TAFARU TA K'ARE......Anyiwa m...

By 68Billygaladanchi

173K 15.1K 1K

"Mesa kake ambatar mutuwar nan wai, idan akan nace banasan kane kayi hakuri ina sonka wlhy, fiye ma da tunani... More

page 1
page 2
page 3
page 4
page 5
page 6
page 7
page 9
page 10
page 11
page 12
page 13
page 14
page 15
page 16
page 17
page 18
page 19
page 20
page 21
page 22
page 23
page 24
page 25
page 26
27
page 28
page 29
page 30
page 31
page 32
page 33
page 34
35
page 36
page 37
38
39
page 40
page 41
page 42
43
page 44
page 45
page 46
page 47
page 48
49
page 50
page 51
52

page 8

2.9K 255 16
By 68Billygaladanchi

*🙆🏻🙅🏻TAFARU TA K'ARE🙆🏻‍♂🙅🏻‍♂.......Anyiwa me dami d'aya sata*

*Billy Galadanchi*

*Haske writer's Association*

*Sadaukarwa ga Ameena jibril muh'd (Slimxy)*

*Barka da sallah*

                    08
Yusuf yana matuk'ar son budurwarsa dasuke soyayya maryam, bayason abinda ya tab'a ta ko yake shirin tab'ata, sannan baya kawowa rayuwarsa auren wata idan ba ita ba, Meenal bata daga cikin tsarin matayen dayakeso bakuma burin sa bane ya taki takalmin da yayansa ya taka, tsohon takalmin yayansa ba abin takawar sa bane ba, gashi kuma acikin wayar marigayin dake hannunsa yaga saqonnin cin zaragi da wulak'anci da meenal ke aika masa ko bayan aurensu, babu sak'o d'aya dayaci karo dashi da arziqi dukna tsiya ne!!! Besani ba ko hadda bak'in cikinta ya haddasa wa yayansa mutuwa koda yake ya sani itafa mutuwa lokacinr koba ciwo setazo...tunda aka gayawa mahaifinsa one month ake so ai auren ya sanr masa seya saka masa kuka wiwi tamkar wani jinjiri ya hau ban baki da roqon Alfarmar amasa rai yawa wata alqawarin aure shiba yaro bane ba, ganin mahaifinsa baze sauraresaba yaje gidansu Meenal aka tara masa har ita da uwarta yasoma roqon su akan subarshi da zab'in sa...kai tsaye mahaifinta yace yaje zewa nasa mahaifin magana kuma shi ya janye, wasiyya ba tsarin Allah bace ba dan Haka ta hak'ura kawai.....

Meenal tayi kuka tamkar ranta ze fita, ga uwar k'uruciya ace ko shekaru 18 bata cika ba amma har yanzu batada nutsuwa, ta gagara yin karatun ma, saura kwana bakwai birhday d'inta amma harta manta dashi itada take 'yar gata shirin sosai iyayenta ke mata ranar zagayowar ranar haihuwata kuma itace take matsawa akan hakan...tayi magiyar tayi roqon akan acika burin muhammad amma mahaifinta yace batasan girman k'iyayya ba, indai har namiji ze iya cewa da iyayenka baya sanka to babu alkhairi a aurensa kwata kwata.........

Wednesday tazo ta wuce amma sam meenal bata lek'a park ba, hasalima ta soma mantawa dasu Hidar....tana cikin tsananin damuwa har seda sati yazo.....

Tana zaune ita kad'ai a lecture hall bayan an gama lecture kowa ya watse, 2 to 4 sukayi ta tuna da sak'onnin dasuka shigo wayanta bata duba ba, koda ta soma dubawa wani na layin datake amfani dasune d'ayan kuma na bank d'inta ne.....Tasha mamakin jin cewan wai yau ne birhday d'inta suna mata happy birhday, idan da lokacin da muhammad yake rayane shine mutum na farko dake fara aiko mata saqo amma baya hana ta aika masa reply nacin mutun ci, bata mantawa last year ma daya mata sak'o yanda ta kasance a tsakanin su

