MAKAHON SO _Blinded Love_

By Shuwerh_Beelkeey22

104K 5.3K 283

It's all about love and sacrifice More

Episode 1
Episode 2
Episode 3
Episode 4
Episode 5
Episode 6
Episode 7
Episode 8
Episode 9
Episode 10
Episode 11
Episode 12
Episode 13
Episode 14
Episode 15
Episode 16
Episode 17
Episode 18
Episode 19
Episode 20
Episode 21
Episode 22
Episode 23
Episode 24
Episode 25
Episode 26
Episode 27
Episode 28
Episode 29
Episode 30
Episode 31
Episode 32
Episode 33
Episode 34
Episode 35
Episode 36
Episode 37
Episode 38
Episode 39
Episode 41
Episode 42
Episode 43
Episode 44
Episode 45
FINAL EPISODE

Episode 40

2K 101 12
By Shuwerh_Beelkeey22

® *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITERS*​💭💭💭

​ɯɛ ɖơŋŧ ʝųŞŧ ɛŋŧɛřŧąıŋ ŋɖ ɛɖųĆąŧɛ, ცųŧ ɯɛ ąٳŞơ ŧơųĆɧ ɖ ɧɛąřŧ❤ ơʄ řɛąɖɛřŞ​

# WWW.PMLWRITERS@GMAIL.COM
# ​IG PML WRITERS​
# https://www.facebook.com/PML_-Writers
FANS-459256761123035
# http://

.
   . ❉ *.¸¸.*✳*.¸¸.*❄*.¸¸*❆ *.¸¸.*❄.¸¸.*✳*.¸¸.*❄*.¸¸*❆ ¸¸.*❄¸*✳'☆´-
…¸.¤ª '☆´_____________☾_____________-'☆´-
   💕💞  *MAKAHON SO*💞

       *Blinded  Love*
•☾• ¯¯¯¯¯¯¯¯¯¯¯¯…¸.¤ª☆“˜¨¨ ¯¯¯¯¯¯¯¯¯¯¯¯•☆•  ゚ ☆   
¸.¤ª☆“˜¨''''''''¨  *'''_*Written By Beelkeey Shuwerh*_ ''* “˜¨¨☆ª¤
¸ 。 ゚'☆_____________☾_____________'☆´
_________________•☾• ¯¯¯¯¯¯¯¯¯¯¯¯…¸.¤ª☆“˜¨¨ ¯¯¯¯¯¯¯¯¯¯¯¯•☆•。 ¯•☆•  ゚☆    
¸.¤ª☆“˜¨•。❉ *.¸¸.*✳*.¸¸.*❄*.¸¸*❆ *.¸¸.*❄.¸¸.*✳*.¸¸*❄*.¸¸*❆ ¸¸.*❄.¸¸.*✳ *.¸¸.*❄*.¸¸*❆

Wattpad @Shuwerh Beelkeey22

        *In dedication to Asmeey Real Pure Pinkeey*
_Happy birthday My Beautiful Hayatie More love more kwana_
   A word alone are not enough to express how happy I'm to know that you are going to enjoy your another year of life.Nothing expresses me than seeing you happy with us this year of life. I wish you the blessings of today to be more happy in your life and moreover I wish you a thousand millions of years ahead Habibty, may Almighty Allah bless your fulfillment of your dreams and aims of yours goals insha Allah .
   Once again wish you a very happiest womb escape... Age with grace... More kwana... More beauty... More kudi to your bank account.... More blessings... More sense... More.. More.. And More farin jini... Miji nagari is mah wish.
May Allah's Rahama.. Khair... Nur... Blessings... Love... Protection... Guidance be always with you better half.
   *أعشقك*
May It Be The Best Day Of Your Life Thus Far, & May Your Happiness Grow With Each Passing Day Through The Many Many Birthdays That Surely Are Ahead Of You..'''
    *Happy Birthday Asmeey Real Pure Pinkeey*
   💋💋💋💋💋💋💋💋💋💋
   🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂🎂
Wishing u a day soft as silk..... white as milk..... sweet as honey and full of money. may all ur dreams come true.... HAPPY BIRTH DAY our dear talented writer wishes u all d best lyf could offer long lyf and prosperity stay blessed is yah day.

Episode 40
2_2_2019
Bissimillahir Rahmanir Rahim.

