SANGARTA COMPLETE

De ZulayheartRano89

120K 6.6K 88

labarin soyayya da ban tausayi Mai multe

part 1
BABI NA BIYU
BABI NA UKU
BABI NA HUDU
BABI NA BIYAR
BABI NA SHIDA
BABI NA BAKWAI
BABI NA TAKWAS
BABI NA TARA
BABI NA GOMA
BABI NA SHA DAYA
BABI NA SHA BIYU
BABI NA SHA UKU
BABI NA SHA HUDU
BABI NA SHA SHIDA
BABI NA SHA BAKWAI
BABI NA SHA TAKWAS
BABI NA SHA TARA
BABI NA ASHIRIN
BABI NA ASHIRIN DA DAYA
BABI NA ASHIRIN DA BIYU
BABI NA ASHIRIN DA UKU
BABI NA ASHIRIN DA HUDU
BABI NA ASHIRIN DA BIYAR
ASHIRIN DA SHIDA
ASHIRIN DA BAKWAI
ASHIRIN DA TAKWAS
ASHIRIN DA TARA
TALATIN 30
TALATIN DA DAYA
TALATIN DA BIYU
TALATIN DA UKU
TALATIN DA HUDU
TALATIN DA BIYAR
TALATIN DA SHIDA
TALATIN DA BAKWAI
TALATIN DA TARA
TALATIN DA TARA
ARBA'IN
ARBA'IN DA DAYA
ARBA'IN DA BIYU
ARBA'IN DA UKU
ARBA'IN DA HUDU
ARBA'IN DA BIYAR
ARBA'IN DA SHIDA
ARBA'IN DA BAKWAI
ARBA'IN DA TAKWAS
ARBA'IN DA TARA
HAMSIN
Complete

BABI NA SHA BIYAR

2.2K 136 0
De ZulayheartRano89

*NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*
*(NWA)*

                 *SANGARTA*

                        ©
            *ZULAYHEART RANO*

       *Sadaukarwa ga Khadija s Muhammad my Cittah*

_*AYSHA WAZIRI kina raina har na rasa bakin da zan ya beki, amma duk da haka Allah ya tsare ki a duk inda kike ya kare ki da sharrin mahassada and  kuma ba zan manta da ke ba i heart you*_

*Fans Ina jin korafin ku, amma Please kuyi hakuri wallahi harkoki ne suka yi min yawa amma insha Allah zan yi kokari na rika yi maku post a kai akai, don farin cikin ku shi ne namu, in babu ku tofa muma babu mu, a dai ci gaba da hakuri, tare da bin Yar Mutan Rano sannu a hankali* jin jina ga surbajo novel👍

''' My Besty taki salon ta daban ce, Yaseen ina mugun yinki'''😍😍

                      *15*

Mamaki karara ne a fuskar Meena, ido kawai ta zuba tana kallon ta, tsawon minti biyar sannan a hankali ta saki ajiyar zuciya ta ce

"Meesha me ki ke nufi? Shi Najeeb kuma ya za ki yi da shi?"

"Shi ma ina son sa, Meena ba zan ɓoye maki ba ina son Dr ɗan fullo har cikin zuciyata,so fa ba na wasa ba, wallahi kar ki so kiga halin da na shiga da jin maganar auren sa."

" Kar ki damu da auren sa, ki sa a ranki in mijinki ne zaki aure shi ko da yaushe ne, amma abin da yake bani mamaki yadda kika ce shi ma Najeeb kina son sa."

" Eh ina son Najeeb saboda yana da halayya masu kyau, amma so ɗaya tak yana ga Dr Asmad."

"To Allah ya zaɓa mafi alheri."

"Amma Please Meesha ki yi kokarin danne son sa a zuciyar ki kar ki bari ya sani, ki ci gaba da dauriya har ya furta maki da kansa yana son ki."

Murmushin takaici ta yi ta ce

"Haba Meena kema kin san halina, ba zan taɓa bari ya sani ba ko da kuwa son na sa zai zama ajali..."