     *"Koda wane lokaci mukan kasance acikin tsananin murna yayin dukda muka k'ara wasu shekaru a saman namu shekarun.....Tsufa bayida magani wannan ne ya sanya gwara kayi murnar da godiyar Allah daya baka ikon kaiwa wannan lokacin, dubunka suna k'abari suna neman irin damanka ta rayuwa su bautawa Allah su k'ara daga cikin mizanin ayyukansu na Alkhairi kozasu rabauta, haka mutuwa ma batada lokaci sam, kayi murnar shekarunka sun k'aru kakuma ji tsoron dukkanin numfashin d'aya daka zuk'a ka kuma fesar to kuwa tabbas kana k'ara kusantuwa ne da k'abarinka,, acikin murna awa gobe tanadi dan samun tsira. Ina miki fatan Alheri ina miki fatan ki ninka fin abinda kika baiwa baya  a shekarunki cikin Alkhairin Allah.*

Wasu zafafan hawayene suna zuba daga idanta tunawa da reply data bashi....

*"A ido kake nuna kana sona amma nasani k'arya ne, banda haka ranar murnar zagayowar haihuwata kakemun fatan mutuwa? Aniyarka ta bika"* Toshe bakinta tai gudun kada wani yajiyo sautin kukan ta, tasani a park baza'a samu mutane sosai yanzu ba, gashi ba weekends bane ba, wannan ne ya bata daman tattare 'yan komatsanta tana tsananin kuka tabar wurin, k'awarta Zulfa ma tayi aure abinta tun tana india, kuma bata k'asar wayoyinta duk basa tafiya, ga alama ta dena karatun anan tunda dama ba nisa sukayi ba  Yanzu ne suke aji biyu....

**************
     Sosai Meenal keso tayi kuka amma abin ya gagareta, zuwa yanzu fa k'iri k'iri tana ji tana gani zata kasa zubar da k'wallan idanta se kukan zuciya dayafi da fili ciwo.....guri d'aya ta k'urawa ido na kusan mintuna talatin batare data koda k'ifta idanta ba, zuciyar ta har wani zafi take mata tamkar ana hura wuta......Hidar ne ya fad'o ajikinta yana ta kuka

"Mommy shine bakizo ba se yau" da wata hausarsa da tukunna bata k'arisa nuna ba, da alama ya jima be iya magana ba...hankalinta ya dawo mata jikinta ta waigo ta kallesa setaji wani tausayinsa ya mamayeta lokaci d'aya takai masa runguma itama

"Kayi hakuri my Hidar nashiga wata hidimar ne ta daban kaji"  lafewa yae ajikinta ta soma shafa sumar kansa a hankali tana lumshe idonta

"Mom dad d'ina yace wai kin karya alk'awari ba kyau" d'ago dashi tai suka kalli juna ta furta"

"Kayi hakuri my Hidar, dalilin dayasa banzoba babba ne, kuma da ace ina lamban wayan daddynka aidana kirasa a waya kaga base kunyita jirana ba" jinjina kanshi yae

"Ina Ameena?" D'an tabare fuska yae

"Adda meenal batada lafiya fa, tanacen asibiti naga an d'aure ta" Da sauri ta mik'ar dashi zaune

"Menene ya samu Meenal d'in?  Waye kuma ya kaita asibitin, yanzu ina daddyn ku yake?"

"Motane ya kad'eta damukazo nemanki anan, tana nan tanata nemanki tafita wajen gate shine mota ya kad'e ta, daddyna yace laifin kine ai" cikeda rud'u ta mik'e tsaye

"Yanzu to ina daddyn ka?" Da hannu ya nuna mata shi, yayi tsaye ya zura hannayensa duka biyu a aljihunsa yana kallon su, fuskar nan babu annuri ko kad'an, jikinta amace taja hannun Haidar zuwa wurin sa.....acikkn farin gilashin dake idansa take hango manya manyan idansa ....ya kad'a yayi jajir da alama yana cikin damuwa sosai, lokaci d'aya wani shakkar sa ya mata dirar mikiya, a raunane ta furta

"Sannu Daddyn Meenal ina wuni?" Yafi dak'ik'u talatin be bata amsa ba har seda ta sare ta kuma shak'a sosai sannan yace

"Lapia" acikin wata murya da bata tab'a jin namiji da irin taba" seda ta tattaro courage d'inta sannan tace

"Dama Hidar yake gayamun wai mota ya kad'e Addansa, shine nakeso dan Allah ko zamuje na dubata?" Zare gilashin idan sa yai

