune sukaje har asibitin suka yiwa jinin da aka sanya   mata allurar poison dazata kasheta slowly ni kad'ai nasan hakan, sabida ni danaje dubata nayi sa'ar d'ana camera ta kuma shi zayyad da kanshi yae aikin, su so sukeyi gabaki d'aya su tarwatsa zuri'ar Takawa data gimbiya hassy video d'in yana cikin system d'ina ta sirri dake gida zan aika miki dashi kiga komai, dama duka k'afafuwanta biyu sun rabu da jikinta se azabar ya sauka mata akan k'afafun na dafin poison d'in wlhy koni danga video sanda ta mutu na tsorata wannan ne ya sanya ban baiwa Sarauniya labarin komai ba game dasu kamala, yaran da aka kashe a masarautar baraya ma ba kashesu Daurama taso yiba, ita aikinta tanasone su nak'asa, maganin da bokan yabata yace ne zasu yi ciwo daze shnyar da k'afafuwan su ya kasance bazasu k'ara iya tafiya ba kinga waze baiwa nak'asashe sarauta? Daga nan kuma se abubuwan suka kwab'e. Jinjiraye datake d'aukewa kuwa siyarwa take a matsayin bayi wasu masarautun, a wancen lokacin kenan da bayi sukeda daraja kinga yanzu bayi sunata raguwa sabida wayewar kai sedi hadimai da wasunsu hayar su mukeyi a gidan sarauta shisa zakiga mulki da sarauta sun ragu sosai a wannan lokacin, wasu kuma shyar dasu akeyi idn sun tashi sesu bautu a matsayin bayi mfi akasarin su 'ya'yan sarki mu'az ne, shisa zakiga ta rage yawan bayi yara k'anana duk sun manyanta sabida tin mutuwarsa ba jinjiraye, yanzu hanya d'ayace datake bi mara kyau itace yanda take had'a bayi maza da mata suna yin zina idan akayi ciki aka haihu seta mayar da yaran bayinta dukda yake yanzu bijire mata sukeyi kodan wayewar kan dasuka samu ne oho" Murmushi tae

"Daurama muguwace wlhy, yanzu kinsan me?, zan barki da kuyangarta dan na dasa rashin yarda a tsakanin su ga wannan dubu d'ari biyu ce ki tabbatar kin siyo infor masu k'arfi daga wurin ta, idan taqi ga audio yan da akayi suke baiwa matan sari Mu'az maganin hana d'aukar ciki dan kar a samu magaji, akwai bayani ma na zubarwa Hajjyar kilisa ciki kusan so uku aciki, kuma tsakanintane da wasu bayi take basu labari seki nuna mata zaki kaiwa Sarauniya daurama idan taji zaki iya rik'e kud'in dan nasan setayi wahalar juyawa, ni kuma sarauniya hassy na gama da Asha kuyangarta amintacciya zanci gaba da aiki akanta" Murmushi Nuceey tae

"Kinsan wani abu Meenal?" Girgiza kai meenal tayi

"Ki sani wlhy ban tab'a had'uwa da mutum me kaifin basira ba irin ki, shishigi kurun nawa sunan Talent amma wlhy kece shi, gabaki d'aya yanda kikasan me aljanai idan kina bayanin abubuwa har tsoro kike bani wlhy" Murmushin k'asaita tayi

"Nusaiba kenan, dake kad'aice se'a miki magani ni kaina nikan baiwa kaina mamaki wasu lokutan, amma ya kika iya abunne daga Allah" haka suka rabu tana mamakin qanqanuwar yarinya kamar meenal tafita wayau, ita yanzu ta sakar mata komai kawai.

***********
   Tunda sarki yaga result hankalin sa ya tashi, tabbas buri yayi kama da mutum kenan dai da gasken gaskene cewar da akeyi Bashi ya haifi Fu'ad ba, baze ce dasu komai ba yanzu seya gama sanin hanya mafi sauk'i ta b'ullowa al'amarin dan haka suka tarkata suka juya masarautar a wannan yammacin.

