TAFARU TA K'ARE......Anyiwa m...

By 68Billygaladanchi

172K 15.1K 1K

"Mesa kake ambatar mutuwar nan wai, idan akan nace banasan kane kayi hakuri ina sonka wlhy, fiye ma da tunani... More

page 1
page 2
page 3
page 4
page 5
page 6
page 7
page 8
page 9
page 10
page 11
page 12
page 13
page 14
page 15
page 16
page 17
page 18
page 19
page 20
page 21
page 22
page 23
page 24
page 25
page 26
27
page 28
page 29
page 30
page 32
page 33
page 34
35
page 36
page 37
38
39
page 40
page 41
page 42
43
page 44
page 45
page 46
page 47
page 48
49
page 50
page 51
52

page 31

3.2K 306 18
By 68Billygaladanchi

*🙆🏻🙅🏻TAFARU TA KARE🙆🏻‍♂🙅🏻‍♂....Anyiwa me dami d'aya sata.....*

*Billy Galadanchi*

*Haske writer's Association*

*Sadaukarwa ga Ameena jibril muh'd(Slimxy).*
 
Wattapad 68billygaladanchi.

    31

Adama ce ta jiyo sautin k'arar abubuwa da kuma gunjin kuka, bisa ga dukkan alamu kuma daga b'angaren sawun takawa ne, dan haka da azama ta d'auki hanyar part d'in nasu, kai tsaye d'akin ta shiga da sallamar ta, Mamakin yanda jini ke fita hannun meenal tayi lokaci d'aya ta d'are kan gadon

"Subhanallah dawun takawa meya samu hannunki haka, ya naga d'akin duk kaya a warwaste?" Batace da ita komai ba dai, haka taje ta tattaro jama'ar gidan takawan baya nan ya fice yanzu, dan haka duka nemi taci akaje da ita asibiti, hannun aka duba aka mata dressing nashi, deep cut ne ta samu gashi hannun nan ne me karaya, kai Meenal dai taga rayuwa itakam, koda sukaje gidan bata dena kuka ba, su a zatonsu kukan zafin da hannunta ke mata take se sannu suke mata dukansu, an gyara d'akin tsaf aka kawo mata abinci amma ko kallon sa batayiba, ita gidan ma gaba d'aya duhu yake mata, Niger take so ta koma abunta.

**************
    Nusy yau abun duniya ya dameta gata an kawota wannan masarautar ga Baraya, an ajiyeta batare da ance mata komai ba, ga sarauniya daurama ta mata alk'awarin kisa, hankalinta atashe yake acikin kwana d'aya dukta rame, batada masaniya akan sak'on da akace ita tayi wlhy itakam, batawa kowa message ba, yama za'ayi ta tonawa sarauniya asiri?, Bakin ciki kam ya isheta matuk'a se kuka takeyi.

