AUREN WUCIN GADI

By zahraaliabdullahi5

19.5K 1.7K 78

labarin wani matashi daya auri wata yarinya na wucin gadi saboda wani dalilin sa. More

1
2
3
4
5
6
7
8
9
10
11
12
13
14
15
16
17
18
19
20
21
22
23
24
25
26
27
28
29
30
31
32
33
34
35
36
37
38
39
40
41
42
43
44
45
46
47
48
49
50
51
52
53
54
55
56
57
58
59
60
61
62
63
64
65
66
68
67
69
70
71
72
73
74
75
76
77
78
79
80
82
83
84
85
86
87
88
89
90
92
91
94
93
95
96
97
98
99
END

81

168 18 0
By zahraaliabdullahi5

💕 *AUREN WUCIN GADI* 💕

STORY AND WRITEN
    ZAHRA ALI ABDULLAHI

✨GORGEOUS WRITTERS FORUM✨

    ✨G.W.F✨

CHAPTER 81

  "Oga wai me wannan yake nufine da mu?
Girgiza kansa yayi yana haɗawa da murmushi saida yakai zaune daga tsaye da yake sannan yace"shiɗin Jarumine sannan Jajirtacce baya taɓa juya baya akan abun harin sa,ire iren sa muke nema dan sune waƴan da zasu kawo karshen su GAGARA BADAU.hhhhhhh

Sake baki Mutumin yayi yana kallon Ogan nasu dake dariya yace"Oga kana nufin karshen GAGARA BADAU cuwa cuwa harƙalla?
Ya tambaya da mamaki"kwarai Mansur yanzu ne lokacin da GAGARA BADAU zasu san muna da jajirtattun ma aikata ba lusarai ba,sannan karshen su yazo dan ze sasu guduwa akan titi ne.

Mansur yayi dariya yace"Oga kace muyi shirin sakasu guduwa ya faɗa yana rage murya"yes Mansur daga randa GAGARA BADAU yayi tozali da A-B sai yayi acawe a wando duk da su biyun ba wanda yasan ɗan uwansa shine abun harin sa.

"Oga kana nufin kace Ahmad besan waye GAGARA BADAU ba?"kwarai be san shi ba,haka shima Gagara badau ɗin basu san junan su ba,ba wanda yasan ɗan uwan sa.

"Amma Oga waye shi wannan ɗin?

kuma wace al'aqa ke tsakanin GAGARA BADAU dashi A-B ɗin?

"Hmm ya sauke ajiyar zuciya ya danyi juyi saman kujeran da yake zaune sannan yace"daga randa ya karɓi aiki a nan ma'aikatan ya dawo mana da martabar mu,bashi da tsoro tun fil'azal har yayi aiki damu,na tsawun shakara biyar ya samu mana nasarori da dama yaɗaga martaban aikin mu kafin barinsa aiki NAPTIP ɗin.

Mutum ne shi wanda bashi da tsoro ko kaɗan baya tsoron ko wace irin barazanar ƴan jagaliya,shine mutum na farko daya taɓa nunawa Alh Rabe hannu yakuma jashi a titi ya makashi kotu da tarin hujoji yanzu haka yana Gidan Mazan yana girban abunda ta shuka.

Bansan dalilin komawarsa aiki damu yanzu ba,saide naji labarin an maka Mahaifinsa kotu bisa zargin sa bisa lefi uku 1kisa
2 fyaɗe dakuma
3fataucin miyagun ƙwayoyi.
Ina da ya ƙinin ko yanzu zuwa yayi dan samun hujja yake nema dan kare Mahaifinsa a kotu yashi komawa aikin da yabari na tsawun shekara biyar na tabbata yanason amfani da wannan daman dan wajen ganin ya kare Mahaifin sa daga zarge zargen da ake masa sannan ya gurfana masu lefin gaban kotu.

Kuma zuwan nan nashi cikin mu ze mana amfani dan kawo karshen waƴan nan azzaluman masu fuskoki biyu cikin al'umma.

"Oga wani irin fuskoki garesu?
"Hmmm Mansur ka cika tambaya to suɗin ba ko wanne irin mutane bane face Dattawa ne su masu faɗa aji jagororine su masu jagoran al'umma amma fa a baɗinin su wallahi idan aka budema su ko Kare  baze shinshine abubuwa da  suke aikatawa.

"Oga yasake kiran sunan cike da kwarin gwiwa dan yanaji aransa yasamu Uban gida da zeyi dashi  tare.

Ɗaga masa hannu yayi yana cewa"Mansur No more question duk da hanashi magana da Ogan nasu yasoyi saide ya magantu da cewa"inason za mowa ɗaya daga cikin tawagarsa,a shirye nake dan rasa rayuwata ga kare ƙasata da al'ummata yafaɗa yana ƙamewa a gaban Ogan nasu.