Saurin toshe mata baki Meena ta yi ta ce

" Please bar maganar ajali insha Allah zaki auri Dr ke dai ki ci gaba da addu'a ni ma zan ta ya ki, ba ri na kawo maki abinci."

"Ko kar ki kawo na koshi."

Harara Meena ta jefa mata cikin wasa ta ce

"Ai ko ya zama dole ki ci abinci, don baki zama da yunwa."

Ta ida maganar tana sauka daga gadon, Meesha kam gyara kwanciya ta yi tare da lumshe ido.

Gidan ango Asmad kuwa ana ta shan angonci, zaune ya ke a babban falon gidan daga shi sai singlet da gajeren wando, laptop din sa ya ke matsawa, zuciyar sa cike da tunanin Ameesha wacce ya kwana biyu bai ganta ba, inda so samu ne yau ya leka asibiti don babu mamaki ta na ciki a yanzu haka, sai dai ya san halin yar matsala wato Aneesa, tana iya hana shi fita.

Lokacin da ya ke tunanin, tana tsaye a bakin koriɗo ta zuba masa ido, cikin wani irin shaukin so. Ita dai Allah ya jarabeta da son wannan bawan Allah, cikin kwalliya  ta ke kai da gani kaga amarya, kai tsaye wajen sa ta nufa da zuwa bata jira komai ba tasa hannu tare da zare laptop din, ta wani narke fuska kamar za ta yi kuka ta ce

" Haba Hamma aikin me kake ta yi ne har yanzu, ya ci fa a ce kana samun hutu"

Kallon ta ya yi tare da ɗan sakin murmushi ya ce

"Ban da abin ki ina hutu a wajen Dr? Ke dai kawai kin rasa abin korafi, yanzu ma tashi zan yi in shiga asibiti don duba petient  ɗina."

Saurin ɓata rai ta yi ta ce

"Haba dai tun yanzu zaka soma fita, ina laifin ka yi one week a gida?"

"Ba zai yiwu ba ne Anee da na yi hakan, yanzu dai tashi muje ki haɗa min ruwan wanka,in yi shaf shaf."

Ba don ranta ya so ba ta mik'e, shi kuma ya saki murmushi kawai ya kashe laptop din.cikin sauri sauri ya kammala da shiryawa, sam Aneesa ta ki saki rai ita a dole kar ya fita.

A haka ta rako shi wajen motarsa

" Please Hamma kar ka daɗe."

" Ba zan daɗe ba My Anee."
Ya faɗa cikin tabbatar da abin da ke ransa.

" Allah ya tsare hanya ya dawo da kai lafiya."

Ta faɗa tana rufe masa kofar motar

"Allah ya sa" shi ma ya faɗa yana ba motar wuta.

**********************************

"Najeeb! Alhaji Taheer ya kira sunan sa cikin murya ta nutsuwa.

Najeeb da ke zaune gaban Abban Ameesha ya amsa cikin ladabi.

"Kasan abin da yasa na kira ka?"

Alhaji Taheer ya tambaya.

Girgiza kai ya yi ta re da faɗin

"a'a Abba."

" Yawwa to akan maganar ka da Auta ne, shin da gaske ka ke sonta ko kuwa?"

Dukar da kai ya yi , cikin sanyin murya ya ce

" Eh Abba."

Murmushi ya saki ya ce

"Allah ya yi maka albarka, na gode sosai, insha Allah zamu zauna da Mahaifin ka domin tattauna maganar, saboda bani son aja maganar."

"To Abba na gode."
Najeeb ya faɗa.

"Dama shi ne dalilin kiran tashi ka ta fi."

*********  ********  ******* ******

Ko da Asmad ya fita kai tsaye gidan su Nenne ya nufa, don ya kwashi gaisuwa  a babban falo ya same su, sallama ya yi su, su ka amsa masa cikin kulawa.