Runtse ido tai da k'arfi ta fad'a baya wane wadda wuta taja, d'agowa tai ta ware idanun ta da suka sake mugun ja kan Abuh daya sunkuyan da kansa saboda tsantsan tausayin ta back to Ya Sadeeyq da hawaye ke race kan cheeks insa, jikin ta na tsanan ta kakkarwa ta d'auke kanta kan Ya Sadeeyq ta maidan kan Ya Omar da Ya Uthman ya k'ank'ame hannun sa yana kuka wane k'aramin yaro, kanta ne ya wani mugun sarawa nan take jijiyoyin kan du suka mimmik'e idanun ta wane an barbad'a mata barkono saboda ja da wani irin zugi da suke mata, da d'ayan hannunta ta dafe setin zuciyan ta da take ji wane zata faso k'irjin ta fito, zafi, zugi, d'aci da rad'ad'i ta rasa gane wanne take ji ga wani abu daya toshe mata mak'oshi.
     Sake kallon fuskan Safwan d'in tai kalamun sa na amsa kuwwa a kunnen ta ”Twiny promise me no matter what it takes idan kika ji labarin rasuwa na bara kiyi min kuka ba addu'a zaki min! cause at the very time ita kad'ai nake buk'ata and please promise me you will stay strong, bansan ya rayuwana zai kasance ba idan babu Safwah that's why i always pray dead to take me before you, I Love You so much”.
Ahankali ta kwantar da kanta kan fuskan sa numfashin ta na fuzga ta soma masa addu'a, du rashin imanin mutum inya ganta saita bala'in basa tausayi, tun tanayi addu'an na fita harta koma na zuciya, sai lokacin ta tabbatan da lallai kuka rahama ne gashi tana son yi amma ya gagara, haka gaba d'aya jikin ta ya saki kan gawar ta dena motsi.
     Ya Haidar ne ya soma fuskantan halin da ake ciki, a firgice ya k'araso ya d'ago ta yana tapping kumatun ta amma ina, fad'in irin tashin hankalin da kowa ya k'ara shiga zan rage muku wani abin, bama kaman Suwayd jiki na rawa ya d'auke ta yai cikin gida, kwantar da ita yai kan sofa kowa yayo kansa da tambaya, baiyi nakan kowa ba ya d'ebo ruwa ya yayyafa mata, a wahalance taja dogon ajiyan zuciya amma bata bud'e idon ta ba.
Dr'n daya gama wa Kadsah alluran bacci aka sa itama ya mata,Suwayd ya d'auke ta yakai d'akin da Kadsah'n ke bacci da kallo d'aya inka mata kasan baccin azaba ne dan yadda fuskan ta ya mugun ja ya kumbura.
     D'aya bayan d'aya suka rik'a zuwa suna masa addu'a har aka zo kan Ummy, dakyar Abuh ya rik'e ta tai masa addu'an saboda yadda jikin ta ke rawa, kukan data ke ta dannewa ne ya kwace mata lokacin data bud'o fuskan sa taga kisan wulak'ancin da aka masa, k'ank'ame Abuh tai sosai tana kuka mai tsuma zuciya, dakyar ya daure ya mik'ar da ita ya maidan cikin gida dan sosai kukan nata ke tab'a masa zuciya, shima daurewa kawai yake dan shikad'ai yasan mai yake ji.
Granny kuwa saboda tsaban rud'ewa har sab'o ta kusan yi cause she never thinks cikin d'iyoyin ta ko jikokin ta akwai wanda zai riga ta mutuwa, itama sanda aka had'a ta da ruwa dan yadda jinin ta ya hau.
    Kuka sosai ne ya b'alle a gurin lokacin da aka zo fita da gawan, haka dai aka sallace sa aka wuce dashi gidan sa na gaskiya.