   Takawa be waiwayi gidan ba se after 9 na daren ranar, be nemi kowa ba ciki kuwa hadda Meenalyn mu'az, zuciyar sa ce ke masa wasu alamu na damuwa da ita yakeso ya k'aryata zuciyar tasa da wannan yae alk'awarin baze k'ara matse mata ba, baya baya ze rik'ayi sabida bayaso yanda jikinsa ke k'aryatasa idan suna tare, ba gangar jikinsa ba xuciyar ma k'aryatasa takeyi,idanshi sesun k'aryata tunaninsa daidai kunnayensa so suke su zauna su saurari muryar Meenal, meyasa ze cuci salma akan hakan? Shi arayuwa ko Salman sa bewa haka ba, yasani wannan sabone kurin ke k'ok'arin shiga tsakanin sa da Meenal badai soba, salma kad'ai yake so baze tab'a had'a son wata dana salman saba, baze cutar da ita a bayan taba, dolene ya nesanci zama kusa da Meenal, Burgesa takeyi, magana idan Meenal nayi seta shagaltar dasu wurin kallon bakinta, Tafiyarta me sanyi tana kashesa, yin tafiyar takeyi tamkar arayuwa sarauta ajininta yake haka yakeso shi dama ce, Besan meke damunsa ba idan idanshi ya tsunduma a nata, seyaji lokaci d'aya jikinsa ya mutu babu abinda yake masa dad'i sama da kwana ajikin meenalyn sa, shifa yana cikin masifa fa, baze tab'a cutar salman saba danma Allah yasa basonta yakeyiba, yaudai juyi kurin 'yan mazan keyi amma bacci ya gagaresu, yau kuma k'aunar kwanciya ajikin Sawun sa yakeyi ita kad'ai zata haifar masa da dukkanin farin cikin dayake buk'atar samu a saman shinfid'ar sa, Lumshe idansa yae, be tab'aji ya kasa bacci ba dan salman sa bata kusa dashi, hasalima sabon sane hakan amma to yu meke damunshi, kenan tsakani daida Allah har k'arfe biyun dare ya gagara bacci akan lallai seya rab'i jikin waccen Meenal d'in? To kodai sabida yawan sha'awar dayakeji ne yanzu yakeso yaje gun mace badai sabida yana meenal bane ba yanaga, Tokuma idan itama ya saba da ita yazo kuma suka rabu yakenan, gwara kurin ya zauna warsa anan d'in, bacci fa ya gagari Malam mu'az har k'arfe Ukun dare, da wannan ya tashi yaje hanyar d'akin Sawun Takawar...!!!!

   Da sallamar sa ya shiga dukda baya tsammanin ganin ta ido biyu kota amsa masa, amma ga mamakin sa zaune take ba komai ajikinta se under skirt dataja har zuwa saman k'irjinta, fitila a kunne tana dafe dakai, dasauri ya taka zuwa inda take ya d'are tsakiyar gadon inda take zaune, hannunta ya sauke daga saman kanta data dafe, yabi idanta data sauke masa a wahalce da kallo, sun kumbura sunyi jajir fuskarnan dake fara k'al tayi pink sosai sekace wacce tasha naushi, kallonta yake ido cikin ido amma ya gagara furta wata kalma, hannunta dake d'aure da bandage yabi da kallo, rik'o hannun yae

"Sunhanallah Little waye ya miki rauni anhannu haka" Lumshe idanta tayi, bazatawa kanta k'aryaba rashin ganin Mu'az ne ya k'ara haddasa mata  ciwon kan daya saukar mata zazzab'in daya hana mata kwana, batasan mesa zuciyar ta take mata irin wannan rashin adalcin ba

"Lil sis menene wai? Kimun magana mana" Bud'e idan nan tayi se hawaye, bazata bada kanta ba wlhy, bazata tab'a bashi damar daze gane tana wani sonshiba har abada, sedai duk abinda son nashi ze mata ya mata

"Flower vast ne ya fad'o mun a hannu ya yankani, tokuma shine ya sakemun zazzab'i da ciwon kai" Tallafota yae ko yanzu harya shagala da kallon d'an bakinta dake d'an tsurut, so yakeyi yae kissing nata amma baze iyaba, babu abinda yake mafarki dama kwana biyu kamar wannan kiss daya mata rannan, kawar da wannan d'anyan tunanin yae a ranshi yace

"Sannu Meenal, shine bakimun waya nazo dakaina na kaiki asibiti ba, waya miki wannan dressing ne" So takeyi ta fara gudanar da shirinta akanshi, bazatayi sanyaba aurenta ya mutu, hannun me lafiyar ta sak'ala a wuyanshi

"Zanfi kowa farin cikin ace kaine ka kaini asibiti ai, banida lambar wayarka tanan k'asar ai my brother da tuni na maka waya kazo kodan in maka rigimar da k'anne kewa yayunsu" Murmushi ya sakar mata

"To gashinan yanzun ma jikinki akwwai zafi sosai, kinsha magani kuwa" Tabare fuskarnan tae

"Yo wane magani zansha bayan kaid'inne baka kulawa da k'anwar ka, ni ambani a asibiti nace bazan shaba sekazo da kanka ka bani" murmushi yae