Kallon sa Sir Olufemi Oba yayi yana faɗaɗa fuskarsa yace"Allah yayi jagora daga haka yaja file ɗinda Ahmad ya aje masa yasoma dubawa, Mansur ɗinma fita yayi daga office din yana nufan nashi office din yana jin wani irin farin ciki a ransa,dan gani yake yau ne karon farko da zeyi aikin da aka ɗauke shi dan shi yakuma yi alkawarin taimakawa Ahmad din da abubuwan da shima yasani gami da abunda yake son yin aiki kai.

******
Aisha suna zaune suna kallon hotona kaman daga sama Fauza ta faɗo musu falon ba sallama balle neman izini tana shiga ta dallarawa Aisha wani mugun harara tajan dogon tsaki tace"Allah wadaran naka ya lalace yanzu Sajida lalacewar taki har takaiki bin miji daga AUREN WUCIN GADI sai ki liƙewa Yayah kamar kaska saboda rashin dajara.

Taƙare maganarta tana wani jijjiga jiki,da mamaki Sajidan ke kallon ta dan ita batasan ma me take cewa ba"ta bude baki da nufin tayi magana kenan sai Fauza ta rigata tana cewa"karkiyi sammanin dan kin riga wasu shigowa ki ɗauka kedin ta dabance ki mike ƙafa ki zauna gwara ki zauna a ɗosane dan da zaran mai waje tazo dolen dolenki ki naɗe ta barmarki ki bar waje.

"Ikon Allah wai Fauza lafiyan ki kowa yau kode baki da lafiyane?kuma maganan me kike nifa bansan akan me kike magana ba,Sajida ta faɗa da damuwa saman fuskarta.

Madadin ta bata amsa sai kawai tace ke ta faɗa tana nuna Aisha da tun shigowarta kallo ɗaya ta mata ta dauke kai ta cigaba da kallon hotona da take,bata amsa mata ba saide ta ɗago ta zuba mata idon ta na mai kama da mai jin bacci .

"kizo Mami tana kiran ki tafaɗa tana yatsine fuska kaman wacce taga wani abun ƙi daga haka tayi gaba mikewa Aisha tayi ta rufa mata baya binsu abaya Sajida tayi.

Da sallama ta shiga falon ba wanda ya amsa sallamar nata daga Mami data sa akayi kiranta har ita Fauza ta wani hakimce saman ɗaya daga cikin kugerun alfarma dake zagaye da a falon ta harare ta ta motsa fuska.

Tsayawa tayi daga bakin ƙofa kanta a ƙasa"gani Mami tace cikin sanyin murya kallon ta Mami tayi sannan ta watsar kaman ba zatayi magana ba sai kuma tace"na ganki ai jita kamar wata ta kirki saboda munafirci wai gani tace tana kwaikoyon muryarta.

"Idan ba kyason barin Gidan nan dole kibi duk wata doka daxan gindaya miki da farko de meke a tsakanin ki da Amadu wace irin alaqace dake tsakanin ki da shi?

"Babu tace da ita a takaice.

Da sauri Fauza ta mike tsaye ta dire gabanta tana kallon ta cikin sakin fuska tace"maimaita abunda kikace yanxu,

"Eh ina nufin babu kawai shiɗin Oga nane kuma wani aiki muka zo yi nan din ta tsinci kanta da faɗin haka.

"Yauwa dama me nafaɗa miki Mami me Yah Ahmad zeyi da kucakar yarinyar nan amma baki yarda dani ba kinfi yarda da maganar da Yah Sajid yafaɗa miki sai kace ba jinin sa bace ni bansan abunda nasama ba da bayasona da Yah Ahmad ɗin.

Ta kare maganan cike da shagwaɓa tana tura baki,ita kanta Mami ajiyar zuciya ta sauke cike da jin daɗin amsa da tasamu a wajen Aishan tace"yauwa kinga yanzu abunda nakeso dake ki koma can ɓagaren ki ɗauko kayanki ki dawo nan da zama ko a ɗakin masu aikine zefi da ku zauna tare da ƙato daga ke sai shi.

Kuma zakina kama ma ma'aikin namu wasu ayyuka dan aiki yana neman yi mata yawa.

Gobe mai Gidan ze dawo daga tafiya inason ki shiga ki gyara masa ɗakinsa ki canza sabon zanin gado abunda ya kaiki kawai zakiyi ki fita bana son yawan kalle kalle na wuce ƙa'ida.

Sannan gyara ɗakin Fauza da wanke mata banɗaki sai wanke mata kaya duk wannan magana da take tanayin sane cike da izza tana zaune a inda take ko motsawa batayi ba,saima ƙafanta ɗaya data ɗaura saman ɗayan.

Ganin tayi shiru yasa Aisha ɗagowa ta kalle ta cikin sake yin ƙasa da kanta tace"Mami niɗin ba'a juyani cikin sauki sai abunda naga dama zuciyata ta aminta nake.