"Ke dawa?" Ya wurgo mata wannan tambayar acikin muryarsa me kamada muryan wani sarki

"Dama ina nufin ko zaka kaini gunta ne dan Allah?"  Juyawa kurun yae ya soma tafiya batare daya bata ansa ba, har yayi nisa yakuma tsaya ya waigo

"Ya dai? Ba gun Meenal kikace na kaiki ba?" Murmushin yak'e ta k'ak'alo sannan tabi bayansa zuwa wurin parking lot d'in, sauri ta k'ara taje ta bud'e motanta ta tarkato wayoyinta biyu data bari da kuma jakarta sannan ta dawo bayansu....fadawane sunkai susu goma sha biyu ga wasu Excort kuma sanye da bak'ak'en suit susu hud'u, gani tai ana ta zubewa ana aika masa gaisuwa amma ko gezau beba bare su saka ran ze amsa, tsaye tai kaman wata statue tana kallon ikon Allah wannan kuma wanene....hankalinta ne ya kaita gun masu gayarda Hidar

"An gaisheda prince Hidar d'an sarki jikan sarki, gaban salama bayanka salama" Yana tsaye shima yayi biris tamkar yanda mahaifin sa yae....cikeda isa da k'asaita ya furta

"Zan koma" haka suka wage murfin motar yashige a gidan baya shida Hidar, kasa koda motsi Meenal tae harseda yawa wani bafade magana akan tashigo sannan ta tako zuwa d'ayan b'arin ta shige ta zauna aka mayar da murfin motar aka rufe d'an satar kallonsa tai tana mamakin inda shegen kaud'inta ya kawota, yasha mur tamkar be tab'a dariya ko bema santa ba

"Daddyna Mom tace wai nayi hakuri hidima ne ya mata yawa kuma batada Number wayaka datace a gayamun, ka dena yiwa fuskar ka haka 😡😡, ya nuna da fuskar sa, kanawa mom fushi kaji" murmushi zancen yaron ya sanya shiyi ita kuma seta d'auke kanta d'ayan b'arin ta basar

"To Haidar na dena shikenan?" Murmushi yaron yae shima amma be kuma magana ba, har suka isa National hospital dake abuja....suka fito daga cikin motar sesukayi cirko cirko kasancewar uban gayyar be fito ba har wannan lokacin, sunyi mintuna kanya zuro k'afarsa d'aya itama ta jira 20 seconds kan 'yar uwarta ta fito, yayinda fitowar gangar jikinsa gaba d'aya suka d'auki wasu seconds ashirin lafiyayyu, tsayuwar sama bayan yayi seda tafiyarsa tajira ayita na wasu daqiqu ashirin, wani irin takaici ne ya tarnak'e Meenal, da badan sanadin tane 'yar sa ta shiga halin datake cikiba daba abinda ze hanata juyawa ta nemi adaidaita zuwa inda dare mata ba, haka suka d'unguma itama dake mace tafishi cira k'afar ta.

  Da gudunta tayi kan yarinyar dukda kasancewar ta tarar da d'akin a cike danqam, kana ganin mutanen dake zaune a wurin zaka tabbatar wa kanka jinine na sarauta kodan yanayin shigar su

"Nashiga uku na, Ameena meya sameki haka?" Hankalinta yakai k'ololuwa wurin tashi ganin hannun yarinyar a ninke ga bandage har a kanta, bata fatan kyakyawar fuskar Ameena ta sauya ta dalilinta.....kuka wiwiw ta saka yayinda ilahirin d'akin yae tsit ita kad'ai ake saurare Meenal kamma baccinta takeyi abinta dukda yake kallo d'aya zaka mata ka gano tanajikin rad'ad'in ciwo, Hidar ne yazo ya rik'e hannunta

"Mom plss ki dena kuka, Adda Amal fa taji sauqi, kuma granny tace muriqa yi mata adu'a" Share hawayenta tae ta rik'o Hidar d'in amma bata dena zubar hawaye ba, seda tai kusan minti biyar sannan ta baiwa kanta hak'uri, Koda ta d'ago kanta ilahirin mutanen dake d'akin sun zubo mata ido ciki kuwa hadda Daddyn Hidar....ganin wani babban  mutum sanye da uban rawani yasha nad'i ga kayan nan na sarauta, ga kuma babbar mace a gefensa zaune itama cike da shiga ta alfarma ya bata daman zubewa a k'asa  ta gaidasu cikin girmamawa, Hannu kawai me rawanin ya d'aga mata yayinda macen dattijuwa tace