"Kai Lil shagwab'a kuma zaki fara yanzu ko" turo fuskar ta k'arayi

"Ea mana to ba yayana bane ba, nifa banida yaya agidan mu nice babba se k'aramun k'anina kuma ina ganin yanda friends nawa kewa big bro's d'insu yanzu Allah ya bani kuma ni se ace bazan ba, Allah kuwan har bashi seka biya" Yana kula sosai k'arfin hali takeyi zazzafan zazzab'ine ajikinta, k'ara banna ta yae ajikinsa

"Anty parrot wato kema kin iya surutu da yawa haka ko, daga kallon idanki bakida lafiya amma se zuba kike, yanzu dai ina maganin zan had'a miki sekisha da tea ma kawai sekiyi baccin ki kinji" Batace masa komai ba illa kai data gyad'a masa, da kansa ya had'o mata tea yazo ba musu ta karb'a tasha takuma sha maganin,  kwantar da abarshi yae hadda wani kawo matta lillib'i da duvet, shafar sumar kanta yayi

"Baby sis kiyi bacci kinji, kinga nayi miki adu'a ma, Gud 9ht" Ya fad'a tare da juyawa, rik'o hannunsa tae ya waigo yana kallon ta ta narke masa fuskar nan abun tausayi

"Bro please mana ka kwana anan" Murmushi yae, shima ai da shirin kwanan yazo amma abinda yake kallo gangar jikinsa dake k'aryata sa, sam babu abinda yakeso kamar yajishi yana shafar jikinta yana kuma tsutsar bakinta, cikin kasala yace

"Baby sis karkisa rigima mana, bakida lafiya fa, da asuba zanzo" shushura k'afa tasomayi cikeda shagwab'a

"Nito idan bazama kwanamun ba zan bika cen, nifa bazan zauna anan ni kad'aiba, ciwo ze kasheni" murmushi yae

"To ya isa, taho muje d'akin nawa, kinga nan da sassafe kuyangi zasuso bana san hakan nafison cen dabasa zuwa"

"Nida nake ganin jiri, sedai ko ka d'agani zuwa d'akin naka" Murmushi yae me nuni da uwar rigima ceke ya janye duvet d'in ya d'auketa zuwa d'akin nasa, hannayenta ta sak'ala ta zagaye wuyan sa ta lafe asaman k'irjinsa, lokacin k'arfe hud'u ma tayi, har suka isa d'akin akan gado ya dire ta, shima seya kwanta amma be rab'a jikinsa da nata ba, itace da kanta ta gangaro zuwa inda yake, ta shige masa ajikin nan, bashida zab'in daya wuce yamata maraba dan shima hakan yake so, K'ank'ameta yae gaba d'aya ya manna mata sumba a goshi, haka ita har bacci ya kwasheta, k'ura mata ido yayi yarasa meyakeji game da Meenal, baso bane danshi yasan meye so yasaba yinshi burgeshi kurun takeyi se tausayi datake bashi banda haka ba komai, sedai yasan yana k'aunar d'an bakin nan nata, sumba ya mata a hankali akan lips nata, ya tallafeta gaba d'aya, cikeda nutsuwa suke bacci wanda basu suka farkaba se after 8, shine ma ya soma farkawa da salati abakinsa ya tashi zaune yana mamakin wannan uban lati dasukayi yau zeyi sallah rana tana kallon sa, Be tashe taba danyasan tace masa tana period be saniba ita kwana uku takeyi, dama da asuba take so tayi wanka yau, Wanka yae har yae sallah tana baccin ta, se wuraren 9 ta farka, tasha mamakin time dan haka a gurguje ta d'auki towel d'insa taje tayi wanka tana fitowa kuwa jallabiyar sa ta saka ta wuce d'akinta, lokacin ma baya nan, acen tayi sallah dukta jik'a bandage dake hannunta ita k'aik'ayi ma yake mata.