("Nenne a nyalli jam? Bobbo a nyalli jam?) "Nenne ina yini? Bobbo an yini lafiya? "

("Jam kolon Asmad noi Aneesa?")" Lafiya lau Asmad ya Aneesa? "

("O jamo kolon,owi mi hofnna mon.") " Tana lafiya, har ta ce a gaida ku. "

(" Min notii Allah wadbarka.") " Muna amsawa Allah ya yi Albarka. "

("Ameen Asmad noti.") "  Amin." Asmad ya amsa

(" Wala damuwa fere Kam?) "Babu dai wata matsalar ko? "

(" Wala ko d'ume Bobbo,minastan noo asibiti on miwi hami yalta mihofna on") "  Babu komai Bobbo, dama zan shiga asbiti ne na ce bari na biyo don na gaida ku. "

("To usoko Allah barkid'in ummu dillu de jam kam da alari kanko fere mako a accimo ha sare useni jogumo amana ta awada ko a wasmititta Yesu.") "  To masha Allah tunda lafiya, ka tashi ka tafi kaga dai ita d'aya ka bari a gida, abin da dai nake kara jaddada maka shi ne ka rike amanar Yarinyar nan, kar ka yadda wani abu ya shiga tsakanin ku na sabani, har ya sa ka aikata dana sani. "

("Insha Allah mi mi hakkilan Bobbo.") " Insha Allah Bobbo zan kiyaye. "

("To Allah wallu") " To Allah ya taimaka. "

(O lari agogo jungo mako dendenta o ummii.) Agogon hannun sa ya kalla tare da mikewa.

(" Nenne minkam mi salan.")" Nenne nikam na ta fi. "

("Allah hoinu lawol a yaltan naa to ad'on qarya?") " Allah ya tsare hanya, zaka biyo ne in ka dawo? "

("Kai gonga miyaltata Nenne mi salan sare on.") " Kai gaskiya Nenne da kamar wuya, don ina tunanin gida zan wu ce. "

"(To Allah karu.") " To Allah ya tsare. "

("Nonnon Asmad wurti sare man odon der seyo.") Da haka Asmad ya fita a gidan cikin farin ciki da annashuwa.

Yana parking motarsa a parking space, ya fito nurse na Asibitin sai masa barka da zuwa suke tare da ta ya shi murnar aure, fuska a sake ya ke amsa masu har ya isa kusa da ofishin sa.

Yasa hannu zai buɗe kofar kenan ya hango ta, zuba mata ido ya yi cikin wani irin yanayi, sai ya ga ta rame ta ɗan kara tsawo, da yaga suna shirin haɗa ido sai ya yi saurin fuskewa

Wani irin daɗi ya ziyarci zuciyar Ameesha, ganin Dr yau a asibiti, ji ta yi duk wata damuwar ta ta ragu. Amma a zahiri sai ta kuma haɗa rai kamar zata ce wayyo Allah.

" Da gani ansan ango ka ke musamman yadda goshi ke kyalli."

Tayi maganar cikin zuciyarta, tare da saurin maida kwallar ta don kar ya gane .

"Barka da zuwa Dr."

Ameesha ta yi maganar a hankali, cikin nutsuwa.

Dan juyo da kai ya yi ya kalleta ya ce

" Yawwa ."

Bata ce komai ba sai ci gaba da tafiyar ta ta yi, har ta ɗan gota shi ya ce

" Ke ina son magana da ke?"

Juyowa ta yi tare da murguɗa baki ta ce

" Ba sunana ke ba Maryam Taheer sunana."

"Nice name." ya faɗa a zuciyar sa, amma a fili sai ya ce

"Oh! Ai ban ma san sunan ki ba, to Maryam ina neman ki."

Ya ida maganar ya na shiga ofis ɗin, ita ma Ameesha binsa ta yi, kujera ya nuna mata ya ce

"Zauna."

Ba musu ta zauna tare da duk'ar da kai k'asa.