_Ya jama'atul muslim ya kamata mu farka daga baccin da muke, make peace with everyone, people are dying... Walai this duniya is nothing, you never know we can die at any time, death awaits no one, dagaske they will come a day when you won't take shower yourself but you will be given one, you won't wear clothes yourself but someone else will do it for you, you won't go to masjid on foot but four people will take you there, you won't pray salah buh a salah will be prayed upon you, my sister my brother please wake up Kullu nafsin za'iqatul maut, zaki mutu! Zaka mutu! Zan mutu! When?  Only Almighty Allah knows mu daure muyi amfani da lokacin mu wurin bauta ma ubangiji tun kafin mutuwa ta riske mu, nobody knows tomorrow and Allah say even if your sins reached of to the clouds in the sky, i would forgive you and I shall not mind, try to seek forgiveness from Almajid, It is so scary death come to us when our imaan is low, let's pray that Allah subhanawu wata'ala takes us when he is most pleased with us, may La'ilah ha'illallah muhammadur Rasulillah be our last word on earth Amin_
     _We love our dear ones buh Allah loves them most, kuka, ihu, aljanu bare tab'a dawo mana da wanda muka rasa ba is better for we guys to stop it, if we can't pray to show love towards them let's just keep calm it will be better, Allah ya k'arba rayuwan mu cikin sauk'i, ya bamu hak'uri da juriyan wad'anda muka rasa Amin_

Sosai al_umma suka cika gidan kowa ya bud'i baki alkhairin sa yake fad'a ba sharri ba, mota guda na marayu aka kawo sukai gaisuwa, sosai yaran ke kuka dan yadda suka bala'in sabawa dashi, Aunty Safwah suka nema a nuna musu aka basu hak'uri dan du a bakin Safwan suka santa.
     Haka dai ranan aka kasance cikin jimami, amma tuni an soma bincike akan abun ga Umaima da ake sa ran inta tashi komai zai zo da sauk'i tai loosing memory.
Sai k'arfe goma na dare Kadsah ta tashi, take komai ya dawo mata runtse ido tai tana tuna last moment nasu, hawaye ne masu zafi suka kwarinyo mata ta k'ank'ame hannun Safwah dake baccin wahala, ta dad'e a wannan halin kafin ta tashi taje toilet ta d'auro alwala ta sauke sallolin dake kanta ta koma sujud ta dinga masa addu'a sosai.
      Sanda ta soma jin jiri ta d'ago ta jingina da gado ta lumshe idanun ta tana hango kyakkyawan fuskan sa da kullum ke cike da annuri, tana wannan halin Safwah ta soma wani irin jijjiga cike da tashin hankali ta soma jijjiga ta amma ina, ficewa tai da gudu tai part d'in Granny nan taci karo da Suwayd, hannun sa ta soma ja dan sam ma ta kasa magana har suka je d'akin.
A matuk'ar firgice ya d'auke ta ya fice kan ya tada mota ya k'ira Dr Alkasim, suna zuwa akai emergency ward da ita ganin ya kasa aikata komai akai waje dashi, du taimakon daya dace aka mata then aka fito da ita zuwa d'akin hutu.
     A daren Mammy tazo dan ita zata zauna da ita, tsayin kwana uku kenan har kuma lokacin Safwah bata cikin hayyacin ta, ga Kadsah ma an rasa gane kanta kullum bata da aiki sai kuka, gashi ta k'aurace ma cin abincin zuwa lokacin sanda tasha ruwa leda hudu.
A rana na hud'u aka sallamo ta sandai bata umm ba umum sai bin mutum da ido, du wanda yazo mata ta'aziya sai dai ta bisa da ido gashi dayawa anzo mata, dan _Beelkeey Shuwerh fans group_, _Miemiebee_, Mhiss_B_Hal_, _Ina da shi_ ma duk sun zo.
       Tsoro sosai ta soma bawa kowa da tsananin tausayi dan gara Kadsah ita tana yin kuka at least yana rage mata wani abun, Safwah kam babu kukan  sai zugi da d'acin zuciya.
Ammey ko kallon Safwah bata yi saboda tsananin tausayi musamman inta tuna lokacin data rabu da nata d'an uwan abin alfaharin ta though shi ba mutuwa ce ta raba su ba, to Safwah fa shikenan ya tafi ya barta da kewa ita dashi sai a darus salam.
    Haka suka kasance har ranan sarakan bakwai, ranan Kadsah tayi kuka like never before, a wurin zaman ne wani mutum yazo bayan yaci abinci ya k'oshi ya mik'a ma su Abuh hannu aka gaggaisa fuskan shi fal annuri wane ba gidan mutuwa yazo ba, koda ya mik'e zai tafi bud'an bakin sa sai cewa yai ”Allah ya maimaita mana Alhaji wallahi munci mun k'oshi, rabon da naci abinci haka har na manta....” tass kake ji Suwayd da zuciya ta ciyo ya d'auke sa da mari, ya d'aga hannu da niyyar sauke masa wani Daddy yai saurin tare sa.
    Abuh kam du yadda yaso kasa daurewa yai sanda ya zubar da kwalla jin mummunar fatar da wannan bawan Allah'n yayi masa kawai dan ya samu daman cin abinci.