  Mu'az se wuraren sha biyu ya dawo d'akinsa be gantaba danshi gidan gaba d'aya ya bari, d'akinta yaje ya tarar tana kan computer tana aikin, ga hannu d'aya ma take using, haye gadon yae

"Baby sis how far kin tashi lafiya" Murmushi tae ta rungumeshi had'e da manna masa sumba a kuncin s

"Big Bro, nayi kewar kafa" Kallonta yae yana mamakin maganar ta

"Baby sis da gaske, ashe kinaji dani" murmushi tayi

"Bro zansha ice cream, ni baka sona tunda mukazo garin nan bamuje yawo ba" Rik'o hannunta yae

"Akwai rana a dubai Baby sis, bari yamma tayi, yanzu aikin me kike a system kuma keda bakida lafiya" kallon sa tae da idannan dake shagaltar dashi tace

"Wani abin mamakine nake so in gano a wannan masarautar, CCTV tana nunamun wasu abubuwa da Fu'ad keyi na zargi gaskiya, bansan alak'ar wa d'an nan mutanen dakuma shi Fu'ad ba, bansan aikin dasuke masa ba, sedai na gaza gane yawon dasukeyi tsakanin b'angaren Takawa zuwa nashiba" kallon ta yae cikeda mamaki

"B'angarena kuma kamar yaya?" Murmushi tayi

"Waka baiwa key naka?"

"Bana baiwa kowafa, yana hannuna" Nisawa tayi tana tariyo videos d'in baya,  sunshiga gidan da fitowa yakai so 7, kuma confidently suke shiga da key nasu, yasha mamakin wannan al'amarin,  zuwa yae ya d'akko laptop  d'insa, CCTV's dake cikin b'angarensa ya soma duba videos nasu, dayike dazaran yayi tafiya baya damuwa dabdubasu, sabida yasan ba kowa daze shiga masa, bincike ne ake masa akan takardunsa, da komai ma, basuda labarin komai nashi yana london, baya wasa da dukiyoyinsa, bayaga takardun wasu gidajensa dana wata kwangilar dayakeyi ta ginin makarantu guda s sha biyar na gwamnati babu wani abu na muhimman takardunsa dake gidan, kuma ya musu b'oyon da k'aryar mutum yagano inda suke, acikin toilet ya ajiye, k'asa drower na wash hand base d'inshi, kuma seda ya kunce ta ya d'aga ya saka kanya mayar, murmushi yae sabida akwai dukiya me yawa a b'angarensa, Agogonsa ma akwai dmna diamond zalla, amma batashi sukeb bincike suke masa sosai, akwai ma sanda suka fita ta takardun daya kasa gano kona meye, shida meenal sun dukufa sosai wurin gano me suke nema amma basu gane ba!!.

********
   Sarauniya hassy dai bokanta ya gaya mata Tabbas Tsohon sarki baya k'asar amma yana nan tare da wani ginshiqi daya shafeshi cikin k'oshin lafiya, yakumayi yunk'urin aika b'akin aljani don a gano masa shidawaye amma aljanun sunce wanda ke tare dashi sunada rik'on adu'a bazasu iya kaiwa ma inda yakeba bare ayi maganar cutar dashi, hankalinta ya tashi dankuwa ansanar mata takawa yana dubai, harma sunyi wayar sirri da Meenal so kusan biyu, Tanaso ta gano bakin zaren, ita kanta takaiwa tsohon sarki ziyara a kogonsa ykai so malami gashin tinkiya, so tari takan gaya masa kai tsaye mutuwarsa kurun zata iya rabashi da wannan kogon, dazata iya kisa kenan dashi kenan sun kasheshi tuni sun huta, tayi matuk'ar  bak'in  cikin rashin kisan nashi dan duk ranar daya dawo tasani kashinta ya baushe, da wannan ta shirya shawarar kai ziyara Niger wa Babban bokanta domin samun damar kasheshi a duk inda yake.

