AUREN WUCIN GADI

By zahraaliabdullahi5

19.5K 1.7K 78

labarin wani matashi daya auri wata yarinya na wucin gadi saboda wani dalilin sa. More

1
2
3
4
5
6
7
8
9
10
11
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
37
38
39
40
41
42
43
44
45
46
47
48
49
50
51
52
53
54
55
56
57
58
59
60
61
62
63
64
65
66
68
67
69
70
71
72
73
74
75
76
77
78
79
80
81
82
83
84
85
86
87
88
89
90
92
91
93
95
96
97
98
99
END

94

272 18 5
By zahraaliabdullahi5

💕 *AUREN WUCIN GADI* 💕

✨ *GORGEOUR WRITER'S FORUM*
        ✨G.W.F✨

CHAPTER 94

Wani irin sauri Alkali Sada yake kaman ze kife ƙasa saboda tsaɓan ruɗewar da yayi yabi ta wata ƴar ƙofa datake ta cikin kotun ta bayan inda Alkali yake zama tanan yabi zuwa ainihin inda  Ofishin Alkalai suke ajejjere,shiga ɗaya daga cikin ƙofofin da suke jere awajen yayi kasa zama yayi sai kai komo yake yama rasa wani irin tunani zeyi.

Duk ya ruɗe ya ɗimauce take wani irin zufa ya karyo masa,yana cikin wanan halin Barrista Tafida ya shigo yana cewa"haba yallaɓe ya zakayi mana haka kuma?ina ganin nasara ta tunkaroni ina kallon kaina matsayin miloniya tsanina da nasarata be wuce taku biyu zuwa uku ba kasaka ƙafarka kayi fatali da ita why why why yallaɓa why?saboda idon sa yariga da yarufe be kula da halin ko ince yanayin da yasami Alkali Sada ba,shi dan gani yake kaman da gangan Alkalin ya ɗaga karan,ya kare maganan sa kaman zeyi kuka mission impossible sunan wani film,sassauta ɗaurin neck tide dinsa yayi yana daukan ruwan gora daya gani saman table din dake Office ya ɓalla murfi yakafa baki yasoma ƙwanƙwaɗa.

Duk wannan hargowar na Barrista Tafida hakan besaka Alkali Sada yi magantu ba,shima din ruwan yake da bukata dan jika maƙushin sa,saida yasha ruwa mai sanyi sosai ji yayi kaman wani abu dayake tokare a maƙoshin ya wuce,saida yakai zaune sannan yace" ina Tafida yake?"gani ranka yadaɗe ya amsa cike da girmamawa,numfasawa yayi naya cewa"inaga kai baka ga abunda ni nagani bane shisa kazo ka cikani da surutu.

"Me ka gani Ranka yadaɗe?wakilai ne sukazo don saka ido kan wannan shari'a wace hukunci zan yanke"what?Barrista Tafida ya faɗa yana ɗan zare ido"kwarai kuwa dan haka inaga idan katashi daga nan kawoce Gidana kai tsaye kudin nan daka kawo mun su jiya ko sisi ban taɓaba dan haka kadauka ka kamaida musu da abun su kuma kace CIKI DA GASKIYA WUKA BAYA HUDA SHI.

Gaskiyar suce kaɗai abunda ze kwacesu"amma Ranka yadaɗe...ɗaga masa hannu Alkali Sada yayi yana cewa kaga Tafida akan su bazan ɓata,aikina dama sunana baki ɗaya ba,shekara ɗaya da rabi yarage mun barin aiki gwara nabar aiki ana mai darajani ba Allah wadai dani ba,ni tunda nake ban ma taɓayin shari'ar rashin gaskiya da zalla son zuciya irin ta yau ba nasan dawaya cikin ƴan kallo sunyi ta Allah wadai dani saboda rashin adalci kiri kiri dana nanu awajen inaga dalili kenan da aka turo ƴan ganin kai daga ƙungiyar kare hakkin dan Adam wato human right.

"Haba Ranka yadade kai wani abu mana yanzu ina ji ina gani zan rasa million goma harfa da sabuwar mota za bani,haka barrista Tafida yake ta sambatu shide Alkali Sada tunda ya faɗamasa yaje Gida ya dauki kudin yamai dama  masu shi abun su besake yin magana sai addu'a dayake tayi na Allah yadaura shi a saman su kawai yake kai karshema cewa yayi da Barrista Tafida dan Allah ya fita masa daga Office yana bukatar kebewa bayason yawan surutu da yake masa haka barrista Tafida yafita daga Office din jiki a mace dan shi yagama lissafin abunda zeyi da kudin.

******
Da ɗan gudu Ammi ta nufi inda Ahmad yake tsaye bayan mutane ƴan ɗauka rahuto sun fiffito abun be musa daɗi ba can na hango Mom Islam hannunta rike da biro da takarda sai cizon  biron take da alama ba haka taso ba,taso tasamu na rubutawa amma Alkalin kotu ya gudu saboda tsaro ba tsoro ba,ni kaina ba hakan naso ba amma ya na iya da samarin kakata haka de na hakura nafito na raɓa ta can gefen inda Ahmad yake tsaye na rakuɓe na tsaya ina jiran suje gida nima in bisu inje dan sake ganin wata wainar za'a toya kuma a can.