"Sannu 'yarnan, dama kece Momyn su Hidar?" Murmushi ta k'ak'alo tana share hawayenta ta gyad'a mata kai alamar E itace, murmushi tae

"Ki dena kuka kiwa Meenal adu'a, inshaa Allah zataji sauqi, karayane a hannu kanta kuma ata bayane ya fashe kuma anyi nasaran yin d'inki ma, abinda ake shirin warewa zuwa gobe ma, hannun ma ana ganin sauqi Alhamdulillah ki dena damuwa kinji 'yata" jinjina kanta kurun tai batai magana ba, gyaran murya wannan dattijon yai yace

"Adena damuwa, ayi hakuri ana kuma adu'a inshaa Allah matar ciki zata samu sauk'i da yardar Allah"  Wani irin kunyan tsohon ne ya mamaye ta, ta sadda kanta k'asa kafin kuma ta k'ara komawa ta k'urawa Meenal ido, adu'a samun lafiya sosai ta mata sannan ta durk'usa tamusu sallama akan se washe gari zata dawo in Allah yaso..... Bazata juri wulak'ancin  wannan man d'in ba dan yana jinin sarauta seyaketa wulak'an ci? Akarin me,,,,, adaidaita taje ta hau tayi tafiyarta batare data tsaya neman saba ma.

***************
     Se yau zulfa takira Ameena, tasha mita kuwa, acikin wayar take gaya mata komai, atare sukasha kukansu

"Amma meenal ke a haka zaki auri usif d'in? Bakya gudun abinda zeje yazo, damuwa bazata miki yawa ba kuwa, tunda ke kinyi niyyan cika wasiyan sa kuma jininsa yak'i baseki hak'ura meenal?" Nisawa tayi

"Tunda nake da Yaa muhammad ban tab'a aikata abinda yake so ba, last wish nashi kam sena cika, a k'auyuka uku yanzu haka an gina rijiyoyi guda uku, kuma masallatai uku zan yi yanda ze samu lada me tarin yawa, kuma duk a k'auyuka zan yisu, auren yusuf kuwa koda ze kasheni se idan na mutu kan auren amma sena aure shi, wlhy ina tsananin kewar muhammad zulpha, ki k'aramun k'warin gwiwa kawai" nisawa ta qarayi

"Allah yasa hakanne mafi alheri"

Godiya ta mata sukayi sallama.

**********
    Wayarta data manta yake jujjuyawa, yazo yayi dogon bincike akan yarinya amma shiga hurumine farawa takan wayanta, ina ze ganta to? Wane irin saunancine mantuwa da waya a mota haka kawai? Tunda tace zata dawo gobe ze bayar a bata......

Mom Nu'aiym

Continue Reading

You'll Also Like

185K 2.1K 50
I actually haven't posted a book on wattpad in about 2 yrs so gimme a break if it isn't good ๐Ÿƒโ€โ™€๏ธ But most are smut so be ready and idc if u vote ju...
100K 5.7K 135
๐ญ๐ก๐ž ๐Ÿ๐ง๐ ๐›๐จ๐จ๐ค ๐จ๐Ÿ ๐ฌ๐ก๐จ๐ซ๐ญ ๐ฌ๐ญ๐จ๐ซ๐ข๐ž๐ฌ ๐š๐›๐จ๐ฎ๐ญ ๐จ๐ฅ๐ข๐ฏ๐ข๐š ๐ซ๐จ๐๐ซ๐ข๐ ๐จ ๐š๐ง๐ ๐ฒ/๐ง'๐ฌ ๐ฆ๐ž๐ž๐ญ-๐œ๐ฎ๐ญ๐ž๐ฌ/๐ฅ๐จ๐ฏ๐ž ๐ฌ๐ญ๐จ๐ซ๐ข๏ฟฝ...
56.6K 4.4K 61
"Bredda yuh deaf say mi and yuh done" I said as I walked out of the bathroom "We nuh left until mi say suh" He said following behind me "Who author...