**********
   Jikin Abba yayi sauk'i sosai, har idan yake shi kad'ai yakan d'an tashi zaune, kuma yana cin abinci sosai yanzu da hira me tsayi, jikin nan ya soma mik'ewa tsufam daya taso masa ya soma raguwa, sabida yanzu yana samum kulawa da abinci me gina jiki sosai.

Yaum bincike sosai ake gudanarwa akan Nusy daga masarautar Baraya, sun duk'ufa wurin ganin sun kamo wanda yae kisan ita kuwa ta kafe taki magana akan batasan komai ba, anyi juyin duniyar nan tak'i tace komai, wani matashin saurayi yaron wazirin wannan masarautar ne yace abarshi da ita, hakan kuwa akayi dole ya tafi da ita domin binciken dayake ganin shine daidai ma rayuwar ta.

    Yaudai jikin Meenaly yayi tsananin da Takawa ke ganin ya dace taga Dr. Sunje asibitin 'yan k'ananun ciwuka duk an gwadasu batada ko d'aya wannan ya sanya ya bada damar amata general checkup inda kai tsaye hakan yabada result na kidney failure!!!!! D'aya daga cikin kidney's nata data samu infection ada ake shan maganin yanzu yayi worst da har ake tunanin tabbas se an mata dashen k'ota, Wannan poison data sha shine ya b'ata komai domin dafin sa yayi yawa, ga eyesight problem dashima suka k'ara ganowa wanda dama ansan dashi sedai shi ba laifi da dama dama beyi wani illan dabaza'a iya maganin matsalar ba. Dr Khal da kanshi yayiwa Takawa Bayani ya k'ara da cewar

"Yarinyar tana wawta ne, idan da zaka kula sosai na tabbatar kaida ka santa zaka gano ta rame, sannan kuma wannan ciwon baya tsanani haka kurun batare da system na jikinta ya barkace gaba d'aya ba, batada lafiya rashin fad'a kuma yajanyo abun yayi tsanani, sabida haka tabbas sedai an dasa indai baso ake d'ayar ta kama ba, yama kula duk wannan kumburin ta k'afanta keyi problem na kidney dinne" wata iriyar kafirar zuface ta yankewa takawa, duk inda hankalinsa yake sedabya tashi yace jikinsa amace

"Yanzu Dr. Babu yanda za'ayi dole se an dasa mata k'odar kenan?" Kallon sa likitan yae cikin tausaya ya dafa kafad'arsa

"Man sedai hakuri naga a file da kuka bud'a she's just 19, amma ya kuka iya da k'addar? Dole se hak'uri haka tsarin rayuwarta yake, idan da za'a samu k'odar inshaa Allah da idan akayi zan jajirce inga cewar nayi maganin daka iya tasowa nan gaba, zata rayu da k'odojin har abada" Nisawa yae

"Yanzu to ina za'a samu k'odar" shiru likitan yae na wasu 'yan dak'ik'u"

"Samun kod'a abune me wahala yallab'ai, ta siyarwar ma wuya takeyi bako kad'an ba, sannan kuma ba lallai asamu mutum me lafiya duka ba, idan aka gagara samu kuma lallai sedai d'an uwanta na jini yayi taimako da tasa idan yanada lafiyar yin hakan, abu na gaba kuma dole kuyi sauri, sabida bakuda wadataccen lokaci" Tashin hankali shine abinda zamu iya cewa Takawa ya shiga cikinsa, bazebiya cewa ko mutuwar salma ta haddasa masa tashin hankali makamancin wannan ba, duk dauriyar sa seda yae kuka agaban likitan, tausayinsa sosai ya kamasa yashiga bashi hak'uri

"Dr. Ni idan tawa zatayi zan bada tawan" kallon mamaki ya masa

"Are you sure?" Likitan ya tambaye sa, cikin raunin murya ya furta

"Ea mana, a gwada tawa idan zatayi zan bada wlhy" murmushi likitan yae yace

"Acikin mazaje ban tab'a had'uwa da mijin dakeson matar sa har haka ba,Allah ya bata lafiya kuma yabarku tare" Be iya furta Amen ba secikin zuciyar sa.