Yaude Ammi ta kauda kunya ta rungumi ɗanta ɗaya tilo ɗa mafi soyuwa a ranta,a bayyanar jama'a  tasaki kuka tana cewa"ka gade ga abunda Mahaifinka ya zaɓarma kansa yafi son yamai daku marayun karfi da yaji ni kuma ya maidani bazawara da girmana,mutum da mutuncin sa yazaɓi yin shiru koda mutuncin sa ze zube shi bedamu da hakan ba,ba ruwan shi da ya makomarmu zata kasance bayan babu shi"Ammi kiyi shiru kidena magana kinga mutane suna kallon mu mu tafi gida idan yaso sai muyi magana,yafaɗa mata hakan ne san ganin hankalin wasu daga cikin masu wucewa ya fara yowa kansu.

Ko kallon inda Mahaifin nasa yake beyi ba,haka yafara takawa rungume da ita saida yakaita mota  yabude mata tashiga ta zauna yarufe motan sannan yaxo yasami Faisal da Barrista Anwar da Janar ɗan Musa mahaifinsu Faisal sai Alh sunusi dama wasu da dake tsaye awajen suna ma Alh badamasin barta da Arziki,su Alhajj sunusi sunde shiga tsawun masu yimasa barkar ne amma zuciyar nan tasu tayi baƙi ƙirin dan bakin ciki  yanzun ma sun tsaya wajen ne gudun mutane su zargi wanibu akan,duba da yanda suke da Alhajin  amma Allah Allah suke su var wajen su kira Alkali da Barrista suji wai meyakawo canjin lokaci ɗaya su suna ganin sun gama komai inde haka ne akwai sauran aiki a gaban su.

Kalle shi tsawon shekaru da dama ya zauna ana juyashi saboda yariga ya damƙa musu yaruwar sa a hannun su sai yanda sukai da ita,baya da kataɓus sai abunda su sukace.

"Ammi ki dena faɗan haka ba kyau kinga hankalin mutane yafara yowa kanmu muje gida idan mun zauna sai muyi magana gyada masa kanta tayi shiya jata a mota saida yabude mata tashiga ta zauna ya rufo murfin motan sannan yaxo suka gaida dasu Barrista Anwar da Janar ɗan Musa mahaifin Faisal yana cewa dasu su haɗu a gida ko kallon inda Mahaifin sa yake tsaye beyi ba,shima din beyi tsamman zeyi masa  magana ba dan sanin halin sa da zuciyar sa.

Dukan su mota suka shiga suka dunguma zuwa gida Alhaji badamasi,Janar ɗan Musa yana nashi motar driven sa soja sanya da kakinsa yake jansa sai Barrista Anwar da shima yake tasa motan sai Alhaji badamasi dayake nashi motar shima drivern sane yake jansa Ammi kuwa tana tare da Ahmad a nashi motan,Barrista Anwar ne yakira Faisal ta waya yake sanar masa da su haɗa a gidan su Ahmad yanzu suma suna kan hanyarsu ta zuwa"lafiya de Barrista kode shari'ar batayi daɗi bane?Faisal ɗin ya tambaya duka a tare dan shi besamu shigowa Kotun ba saboda wani aiki dayashi masa kai.

"Lafiya amma ba lau ba Faisal dan wallahi shari'a kwata kwata batayi mana daɗi ba,saide kasan ance duk abunda Allah be ɓatashi ba baze taɓa ɓaci ba,badan Allah ba da yau saide kaji wani labarin tsabanin wannan ɗin.

"Allah mun gode maka Faisal ɗin yarinƙa cewa sai kuma yasake cewa naji kace mu haɗu gidan su Ahmad din lafiya de ko?ko Ahmad din yashigo ne?"eh yashigo dan Allah kazo karka ɓata lokaci dan yanzu haka muma can muka nufa harda Daddy ɗinka"Ok gani nan zuwa ya amsa masa da haka yana kashe wayan.

Tafiyane suke kowanne cikin su da abunda yake sakawa a ranshi,shi kansa Alhaji badamasin zuciyarsa tana masa rawa gami da hukuncin daya ɗaukama kansa na yin shiru baze faɗi sunan kowa cikin wayanda sune suka sakashi cikin wannan halin dayake ciki ba, dan ma sunan sa ɗaya yake neman ɓaci ta sanadin su,anƴa yama Matar sa abun so da kaunar sa adalcin kowa?anƴa yama ɗansa abun alfarin sa adalci kuwa?dalilin wannan abun ne yasaka yaran sa mata ke zaune a gida basa zuwa Makaranta saboda gudun tsangwama da suke fuskanta a can makarantar tasu,ɗan sa yake gudun sa,amma sufa dasuka sakashi a wannan hali?suna can zaune da matayen su da yaran su lafiya cikin farin ciki da walwala ko ze cigaba dayin shirun ne dan kare rayukan iyalan sa kaman yanda yafaɗa musu tun farko,idan yayi hakan yamusu iyalin sa adalci kuwa? tunda bayason yarasasu ko yasaka rayuwarsu cikin haɗari.