Shi kuwa wasu file ya dauka yana dubawa, tsawon minti biyar babu wanda ya yi magana, ita Ameesha ci gaba da wasa da zoben hannun ta ta yi.

"Wai Maryam baki da labarin na yi aure ne?

Asmad ya yi maganar ya na ci gaba da abin da yake yi.

Wani mummunan faduwar gaba ya ziyarci Ameesha, da jin maganar sa duk da ta sani amma sai ta ji na yanzu ya fi ranar da ta soma jin maganar ta da hankali.

Amma sai ta yi saurin da kewa ta ce

"To kuma me hadina da auran ka?"

Ta yi maganar tana hararan sa.

"Oh! Ashe fa ba ruwan ki da aurena? Amma ai yana da kyau ko murna ki ta ya ni."

Wani kallo ta watsa masa wanda ya kasa fahimtar ma'anar sa.

Yau dai yana son ya ga shin Ameesha ta na sonsa, in tana sonsa zai tabbatar ,don haka sai ya tashi daga kujerarsa ya matsa inda ta ke, hannun ta ya rik'o ya ce

"Maryam me yasa ki ke min rashin kunya baki ganin girma na, kullum kallon tsana ki ke min?"

Juyar da kai ta yi murya na rawa ta ce

"Please Dr ka sakar min hannu, sauri na keyi fa Ummi na jirana."

"Zan barki amma sai kin bani amsar tambayar da na yi maki."

"Babu komai."

Ameesha ta ba shi amsa, dai dai da zubowar hawayen da ta e ɓoyewa, hankalinsa ya tashi da ganin hawayen Ameesha, don haka cikin sauri ya ce

" Iya sani na na taɓa marin ki a Sahad store, kuma shi ɗin ma wallahi ke ki ka jawo, domin kuwa in da ban mareki ba, to fa babu shakka ni zaki mara, amma ki yi hakuri ga fuska ta ki rama marin."

Maimakon hawayen su tsagaita sai k'ara tsiyaya suke, a kan fuskar ta tama kasa furta komai, don abin da ta ke son ji daga gare shi bai furta mata ba, duk da tasan da kamar wuya ta samu wannan tsadadden kalmar daga gare shi.

Asmad kuwa zuba mata ido ya yi yana kallon ikon Allah, zuwa can yasa hannu cikin aljihu ya cire hankacif na shi ta re da mika mata.

"Sorry Maryam ki bar kuka, ga shi ki share hawayen ki."

Ya kai karshen maganar yana mik'a mata.

Amsa tayi tare da goge hawayen da hankerchief ɗin da ya mika mata, sai ya kuma jan hannunta kamar dai wata karamar yarinya, zuwa kan doguwar kujerar da ke office din, ya zaunar da ita sannan shi ma ya zama .

Sanyaya murya ya yi ya ce...

_*Yar Mutan Rano*_

Continuă lectura

O să-ți placă și

49.9K 6.6K 55
"ඒයි ඇටිකිච්ච ඔහොම ඉන්නවා" "නේත්‍ර, නේත්‍ර... මගේ නම නේත්‍ර" "මොකද උඹේ කට ඔච්චර සද්දෙ, මට ඔය වයසට වඩා උඩ පනින්න දඟලන ඇටි කිච්චන්ව පේන්න බෑ. ඒ නිසා මට...
15.9K 1.6K 18
" ඇයි අයියෙ ඔයා කොයි වෙලෙත් මාව සුදු අරලිය මලකට සමාන කරන්නෙ.." මං අයියගෙ මූන දිහා බලන් අහනකොට එයා මගෙ ඇස් දෙක දිහා බැලුවා.. මගෙ අයියගෙ මූනෙ ඇඳිලා තිබ...
56.8K 1.2K 26
.. a story, of a girl who has a condition that could change her life for the greater good. Loni has a medical condition that stopped her from develop...
812K 16.3K 112
Yaszy Romano has been through so much pain and suffering her entire life but it makes her who she is. Dark Angel...Dangerous, Powerful. An Assassin...