_Ga wani matsalan ire-iren abubuwan dake faruwa  a gidan makoki kenan, wani walai cin abinci ke kawo sa, abin haushi abin ban takaici ma wasu zaka ga har maggi ko yaji suke guzuri in case in abincin batayi musu yadda suke so ba, wannan abu har ina wai shin baka tunanin kaima zaka mutu? Shin kai acikin duniyan zaka dawwama ne, miji tsoron Allah walai all this we are doing is wrong, yanzu idan talakan mutum ne ya mutu wallahi wallahi zaku sha mamaki in kunga 'yan mutanen dake  zama ai makoki dasu amma in akace yana da kudi wani inya zauna wallahi har sarakar bakwai, dan Allah muji tsoron Allah muma fa zamu mutu, yaushe ne?  Bamu sani Allah daya halicci sammai da k'assai ya halicci rana da wata da this dunya we guys living in shikad'ai ya barma kansa sani, Allah yasa muyi kyakkyawan k'arshe Amin_

Cikin gidan kuma Ammey ce ta shiga kitchen da zummar d'auka ma Kadsah ruwa ta iske wasu mata, sun dage sai jidan abinci suke both d'anye da dafaffe, da mamaki ta tsaya jin abinda suke cewa.
    ”Wallahi k'awata kinga dama baya nan inna tafi da wannan ma rage, kud'in da zai turo mana kuma na k'ara jari”.
Dariya itama tai ta bata hannu suka tafa wane ba'a gidan mutuwa ba tace ”Wallahi ki bari k'awata aini har so nake naji anyi mutuwa a irin fantama fantaman gidajen nan, kedai kawai muyi addu'a Allah ya maimaita da wuri wuri”.
    ”Amin” suka fad'a a tare suka cigaba da abinda suke, juyawa Ammey tai cike da zafi da k'unan zuciya, hawaye kuwa batasan when suka b'alle mata ba.

_Ga matsalan mu mata ta bayyano wa'iyazubillah, naje biki naga abinci available na d'iba zan tafi dashi gida innaje saina huta me hakan kenan? Same goes to gidan suna and mutuwa, imma ta d'iba miya tace in taje gida farin shinkafa zata dafa ko ta d'iba shinkafan tace already dama tana da miya, koma dai ta d'iba duka, shin akan idon masu abin ta d'iba? Shin idan basu bata ba ya kenan? Shin ma halal d'in ta ne ko sata tayi? Dan Allah dan Annabi masu haka ku daina dan inhar masu abin basu yafe ba wallahi Allah bazai yafe ba dan bai yafe hak'k'in wani akan wani Allah yasa mu dace_