Se bayan magrin meenal tashigo gidan, watsa ruwa tae tai salla tana idarwa tanufi waje neman abinci mugun cinta yana bata tsoro wannan abu har ina, a k'ofar d'akin tae karo da mutum, idannan ya kad'a yayi jajir, baya baya taja ganin yanayin sa kenan ya gano bata cikin masarautar haka har suma isa gun mirror, hannunta ya kamo ya mugun murd'eshi seda ta saka wata uwar k'ara sannan ya saketa

"Ina kikaje baki sanar dani ba?" Narai narai tayi da ido

"Nasan ban kyautaba amma kayi hak'uri fitar ce take buk'atar sirri" kunnenta ya kama ya murd'e sosai

"Amma ke agidanku ba'a gaya miki ba'a fita babu izinin mujiba? Eh wane irin mugun sirrine daze sanya ki fita ban saniba, kega me wayo ko idan kikaci gaba da barin masarautar nan bada izininba wlhy sena sassab'a miki kuma ki sani wlhy idan wani abu ya sameki bazan tab'a gafarta miki ba, yaya kikeso inyi idan bakya raye ya kike neman ki mayar dani k'aramun mahaukaci ne wai? Fitar da kikai yanzu seda akabi bayanki, dabanbi bayanki ba Allah kada'i yasan meze biyo baya" Ganin rik'on  dayawa kunnen ta na mata zafi seta rungumeshi gaba d'aya

"Kayi Hak'uri Abu hidar bazan k'araba i promise, saken kunnen yae shima ya rungumeta, lumshe idanta tae kunnenta da hannunta har lokacin suna mata zafi, amma kuma k'amshin turarensa ya gama da natsalar ta😥, shinshinar k'irjinsa ta somayi tana share k'wallan daya zubo mata asaman rigarshi, itadai taga jarabawa akan son mu'az amma shi tasan baze tab'a sontaba wannan muguntar har ina meta masa? D'ago.kanta yae

"Meenal kiyi hak'uri na miki da zafi ko?"  Ga mamakinta shi d'inma kuka yakeyi

"Idan na rasaki banida wani sauran farin ciki, bansan mesa kikemun wasa da rayuwar kiba, kinsan had'arin masarautar nan da kewaye amma sekikeyin abu wasu lokutan kamar bakida tunani, wlhy bin bayanki akayi, Allah yasa nabi bayanki da excort danaga kin fita ana fahimtar ina biye aka dena binki kinga ke bakima kulaba, yaya zan rayu idan babuke a rayuwata Meenaly na?" Sheshekar kuka ta somayi sosai

"Shine kakecin zalina seka dinga dukana kanamun abubuwan k'arfi, dabakaso wani abun ya sameni aikai ma da bazaka cutar dani ba" Harshensa me taushin gaske ya sanya ya lashe hawayenta yana lasarsu wasu suna k'ara kwaranya abun yana bashi mamaki

"To kiyi hak'uri my meenaly, namiki alqawarin bazan k'araba shikenan?" Tabare fuska tayi

"Nika dakeni ma idan kanaso amma ka dena hanamun jin  k'amshin jikinka, kasan wani abu ne wai, idan banji k'anshin kaba ji nake komai wari yake mun, kuma ni banida lafiya ma ka kaini gun Dr. Banason warin abinci, kuma se intajin yunwa da wuri gakuma son k'amshin kanan, kaga idan na fesa turaren ka amai ma nakeyi, bansan meke damuna, idan naci abinci se adinga sanya guduma da adda ana kwankwatsar mun kaina se nayi bacci na tashi yake denawa sekuma in k'ara jin wata yunwar" Murmushi yae

"Kiyi hakuri zan gayawa Dr. Har maganin kanshin nawa seya baki ko?"