Kwance ya sameta a saman gadon tayi shiru hankalinta yanaga yanda k'afafuwanta suka kumbura, ga yanayin datakeji ajikinta yafi k'arfin tunanin ta, wato acikin kwanaki bakwai kacal Allah haka yae da ita yauta kara tabbatar wa kanta d'an adam ba'a bakin komai yake ba kamar yanda Muh'd ya fad'a acen bayan sanda ciwo ke cinsa. Da hannu yawa kuyangin alama akan su bar d'akin, itadai se kallonsa takeyi, Kneel down agaba gadon daidai fuskarta ya kamo hannunta dakeda bandage har lokacin ya soma murza yatsun a hankali, bashida kalmar yi mata besan tayaya ze soma yi mata bayanin abinda Dr. Ya fad'a ba, hawaye kurun taga yana bin kuncinsa wanda shi harga Allah bekosan suna zuba ba, hannunta me lafiya takai ta shafo hawayen ta kalli hannun nata sannan ta mayar ta k'ara soma shafe masa sauran

"Bro kadena kuka, rannan da yaa Muh'd baida lafiya da ina kuka yace inyi bak'uri koda ya mutu in dinga masa adu'a nima kayi hak'uri koda mutuwar nai ka dinga mun adu'a kaji my brother, kaga idan kana kuka nima kukan zaka sakani" se kuma ta soma kuka itama amma kwallan kurun b sauti

"Cewa akayi zan mutu ko Abu Haidar? Haka nima nakeji ajikina, kalli k'afana Abu hidar, kalli fa bana iya tashi tsakanin shekaranjiya da yau, kalli Abu Hidar ko sallah daga kwance nakeyi, nasani mutuwa zanyi ka kiramun Mommyna na daddyna ince su yafemun abinda namusu" Hannunsa yakai ta toshe bakinta ya duk'ar da kanshi baze iya hanawa kanshi kukaba, kalamanta sun karyar masa da zuciya, ya zamar masa dole ya kula da ita, dolene yabata k'odar s koda kuwa hakan yana nufin shize mutune ita kuma ta rayu!!!!!

Mom Nu'aiym.

Continue Reading

You'll Also Like

95K 2.4K 35
A little AU where Lucifer and Alastor secretly loves eachother and doesn't tell anyone about it, and also Alastor has a secret identity no one else k...
296K 8.2K 137
"𝑻𝒉𝒆𝒓𝒆'𝒔 𝒓𝒆𝒂𝒍𝒍𝒚 𝒏𝒐 𝒘𝒂𝒚 𝒐𝒇 𝒘𝒊𝒏𝒏𝒊𝒏𝒈 𝒊𝒇 𝒊𝒏 𝒕𝒉𝒆𝒊𝒓 𝒆𝒚𝒆𝒔 𝒚𝒐𝒖'𝒍𝒍 𝒂𝒍𝒘𝒂𝒚𝒔 𝒃𝒆 𝒂 𝒅𝒖𝒎𝒃 𝒃𝒍𝒐𝒏𝒅𝒆."
221K 4.9K 71
imagines as taylor swift as your mom and travis kelce as your dad
37.9K 2.5K 61
𝐭𝐡𝐞 𝟐𝐧𝐝 𝐛𝐨𝐨𝐤 𝐨𝐟 𝐬𝐡𝐨𝐫𝐭 𝐬𝐭𝐨𝐫𝐢𝐞𝐬 𝐚𝐛𝐨𝐮𝐭 𝐨𝐥𝐢𝐯𝐢𝐚 𝐫𝐨𝐝𝐫𝐢𝐠𝐨 𝐚𝐧𝐝 𝐲/𝐧'𝐬 𝐦𝐞𝐞𝐭-𝐜𝐮𝐭𝐞𝐬/𝐥𝐨𝐯𝐞 𝐬𝐭𝐨𝐫𝐢�...