Haka ba tsoron Allah suka d'iba kayan suka ware, yayin da shima mutumin da masu hali irin nasa suka tafi.
    Yauma anzo da marayu sosai harda 'yan matasa, Safwah na zaune akan gado ta kifa kanta a k'afafun ta suka shigo, har suka samu guri suka zazzauna batai noticing ba tsaban yadda tai nisa cikin tunani sanda wata three years old kid acikin su ta k'arasa kan gadon ta dafata ta d'ago a firgice ta tsare yarinyan da jajayen idon ta da kullum suke k'ara rinewa maimakon dawowa daidai, yarinyan kanta sanda ta tsorata da idanun Safwah.
Runtse ido tai saboda wani mugun ciwo da gefen kanta yake yi, tafi five minutes ahaka kafin ta bud'e ta soma bin yaran da kallo d'aya bayan d'aya, jiki a sanyaye wasu na kuka suka mata gaisuwa, du yadda suka so tai musu magana tak'i haka dai suka hak'ura suka tafi.
    Da daddare bayan kowa ya watse Granny tace da yaran kowa ya d'au matar sa ya tafi, haka kuwa akayi wucewa Suwayd yai d'akin da Safwah take dan d'auko ta su wuce gida.
    Tana kwance ta zurawa ceiling ido ya shigo, k'arasawa yai ahankali ya zauna gefen gadon ya mik'a hannun da niyyar jawo ta jikin sa ta zame da k'arfi, ahankali ya soma lallashi yana kwantar mata da hankali amma ina sam tama k'i fuskan ta, da yai attempting hugging ta ma ihu ta soma har Mammy ta shigo, masifa sosai Mammy ta rufe sa da ta kuma shaida masa ya d'au Zee ya tafi Safwah sai bayan arba'in wane zaiyi kuka ya soma bawa Mammy hak'uri amma sam tak'i jin sa dan bala'in haushin sa takeji ganin yadda Safwah ta lalace ta fice hayyacin ta, hakan ne ya tabbatar mata muzguna mata yake, wane zaiyi kuka ya fice, Zee na zaune ya fito cike da bala'i yace ”Dalla malama ki tashi mu tafi”.
Mamaki ya bata amma ganin yadda ransa ke a b'ace ta mik'e ta bisa suka tafi.
Koda suka je gida baiyi nakan ta ba ya wuce part d'in sa ya maidan da k'ofan yai locking, k'ofan da yasan zata iya shigowa tanan ma yaje ya kulle ya wuce bedroom d'insa, a bakin k'ofa ya zame sai kuka wane wani k'aramin yaro, kuka yake sosai saboda bak'in ciki da takaicin abinda Safwah tai masa.
    Sanda yai mai isan sa ya mik'e ya wuce toilet ya sake ma kansa shower, nanma wani kukan yasha kafin ya samu yai wanka ya fito, Sharp sharp ya shirya ya haura gado ya kwanta ya zurawa ceiling jajayen idanun sa yana tunanin ta har sarkin sata ya d'auke sa.
Zee ma na shiga part d'in ta tai wanka ta nema guri ta kwanta though b'acin ran nasa ba k'aramin tab'a ta yai ba itama haka dai ta kwana cike
da kewan sa.
    Haka dai rayuwan ya cigaba da tafiya there is no days goes by Suwayd baije gida ba duban ta amma sam bata bari su had'u, zuwa lokacin hauka ne kawai bai ba dan two weeks kenan amma tun daren ranan bai sake sanya ta ido ba kuma inya k'irata bata picking.
   Tana kwance a bedroom d'in Ummy ta lumshe idanun ta da suka shige ciki wane maijin bacci ta jiyo muryan sa, ajiyan zuciya ta sake dan tasan baya iya shiga bedroom d'in ta Ummy.
Kallon sa Ummy tai gwanin ban tausayi dan yai bak'i ya rame wane bashi ba, da raunin murya yace ”Ummy tana ina?”
    Dakai kawai ta masa alama, du kunyan da yake ji yau ya neme ta ya
rasa ya mik'e da sauri ya shiga d'akin, maida k'ofa yai ahankali yasa lock yadda barata ji ba ya k'arasa.
Tsayawa yai yana k'are ma milk armless silky rigan dake jikin ta kallo kafin ya hau gadon ya mata rumfa da faffad'an k'irjin sa, a rikice ta bud'e ido tana kallon sa dan ta d'au k'amshin turaren sa data jiyo kusa iska ne ta kawo mata.