"Tokuma kaga ina yawan yin fitsari kuma se inajin kamar jiri jiri, nidai kawa banida lafiya komai ciwo yake mun wasu lokutan" Nisawa yae

"Base kinje gun likitaba, zan gaya masa wannan bayanin seya baki magani"

"Idan ze bani magani banda Panadol sabida inata shanshi amma ban dena jiba" waro idanshi yae waje

"Panadol kuma kewaye ce kish to, karna k'araji ko paracetamol kinsha" kallonshi ta tsayayi

"Mesa?" Shiru yae bayas ko kad'an ta fahimci tanada ciki

"Ance yanada side effect kurun ki  dena" Jinjina kanta tae sekuma ta lafe a k'irjinsa

"Takawa hannuna da kunnena sunamun zugi sosai fa" hannayensa ya d'aura a bayanta

"Sannu zona hura miki kunnen kinji" kwantar da ita yae ya d'are kan gadon ya shiga hura mata kunnen ta daniskar bakinsa me sanyi se lumshe ido takeyi

"Dan Allah kacewa Driver yaje ya siyon kaza gashashiya da tsire" murmushi yae

"Yauma kazar d'aya zaki cinye ne ogar ci?" Turo baki tae

"To ai nima bansan meye alak'ar tawa da kaza ba, yauma zan kira mom in gaya mata halin danake ciki, ko ulcer nane ya tashi" Da sauri yace

"Kaikakai karma ki gayawa kowa, yanzu za'ace waye waye, kiyi shiru da bakinki indai cin kaza ne meye aciki kullum zansa akwo miki me zafi ko k'waya nawa kikeso base kin gayawa kowa ba" D'an kallon sa tae mesa yake tattarewa ne akan zata gayawa wni? Batae magana ba dai ta kawai da kanta gefe kurun, Bakintane ya d'auki hankalin sa zuwa gareta, fake ya mata tai murmushi "Meenal zansha" ya furta cikin wata murya dabe saba yi mata magana da itaba kallonsa tae

"Mene?" Da yatsanta ya nuna mata, bakinta da breast d'inta

"Wannan zansha da wannan"Tafukan  hannayenta ta saka rufe fuskarta

"Ni bakajin kunyane waikai" tafad'a har lokacin bata bud'e fuskar taba, hannunsa ya d'aura kan breast d'inta da sauri ta bud'e fuskarta rik'e masa hannu

"Dan Allah kayi hakuri ma...." Saukar bakinsa a wuyanta ne ya dakatar da komai wani yarr taji ajikinta...ya dagulawa 'yar baiwar Allah lissafi gaba d'aya ya warware mata, tayi azamar mik'ewa tsaye ta tureshi, rik'ota yae yakai hannunsa saman waist d'inta, cikin wani salo ya shafi bayan nata zuwa k'asan mararta lumshe idanta tae ya k'ara sumbatar wuyanta abinda ya sanya ta bank'are masa gaba d'aya, murmushi yae

"Yarinya ashe kin girm yanzu" turo bakin ta tae dukda abinda takeji

"Ka bari in tfi yunwa nakeji" Idanshi ya kafeta dasu ita kuma ta gaza sanya nata a nashin

"Ki rantse nida abincin wa kika fi buk'ata a yanzu?" lumshe idanta tae sabida salon dayake mata a bayan k'eyarta cikin sumar kanta

"Haba mana Abu Hidar dan Allah ka bari" wata 'yar siriryar dariya yae jinda yae muryarta ta sauya yace

"Iyyey 'yan matan Mu'az an san dawan garin, irin wannan muryar haka" Shagwab'e fuska tae

"Takawa dan Allah ka bar..... Saukar bakinsa asaman k'irjin tane ya kuma katse hanzarinta, da k'yar ta had'iyi yawu, ta kasa cewa komai illah kalmar "Assh" data sub'uce daga bakinta da batasan sanda ta furta ba, murmushi yae ya k'ara rik'ota

"Yau maganin tsiwar nakeso nayi inga tsiyar" Tabare fuskar nan tae amma batace komai ba, iska ya hura mata a kunnenta na dama me d'umi, take ta nemi zamewa ta fad'i seda ya rik'ota da sauri

