TAFARU TA K'ARE......Anyiwa m...

By 68Billygaladanchi

172K 15.1K 1K

"Mesa kake ambatar mutuwar nan wai, idan akan nace banasan kane kayi hakuri ina sonka wlhy, fiye ma da tunani... More

page 1
page 2
page 3
page 4
page 5
page 7
page 8
page 9
page 10
page 11
page 12
page 13
page 14
page 15
page 16
page 17
page 18
page 19
page 20
page 21
page 22
page 23
page 24
page 25
page 26
27
page 28
page 29
page 30
page 31
page 32
page 33
page 34
35
page 36
page 37
38
39
page 40
page 41
page 42
43
page 44
page 45
page 46
page 47
page 48
49
page 50
page 51
52

page 6

3.7K 296 10
By 68Billygaladanchi

*🙆🏻🙅🏻TAFARU TA K'ARE🙆🏻‍♂🙅🏻‍♂.......Anyiwa me dami d'aya sata*

*Billy Galadanchi*

*Haske writer's Association*

*Sadaukarwa ga Ameena jibril muh'd (Slimxy)*

*Barka da sallah*

                     06
Da k'yar da rarrashi suka samu ta dena kukan tayi sallolin dasuka gabata da akayi tana bacci abincin ma da aka kawo mata gagara ci tai se kukan zuci datakeyi wanda yafi na zuciya ciwo, ta k'urawa abincin ido amma zahiri ba abincin take kallo tunanine ya lulata wata duniyar ta daban........

"Mesa kike cin abinci da spoon me my meena? Kuma babu tarbiya ko kad'an a yanayin  zaman ki nacin abinci, bakya ganin rashin dacewan hakan?" Wani kallo ta wurga masa a wancn lokacin kantace

"Kaga nifa ban iya kalan jahilcin daka iyaba, yaya zanzo acikin mutane irin wannan na saka hannu naci abinci, kagama bani kunya sannan kazo kanamun hauka akai" Murmushi yae

"My meena yana da kyau ki daraja d'an adam komai k'ank'ancin sa, kasancewar wani lokaci zezo dazaka gane amfaninsa, a wannan lokacin kuma  ba lallai ya kasance yana nan ba, abubuwa da dama game da halayenki suke rikitar dani, idan na d'auki b'angaren yanda kike yarfe manyanki da magana mara dad'i nikanyi fatan Allah ya sanya nini kad'ai kike yiwa hakan dannikam zan jure komai munin abinda zakimun, abinci dakike gani yanada matuk'ar muhimmanci ya cancanci darajawa me yawa wasunki sunacen asibiti sunason cin abincin amma Allah be basu ikon ciba, suna kuma da wadata sunada abincin, dubunki suna cen suna neman na safe babu bare sauran wuni, Akwai malali gashin tinkiya dasuke acikin k'aburburansu suna kuma son su dawo duniyar su k'aru da koda ladan cin abinci da hannu ne su qara dashi amma basu samu ba....ki gane mana my meena!!"  Ture abincin gabanta tayi lallai ta yarda ka kalamansa yanzu yanzu gata da ranta da lafiyarta amma damuwa kurin ta hanata cin abinci...tayi kuka tamkar ranta ze fita da k'yar suka samu tasha tea se kuma sukace a k'ara mata alluran ko kad'an ne sabida sunga tana cikin yanayin tashin hankali....