Hakade shi kaɗai yaringa magana da zuciyan sa har suka isa gida besan sun isa ba saida drivern sa yace"yallaɓa ai mun karaso tun tuni tukun ya ankara ya fito daga cikin motan jiki ba kwari daidai Fadwa da Ummu salma sun fito da gudu jin dirin motoci yasasu fitowa ganin Yayan sune suka fara yimasa Oyoyo suka juya suka gaishe da Janar  da barrista Anwar amma ko kallon inda mahaifinsu yake ba suyi ba suka juya suka shiga ciki.

A falo suka zazzauna Ammi ce ta saka kuka irin mai cin rannan kukane daya tasone tun daga ƙasan zuciyarta yaran suna tayata duk taurin zuciya irin ta Ahmad saida ya zubda ƙwalla shi ba komai yakeyi ma kukan sai dan ƙannen sa da maza ne ma da sauki amma dukkan su matane ya rayuwar su zata kasance? wane mijine ze yarda ya aure su ba tare da ya goranta musu halin Mahaifinsu da duniya take masa kallon maci amanan ƙasa dama al'umma dasuka yarda dashi suka damƙa rayukansu a hannusa suna amfana da ilimi da Allah ya bashi na haɗa magunguna.

Katse masa tunani Janar ɗan Musa yayi sanda ya kalli halin da yaran suke cikin da Mahaifiyar su,juyawa yayi ya kalli Alhaji badamasi daya dukar da kansa ƙasa yakasa ɗagowa ya kallisu,gyaran murya yayi yace"Ka dubi Allah ka kuma kalli halin da iyalan ka suke ciki ka bude baki kayi magana ta yanda zamu sami makami koda ƙanƙanine.

Be ɗago ya kalle shi ba, be kuma amsa masa ba, shiru yamasa still kansa a ƙasa"ba zeyi magana ba saboda yana ganin shirun sa kaman ceton a halin sa zeyi abunda besani ba shine koda kayi shirun ba barin nasu za suyi ba,duk kansu kusan a tare suka zubawa ƙofan shigowa falon ido inda zuke jiyo murya,sanya yake da farin yadi mai shegen kyau yayi shigan manyan kaya kansa sanye da hula damanga dukka ya manyanta amma kyaun nan tasa na nan ga wanda yamasa farin sani mutum ne mai cikan kamala da dattako kusan a tare suka miƙe tsaye nunashi Janar ɗan Musa yayi da yatsa yana cewa"dama baka mutu ba kana raye?

"Wanake gani haka kaman Ishaqu cewar Ammi tana mai bayyana mamakin ta.

"Dama dama kana raye ɗan jarida cewa Alhaji badamasi da dakyar ya iya haɗu maganan yayi ta saboda ɗaukewar da ƴawun bakinsa yayi lokaci ɗaya,Anwar da Ahmad kuwa ƴan kallo suka koma anan suna kallon yanda iyayen nasu.

Murmushin su na manya yayi yana cewa"ban mutu ba ina raye Janar"Amma ina kashiga tsawon wannan lokacin?yasake jeho masa da tambaya"hmm labarine mai tsawo Janar ɗan Musa zamuyi ta data baya.

"Zauna mana Ishaqu zama yayi suma dukan su zaman sukayi,kallo Alhaji badamasi yayi yana cewa dashi"shirun ka baze hanasu ai watar da mugun nufunsa kanku da Iyalinka ba,abu mafi sauki kawai shine kabude bakin ka ka faɗa musu wace alaqa ke tsakanin ka da Alhaji Sunusi dama Alh Shehu Alh Surajo rumbun kunɗi da Na Allah G.G.B....


ALLAH YASA MUDACE

Continue Reading

You'll Also Like

704K 40.9K 35
|ROSES AND CIGARETTES Book-I| She was someone who likes to be in her shell and He was someone who likes to break all the shells. "Junoon ban chuki ho...
3M 195K 89
What will happen when an innocent girl gets trapped in the clutches of a devil mafia? This is the story of Rishabh and Anokhi. Anokhi's life is as...
426K 40.9K 32
She is shy He is outspoken She is clumsy He is graceful She is innocent He is cunning She is broken He is perfect or is he? . . . . . . . . JI...
1.9M 141K 63
"ရှင်သန်ခြင်းနဲ့သေဆုံးခြင်းကြား အလွှာပါးပါးလေးကိုဖြတ်ကျော်ခါနီးမှာမှ ငါမောင့်ကိုစွန့်လွှတ်တတ်ဖို့ သင်ယူနိုင်ခဲ့တယ်၊ လူတွေက သံသရာမှာ ရေစက်ရယ်၊ဝဋ်ကြွေး...