"Kinga karki wani Fad'i anan ni bawai iya d'aukar ki zanba, jeki abinki" ya fad'a yana sakinta, kwanciya tae ta nad'e gu d'aya jin datai marar ta ta had'e wuri d'aya ita cewa ma tae period ne zatayi dama lokacin yinshi yayi. Zama yae kusa da ita

"Amfasa yunwar kuma konaje na karb'o miki da kaina ne?" Girgiza masa kanta tae alamar aa

"Mesa zakice kin fasa ci to?" Cikin kasala ta furta

"Cikinane ya d'auremun gu d'aya, banasan komai yanzu" Tausayinta yaji yasani shine yaja mata, kwanciyar yar ya rungumeta ya shiga shafar jikinta cikin sigar rarrashi daganan zance ya sauya lokaci d'aya ta bada kai bori ya hau🤗🤗🤗.

************
      Shirin tsaf Sarki Abduljalal yae cikin shiga ta kamala ya ziyarci masarautar shirin dama sun yishi shida su Takawa, tare da Takawa sukaje dan haka iso a gunshi be musu wahala ba dukda yake bayan isha suka je, yasha nad'i sosai daba kowa ne ze iya shaida shiba, Sarki ma dasuka zauna be iya shaida yayan nashiba, seda suka gaisa sannan Takawa yace

"Ranka ya dad'e me garin ne yazo ku gaisawa Takawa me masarautar Hankaka kafin ya b'ata abaka rik'on" Murmushi yae

"Takawa kenan, a tunanin ka zaka rud'eni da wannan maganar? Ka sani niba yaro bane kamar kai, ko kanaso ko bakaso ni ubanka ne, kuma base ka b'ullo da kawo Mutumin k'arya a matsayin sarki me b'ata ba, idan yanzu kace sarautar ka kakeso wlhy bakoja zan sauka in baka abarka dama lokaci nake jira kuma gashi ka isa ka kawo ka mulki wannan  masarautar" Murmushi Takawa yae yace

"Abba daka sauke wannan rawanin dazefi sauk'i agaremu baki d'aya" hannunshi ya sanya ya kunce rawanin kanshi tas har hular ya zame😲, wara ido sosai Sarki Abdurau'uf yae cikin tashin hankali ya furta

"Jalal kaine?" Murmushi kurun Sarki Jalal yae shi kuma Sarki Ra'uf ya janyo hannunsa ya janye rigar sa, tabbas wannan d'an uwan sane ga tabo nan dashi ya masa shi dan kuwa mussa shi ra'uf ke tsoron jalal yaje garin kareshi ta yayyageshi, baze tab'a mantawa ba ga kuma na goshinsa daya goyashi suka fad'i a tare ya fasa goshin, rungumar sa yae ya saka kuka

"Yaya jalal na nemeka kamar babu gobe, nayi kukan rashinka yaya jalal, narasa abokin shawara, rayuwata tashiga rud'u da firgici akan rashin ka, wlhy Allah ne shaidata har kawo yanzu ina neman ka, ina rok'on Allah koda mutuwa kai ya kawomun wanda ze bani labarin mutuwar ka konaji sassauci, Jalal masarautra ba dad'i kowa mugune kowa kansa kurun ya sani" Rungumeshi shima yae

"Duk nasan hakan Ra'uf ka nutsu masarauta akwai masu jinka suna ganinka har hanji, wannan ziyarar sirri ce, banaso kowa yasan nazo lallai ka kame bakinka, nazone muyi wata magana me muhimmanci dakai" Nutsuwa yae suka samu doguwar tattaunawa data d'aukesu fiye da sa'o'i Hud'u.