*****************
     *Bayan kwana bakwai*
Haka meenal ta dangana sabida ta k'ara yardarwa kanta babu wani mahaluk'i daze mayar mata da muhammad d'inta mutumin data haqiqancewa kanta batada wanda take k'auna sama a fad'in duniyar seda *TA FARU* ta kuma *KARE* sannan tasan akwai so a ranta!!! Tun tana samun daman kuka da idanta harta ya dawo sedai kukan zuci duk ta yamutse tayi dana sanin rayuwarta  da abubuwan data aikata agareshi ta tsani kanta har wannan lokacin bata karanta takardan daya rubuta mata ba yaune kuma ake shirin barinta a gidanta domin ta samu daman yin takaba cikin mutunci wannan umarnin mahaifinta ne wannan ya sanya aka qara me gadi d'aya dakuma wata baiwar Allah domin tayata zama wacce take 'yar uwa awurin mahaifinta da kuma 'yarta wacce take kusan sa'ar meenal d'in domin d'ebe mata kewa...yaune take shirin duba wasiyyan mamacin datayi Alk'awarin bi komai nauyin wasiyyar akanta kuwa inshaa Allah....ta sanya a ranta zata yi komenene tamasa abu na k'arshe dayake buri tayi agareshi......

*Ga abinda yace*

Assalamu Alaiki Ameenaty....dukda ina gab da barin duniyar nan hakan baze hanani so dakuma k'aunar kiba, ki sani babu me iko da rayuwata se mahaliccina amma likita ya gayamun kai tsaye huhuna baida wani saura!!!! Ya gama lalacewa kaf my meenal! Wlhy Ameena naso in rayu dake rayuwa me tsayi, nayi mafarkin tsufa in tara zuri'a a tare dake amma Allah be nufa ba, naso in sauke nauyin daban tab'a sauke munba Allah be bani iko ba kimun rai ki yafeni kinji...dalilin rubuta miki wannan shine domin in k'ra jaddada miki k'udiri na son ki auri k'anina Yusuf.... Ko bana raye 'yayan da yusf ze haifa nawane bazan yi bak'in cikiba idan kika hayayyyafa dashi se murna ma har a makwanci na, ma sani ni kika haifawa 'ya'ya bayan rai na, naso ki tsaya mui magana amma naga kin karaya da kala maina....ki daure ki taimakeni kimun wannan.

Acikin akwatin bankina na b'oyayyen acc d'ina dana bud'a  na adane  kud'ad'e masu yawan gaske fiye da rabin dukiyata ne wanda ni muhammad na mallaka miki su acikin sirri, akwai komai nawa  awurin Aminina sharif kuma nagaya masa da lauyana zakuje ki cire, acikin dukiyar dana mallaka miki ba acikin gado naba ina roqon alfarma ki gidanmun rijiya da masallaci ladan yake zuwamun ko bayan bana nan idan Allah ya baki iko ga number sharif nan koda yake ko baki nemeshiba shize nemeki ***********.

Banida rayuwata a hannuna kuma bansan gaibuba amma dai ina barmiki wannan wasiyyar ne sabida banida tabbacin zankai safiya! Ki taimaka ki cikasamun alqawarina na auren yusuf dan Allah my meenal..... Ko daure ki gidan rijiyar nan da masalallaci.

Abu na k'arshe kuma adu'a ina rok'on alfarmar acikin lokutan dasuka rage miki na rayuwa karki manta ni, ki sakani acikin adu'oin ki don nemamun rahamar Allah kinga fa my meenal banida magaji, banida d'a banida jika babu me tunawa dani dagake se mahaifana da 'yan uwana....ki rik'e koyarwar musulunci meenal banason yanayin shigarki ina jiyemiki lahirarki a sassautawa duniya ayi sirki da neman lahira....

*Ina sanki Ameena!! Ina miki son so fiye da tunaninki, aduk fad'in duniyar nan banda iyayena babu wanda nakeso sama dake...inajin tsoron mutuwa, idan na kutu ki sani na tagine dan amsa kiran mahaliccina amma ina cike dason k'arin lokaci don bauta masa in kuma rayu dake....hakance tsarin rayuwata amma ina tsananin san rayuwa ta ki riqa mun adu'a....

*Ki auri yusuf my meenal, amma idan hakan yana daga cikin tsarin Allah.....karkiyi jayyya da zab'in Allah idan har kikaga babu alkhairi aciki... Ki hakura..karki d'auki wasiyya matsayin dole zab'in Allah shine daidai.