     Zuba mata lazy eyes d'in sa yai yana binta da wani irin kallo mai cike da kewa da tsanin buk'atan kasancewa da ita, nan take kuwa ya kashe mata jiki ta juyar da kanta gefe dan bazata Jure kallon nasa ba, matsan da fuskan sa ya soma yi zuwa nata yasa hannu ahankali ya juyo da fuskan ta suna kallon Juna, kafin tai wani yunk'uri yai shutting ta da wani irin had'amammen kiss, kissing ta yake passionately yet affectionate in a demanding way yayin da hannun sa d'aya ya samu masauki cikin rigan ta squeezing her boobs roughly, du yadda taso dakatar da shi ta kasa dan sosai take enjoying abinda yake mata, tun tana k'in basa had'in kai hartai giving in wa abun suka soma romancing juna like never before.
     Tsaban yadda suka shagala har wani juye juye suke ganin suna neman cinye juna na basu guri, tunda ya shiga d'akin Ummy ta fice ta tafi gurin Kadsah dake fama da mugun laulayin ciki wanda Sam batasan tana dashi ba sai iyayen, cikin yazo mata da wani irin laulayi mai mugun ban tausayi dan ko ruwa bai zama acikin ta inta sha, ta zabge ta rame du ta fice hayyacin ta wane ba ita ba, lokacin da Musty yaga halin da take ciki sosai ciwo ya sake kwantar dashi saboda tsantsan so da tausayin ta.
Koda na koma still romancing juna suke, jin ya soma k'ok'arin wuce gona da iri ta nemo nutsuwan ta nan take ta kwace kanta, rik'o ta yai jikin sa na rawa idanun sa du sun chanza launi ya soma lallashi, ganin da gaske yake kawai ta sa masa kuka cause abinda zai iya kwatan ta daga gare sa kenan tunda baso yake ba, k'ank'ame ta yai ajikin sa yana maida numfashi sanda ya samu nutsuwa ya lalibo rigan ta ya miyar mata yai adjusting shima ya mik'e dakyar ya fice.
    Tunda akai mutuwan kuka ya k'aurace mata sai yau, yinsa ta soma yi sosai ko ta rage abinda take ji a zuciyan ta, gaba d'aya ranan koma mata yai wane ranan tai tozali da gawan Twiny d'in ta, kukan da take har ya wuce na hankali dan yadda take kokawa da numfashin ta, jikin ta banda kakkarwa ba abinda yake ga bala'in ciwon kai.
   Haka Abuh ya shigo ya same ta, da sauri ya k'arasa ya d'ago ta ya k'ank'ame cike da bala'in tausayin ta, ya sani ba abinda tafi buk'ata a lokacin sama da kukan dan haka ya kyale ta, ya soma shafa bayan ta ahankali sanda tai mai isan ta tai shiru, zame ta yai daga jikin sa ahankali ya rik'o hannun ta both ya soma mata nasiha mai ratsa jiki though shima daurewa kawai yake.
Ahaka Ummy tazo ta same su itama ta d'aura da nata, sanda suka tabbatar nasihan ya shige ta Ummy taje toilet ta had'a mata ruwan wanka, har k'ofan toilet Abuh ya raka ta ya dawo ya zauna cike da damuwa, kallon Ummy dake goge hawaye yai ya mik'a hannu ahankali ya jawo ta jikin sa ya rungume, hakan ne ya bata daman sakin nata kukan dan dama tana daurewa ne kawai dan ta k'arfafa ma d'iyan tata gwiwa.
Tun daga ranan Suwayd ya soma k'irga wane sha-sha-sha, Zee kuwa inta gansa da safe barata k'ara ba dan sai tayi bacci ma yake dawowa, sandai inya tashe ta da asuba taga ashe nan ya kwana.
   Ta fannin Safwah bata sauya zani ba dan bata sake yarda sun had'u ba kuma bata d'aga wayan sa, tsakanin ita da Kadsah an rasa wa yafi damuwa da damuwan wani dan kowacce da amanan kowacce kanta.
Yauma suna zaune abin tausayi Kadsah tasa Safwah'n gaba da abinci tana hawaye tana rok'on ta taci amma, sanda Kadsahn tasa mata kuka like domin shi tazo duniyan sannan ta daure taci five spoon, haka itama tasa ta agaba tasha Lipton dakyar then suka nemi guri suka kwanta.
    A kwana a tashi ba wuya gurin Assamadu har ranan arba'in ya dawo, an cika sosai anyi addu'a anyi karatu Allah yakai lada wa mamacin, allura akai ma both Safwah da Kadsah dan kowa ya soma tsorata da lamarin su.
Haka dai har kowa ya watse, da dare Granny tasa aka k'ira mata Safwah, lokacin da Safwah taji dalilin kiran k'aramar hauka ta soma.