Batun share ɗakin mai Gidan zanyi,amma Mami idan har kina tsoron wani abu maiyasa ke ba zakiyi hakan da kanki ba,kiyifa hakuri idan magana ta taɓata miki rai.

Sannan bazan taɓa yima wannan wanki da gyara mata ɗaki da kika ce ba,dan itama macece wataran Aure zatayi idan tayi aure a irin haka itama  zata sa ƴan aiki ɗakin kwanan su suna gane musu sirrin su ne?

Sake baki Mami tayi tana kallon Aisha tare da mamaki karfin hali irin nata,dan ita ba taɓayi mata irin haka ba.

Sajida dake tsaya a wajen sai kumshe dariyar ta take gudun kar tayisa a bayyane ta shiga uku gun Mami da ƙanwar mijin nata dan Fauza ba kunyace da ita ba,idan ta tashi rashin kunyar ta hatta da Yayan nata ba ragamasa takeyi ba.

Suna nan tsaye a gun Ahmad ya dawo daga wajen aiki yashiga sashin Sajid basa nan shine yazo nan din da sallama yashigo Mami da Fauza basan wanda yafi ɗan uwan sa ba,gun nuna farin cikin shigowar sa nan din idan suka tuna a yanda yafita daga gidan ɗazu duk da ko a fuskane be nuna musu komai ba,da fara'a tare haba haba suka shiga amsa sallamar nasa.

Tunda yashigo idon sa kurr akan Aisha ko kiftawa babu itama din sai akayi sa'a shidin take kallo.

Kana ganin yanda suke kallon junan su cike da shauƙi harma sun mance da akwai wasu halitta a wajen bayan su ɗin.

Takowa yake a hankali a hankali harya iso gareta yakai hannu saman tattausan fuskarta kenan "Amadi me haka Mami ta faɗa a tsawace dan ita kanta batasan tayi hakan ba.

A tare suka janye daga kallon junan nasu ko wanne na kokarin basarwa,kallon ta yake cike cikin kamilaliyar fuskarsa ya ɗan ɓata fuska sai yace"Mami barka da yamma.

Ba karamin ƙoƙari tayi wajen tattara nutsuwarta dan ganin bata kofsa ba,ita ko Fauza tunda taga yanda suke kallon junan su ta fece dan bazata iya tsayawa ta kalli wannan kayan taƙaicin ba.

"Yauwa barka Amadi fatan ka dawo lafiya?"komai normal ya amsa mata idon sa nakan Aisha da taƙi tasake kallon sa,saide tanajin a jikin ta kaman idanunsa na kanta.

Sajida ta kalle sa cike da zolaya tace"irin wannan kallo haka Yah Ahmadi kamata kurage wa Yaranku su samu na kallo wataran.

Mami ta faki idon Ahmad ta harari Sajida dake kallon ta a fakaice dan ita Allah yana gani tafison Aisha da Ahmad din fiye Fauza data take kawar mijinta ma.

Ahmad ba kunya yaja Aisha suka fita daga falon sakin baki Mami tayi tana jinjina girman rashin kunyan Ahmad ɗin  shikuma yana sane da gayya yayi hakan.

A zafafi Mami ta koma kan Sajida tana surfa mata ruwan masifa ta inda ta shiga ba tanan take fita ba karshe tace"wallahi kin bani mamaki Sajida na dauka ko ba komai kemai tsayama Fauza ne kan abunda take so harsai inda karfin ki ya kare amma dake za hada kai a hana mata samun wannan farin cikin .

"Yi hakuri Mami aini bansan da alaqa dake tsakanin ta dashi ɗin bane"dallah rufamun baki kuma wallahi nasake jin yarinyar nan ta zauna wajenki kaman yanda naji ɗazu kemadin zamanki ya kare a gidan nan karki dauka zan daga miki ƙafane dan Abot da ke tsakanina da Mahaifiyarki wallahi sai in rufe idona naci miki mutumci dan farin cikin Fauza yafimun komai aduniyar nan.


ALLAH YASA MUDACE

Continue Reading

You'll Also Like

206K 14.7K 19
"YOU ARE MINE TO KEEP OR TO KILL" ~~~ Kiaan and Izna are like completely two different poles. They both belong to two different RIVAL FAMILIES. It's...
432K 24K 17
𝐒𝐡𝐢𝐯𝐚𝐧𝐲𝐚 𝐑𝐚𝐣𝐩𝐮𝐭 𝐱 𝐑𝐮𝐝𝐫𝐚𝐤𝐬𝐡 𝐑𝐚𝐣𝐩𝐮𝐭 ~By 𝐊𝐚𝐣𝐮ꨄ︎...
163K 12.9K 21
"Why the fuck you let him touch you!!!"he growled while punching the wall behind me 'I am so scared right now what if he hit me like my father did to...
3.5M 148K 61
The story of Abeer Singh Rathore and Chandni Sharma continue.............. when Destiny bond two strangers in holy bond accidentally ❣️ Cover credit...