Ma assalam ina miki fata Alheri"

😭😭😭😭😭 koda ta gama karanta wannan dakardar tayi kuka mara iyaka ranar a zaune ta kwana, tana kallon yanda rubutun yake kana gani kasan yana cikin azaba sanda yake rubutun.....

*****************
   *Bayan meenal ta gama takaba*

Tattarewa tai ta koma gidansu, amma abun nacinta nason tawa yusuf maganar amma ba fuska, mahaifinta ta sama ta gaya mai komai gameda wasiyyar da muhammad ya bari nason ta auri yusuf!!! Mahaifinta kuma besha mamaki ba ya nemi mahaifin marigayin kai tsaye suka tari yusuf da zancen yayi musu kam!!! Yasha musu amma mahaifinsa yaja layin tsinuwa akan baze bari abinda d'an uwansa ya buk'ata d'aya ba a ce baza'a masa dole ya hakura

Abubuwa biyune suka tashi hankalin yusuf yace bayason auren meenal, na farko dai  yagama shirin aurensa da budurwarsa maryam sun gama d'inkewa....yana kuma masifan santa, na biyu kuma ya tsani meenal, yanajiyo sanda take cewa idan akan tace batasan yayansa yake cewa ze mutu ta janye, dama kenan cewa take batasan shi kanta tsaye, da wannan ya k'udiri niyyan wulaqanta mata rayuwa dama ga yusuf da shegen zafi ba kad'an ba.

   Kallon kallo suke da ita tunda yazo, sosai tsoron yaa yusuf ya d'arsu a ranta tunba yauba shi dama baya wasa da yara, kuma sam shi baya zuwa koda gidan sune, tsaki yaja yana wurga mata mugun kallo yace

"Mayya wai meye haka? Kallon na meye?  Kin cinye mun yayana ni kuma yanzu zaki cinyeni ne, wlhy nafi k'arfin ki kurwata kur" Nisawa tae

"Yaa yusuf to kuma duk me ya janyo wannan maganar?" Ta tambaya tana langwab'e kai

"Wlhy na tsaneki, banza wazakiwa karuwanci anan? Kin gama kashemun d'an uwana ni kuma kike cewa zaki aureni, wlhy sekinsha  azaba a hannu na, inada budurwata kin kawo zancen wasiyya jahila kawai" kallon mamaki take binsa dashi meya kawo zancen kisa, ta k'udirta a ranta kome zeyi seta cikawa muhammad burinsa, tunawa tae da wata magana da muhammad ya tab'a yi mata

"Ki dena furtamun kalmar tsana kanki tsaye my meenal, ba kyau ranar dukda wani ya gaya miki bazakiji dad'i ba zakuma ki gane abinda nake nufi, koda mak'iyinka bakaso yace ya tsaneka bare kuma abinda kakeso" Runtse idanta tai ta bud'esu a hankali, ta gane nufinsa taji zafin kalaman yusuf fiyeda tunanin sa, koda ze kasheta kuwa seta cikawa muhammad burinsa na auren yusuf din

"Kai hakuri yaa yusuf" mik'ewa yae yana banbami

"Wlhy senaci qaniyar ki idan kika k'ara gigin kiran wayana yanda kikai d'azu, bana buk'atar hakan shashasha kawai"  sororo tai tana kallonsa harya b'acewa ganinta, takula yanzu ta fara ganin abubuwa indai wannan yusuf d'inne to akwai matsala, kumafa kome ze mata se dole  ta aure san.....figar motarta tai zuwa Island park tana cikin tsananin damuwa, Ba kad'an ba take k'aunar muhammad d'inta yanzu kam, shikam be tab'a zaginta ba baya son b'acin ranta ko kad'an, betaba yi mata koda tsawaba, kome zata ce masa baya damuwa, yau itace ake zagi, zagin ma na wulaqanci amma ta gagara yin komai, gefe d'aya ta samu inda babu hayaniya ta zauna tanata rizgar uban kuka me tsuma zuciya.......kaman daga sama tajiyo muryan yarinya ga kuma hannunta a kan nata tana jijjigata