    ”Kiyi hak'uri Granny bazan koma gidan sa ba, all I need is takarda ta i don't love him anymore dan Allah karkuce na koma wallahi zaku rasa ni, natsane sa bana son sa, kafin Twiny ya mutu haka yake cewa nadena son sa Ya Suwayd nake so, Wallahi Twiny kazo kaji zan fad'a a gaban ka bana son sa na tsane sa bazan koma gidan sa”.
     Da sauri Kadsah ta rik'o k'afan Granny tana hawaye sosai tace ”Granny dan Allah don't force her na masa alk'awari no matter what barin bari ayi mata abinda bata so ba, dan Allah kuce ya bata takardar ta in hakan zai faran ta mata rai”.
      You guys can't believe if i said by the time Suwayd is helplessly crying hakan yasa iyayen shiga  tsananin mamaki da rud'ani.
Rik'e hannun Safwah Kadsah tai suka wuce d'akin su suna kuka abin tausayi, k'ank'ame k'afan Granny Suwayd yai crying so hard in crack voice ya soma magana ”Itace rayuwa ta dan Allah karku rabani da ita, wallahi bazan iya sakin ta ba saboda tsananin so da k'aunar da nake mata, Granny ke shaida ce akan *MAKAHON SO* da nake mata dan Allah kiyi musu bayani”.
D'agoshi tai ta rungume cike da tausayin sa tana bubbuga bayan sa wanting to calm him amma ina, dakyar ta samu ta lallab'a sa yai shiru tace ya tafi bayan kwana biyu zata dawo masa da matar sa, dakyar ya tafi dan gani yake kaman inya tafi shikenan ya rasa bugun zuciyar sa.
     Ganin yadda iyayen suke cike da mamaki Granny ta fayyace musu komai, Murmushi Ammey kawai tayi dan dama tayi suspecting haka, juya Sayyid yai da sauri yana hawaye ya fad'a motan sa yai gida, daren ranan bai runtsa ba yana kuka saboda tsananin tausayin Suwayd, lallai shiya fi DACEWA _Mamuh gee_ ya auri Safwah, haka ya Kwana da k'udirin mayar masa da Safwah gobe ko bata so.
      The following day
Misalin k'arfe hud'u tana kwance Sayyid yai sallama ya shigo, tsaban yadda tai nisa a duniyan tunani ko sallaman nasa bata ji ba, k'arasawa yai ya nemi guri gefen gadon ya zauna, yafi minti biyu yana kallon ta kafin ya d'an ja gefen rigan ta, hakan yasa ta d'agowa tana kallon sa batare da tace komai ba.
      Ganin ta soma hawaye yasa hannu ahankali ya mik'an da ita zaune ya rungume, hakan  ne ya bata daman fashewa da masifaffiyar kukan dake cinta.
Suwayd na gama shiryawa ya d'au hanyan gida dan zuwa ya bawa *PureLamp* tasa hak'uri, gudu sosai yake hakan yasa bai wani d'au lokaci ba ya iso, part d'in Ummy yai deciding soma zuwa sai kawai ya wuce na Granny, ganin bata falour ya wuce d'akin su Safwah kai tsaye, kansa a sunkuye ya shiga ya maidan da k'ofan ya rufe, juyowan da zaiyi ya gansu mak'ale da juna, nan take zuciyan sa ta soma bala'in tafasa jijiyoyin kansa suka mimmik'e saboda azaban kishi, bud'e k'ofan yai ya fice yai banging da k'arfi hakan yasa ta sake k'ank'ame Sayyid dan ta mugun firgita, shima a tsorace yabi k'ofan da kallo dan ko ba'a fad'a ba yasan Suwayd ne..........

Follow
Vote and
Comment on Wattpad
@Shuwerh Beelkeey22

MAKAHON SO ~Blinded Love~

*'Yar Gatan Miss_B_Hal Ce*💞

Continue Reading

You'll Also Like

267K 18.5K 56
ABHIMANYU RATHORE :- Rude , workaholic CEO of Rathore Empire .Devilesing hot , every girls drools over him .But loves his family to dearest . . SAKS...
4.3M 236K 49
"Stop trying to act like my fiancée because I don't give a damn about you!" His words echoed through the room breaking my remaining hopes - Alizeh (...
200K 15.5K 35
𝐕𝐈𝐇𝐀𝐀𝐍 ♡ 𝐑𝐔𝐇𝐀𝐍𝐈𝐊𝐀 Ruhanika, a quiet introvert with a passion for books and study. She thrives in the world of words, finding solace in...
111K 14.8K 32
#Book-3 Last book of Hidden Marriage Series. 🔥❤️ This book is the continuation of the first and second book "Hidden Marriage - Amazing Husband." If...