**********
    Zaman Fada ake kowa yayi mamakin ganin Takawa a fada, dankuwa an sani baya zuwa seda muhimmin abu, dukda kasancewar muk'aminsa me matsayi sosai sam baya zuwa sedai shi sarkin yae aikinsa yae kuma na Takawan gaba d'aya, bayan an gama zayyano bayanin komai da komai daya shafi fad'a se sarkibya sako zancen son ya baiwa Takawa kujerar mulkin sa akan dama shiyakeda gadonta kuma gashi ya kawo yanzu, ya girma ya isa dan haka shi zeyi murabus!!! Zukatan mutane da yawa sun girgiza hankula sun tashi zuciyoyi sun raunana, take aka soma yin musu inda manyan fada sukace tunda ba tsufa yae ba kuma ciwon komai ne dashi ba bazasu barshi yae murabus ba, aikam yace dama rik'on k'warya yake, me kujerar be dawo ba kuma yanada magaji, sukace ai shima yanada gadon sarautar da ace bashida gadon tane, dama Takawa ba kowa ke sonshi ba, sarki dai kam ya kafe akan wata asabar ze bashi sarautar sa shiya huta, hatta magajin gari wato Yarima Fu'ad seda ya girgiza kowa da mugun nufin da yake k'unsawa akan takawa, haka taron fada ya watse zuciyoyi na komai se mugun b'acin rai!.

***********
   Wata iriyar zuface ta tsatsafowa sarauniya hassy itada hajiyar Rusau, bazata yarda a wargaza mata shirin ta na shekara da shekaru ba, shekaru kusan arba'in take shirin ganin tayi yanda take so a masarautar yanzu seda aski yazo gaban goshi sannan  kuma ace wai duk efford d'inta ya tashi a banza, takan Meenal zata fara, wlhy seta d'agawa takawa hankali daga bisani kuma ta kashe su su dukansu kowa ya huta, Gimbiyar Rusau ma birkicewa tae taje take gayawa d'anta idan yae murabus seta tsine masa, shi yanzu kowa ma mamaki yake bashi wlhy.

//////////////////
   Meenal k'urawa Mu'az ido yae tana nazarin sa ta kula yau duk sukuku ya wuni, batasan meke damun saba, seda ta gama nazarinsa sannan tace

"Yayana menene yake damunka wai? Tun safe kake d'akin nan ba inda kaje, kuma sukuku nake ganin ka ko maganar ma yau ba'amun" murmushin yak'e yae

"Bansan meke sanyani yawan fad'uwar gaba ba meenal, tun daren jiya nake cikin yanayin nan, bana cikin nutsuwar kwana masarautar nan, yau inaga mu d'anyi fitar sirri, mu fita k'ofar baya, wacce nasa akamun me had'e da gini na tabbatar kema baki santa ba, acikin d'akin nan take kuma, kuma mu fita da k'afa, muje cen wani hotel mu kwana, haka kurun nake a tsorace" Shiru tad'anyi sabida ita ba lafiya ce da itaba, amma a haka ta amince masa anayin sallan isha suka bi wannan hanyar kowa be sani ba suka fita daga masarautar, basuda labarin ana ganinsu, anga fitowar su dama ido na kansu, dukda shigar b'adda kama dasukayi hakan be hanawa mutanen dake gadin shige da ficen su gane su bane, Haka kuma kai tsaya suka gayawa Yarima Fu'ad shine yae umarni dacewar lallai a kashesu abi bayansu.

Tafiya sukeyi amma meenal ta soma gajiya da tafiya, da haka suka tari a daidaita sahu suka shiga, Suna shiga sun d'auki hanya me adaidaitan ya juyo ya wurgo musu wani farin k'yalle...

Mom Nu'aiym.

Continue Reading

You'll Also Like

36.9K 2.9K 60
Hamza Siddiqui- The new student in the school, whose smile made every girl lose her heart but he is a cold , ruthless and rude demeanor person Fiza...
66.4K 3.7K 79
When shrivi goes home after a long time. Who doesn't have her parents' love and family's love for some reason. She had support from her grandmother...
153K 5.6K 26
فيصل بحده وعصبيه نطق: ان ماخذيتك وربيتك ماكون ولد محمد الوجد ببرود وعناد : ان مارفضتك ماكون بنت تركي !