"Mommy meyasa kike kaman daddy na ne ehm? Kullum shima seyazo nan ya dinga kuka kuma idan na rarrashesa baya denawa, dan Allah ku dena kuka kunji, kinga Hidar ma sabida kuna keda daddyna se kuka yake" D'agowa tai ta kalli yarinyar bazata wuce shekaru bakwai ba se yaron dake binta iyakacin sa hud'u yanata kuka, ita d'inma yarinyar k'walla ya taru a idonta k'arfin hali kurin takeyi kamo hannayensu tai dukansu  tace

"Mesa daddy yake kuka, ni kinga cikina ne yake mun ciwo, Haidar meya same ka" jan hannunta ya somayi

"Kizo muje kice daddyn mu yae hakuri ya dena kuka, mommyn mu mukazo nema kuma bamu ganta ba, shine yake kuka, kozaki nemamun ita ne" bata gane kalaman yaron na, amma bata mik'e ba, sema rumgumesu da tai dama hakan take buk'ata ta dinga rizgar uban kuka, suma yaran kuka suka saka sunfi 5mns sunayi sedaga bayane sukayi shiru dukkansu,ta kalli babbar tace

"Yaya sunanki?"

"Sunana Ameena" yarinyar ta bata amsa kai tsaye.... Jinjina kanta tai

"Mesa daddy yake kuka ne?" Ta tambaye ta

"Mommy ce ta b'ata tun kwanan baya fa, shine bama ganin ta, kuma haidar seyace azonan a duba masa ita tunda nanne muke yawan zuwa, idan ya matsa se daddy ya kawomu idan munzo bamu ganta ba sekuma daddy da haidar su dinga kuka" bata gane komai ba akan bayaninsu amma a hakan seta basu hakuri akan zasu ganta  ne wataran.....

Mahaifinsu kuwa tsaye yake k'ik'am yana kallom su a tare da ita, har sukai sallama yana kallon su, Hidar harya juya ta rik'oshi ta rungumesa a durk'ushen datake sannan ta manna masa sumba a kuncinsa......wani memory ya flashing wa daddynsu Ameena wanda seda ya runtse idansa na mintuna kannan ya bud'esu.... Wayam babu ita ba labarinta sesu hidar dake d'aga hannu alamar bye bye da alama ta b'ullee....gun yaransa yazo be damu da sanin wacece sukaje gunta ba, damuwar dake zuciyar sa ma ta ishesa.....

*Masu karatu yanzu muka fara wasan fa😍😍😍😍✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻 anya meenal zata k'ara samun farin ciki kuwa?*

Mom Nu'aiym

Continue Reading

You'll Also Like

616K 1K 22
Smexy One shots😘 Got deleted twice 3rd times a charmπŸ€¦πŸ»β€β™€οΈπŸ˜­
221K 4.9K 71
imagines as taylor swift as your mom and travis kelce as your dad
94.9K 2.4K 35
A little AU where Lucifer and Alastor secretly loves eachother and doesn't tell anyone about it, and also Alastor has a secret identity no one else k...
154K 15.1K 30
"α€žα€°α€€ α€žα€°α€…α€­α€™α€Ία€Έα€™α€Ύ α€™α€Ÿα€―α€α€Ία€α€¬..." "..............." "α€‘α€Ÿα€„α€Ία€Έ..α€„α€šα€Ία€žα€°α€„α€šα€Ία€α€»α€„α€Ία€Έα€œα€­α€―α€·α€•α€Όα€±α€¬α€›α€™α€œα€¬α€Έ..ထတန်းတူတက်ခဲ့ဖူးတဲ့ α€‘α€α€”α€Ία€Έα€–α€±α€¬α€Ία€œα€­α€―α€· α€•α€Όα€±α€¬α€›α€™α€œα€¬α€Έ...α€’α€«α€™α€Ύα€™α€Ÿα€―α€α€Ί..α€›α€”α€Ία€žα€°α€α€½α€±α€œα€­α€―...