WAZEER!

By REAL-SMASHER

3.2K 338 50

...Me zai sa mahaifi ya aure budurwar ɗansa? Son zuciya? Son kai? Kou kuma budurwar zuciya? #Follow this... More

THRILLER
Mysha!
Divorce
Force play
Dumb out
Hoor
Interpolated
Decision maker
Guilt-ridden
Camp
Wedding march
Vie
Overlook
Rivalrous
Envious
Power of love
Mission
Mislike
Affinity
Envious 2
Beseech
Inexplicable
Strangerlike
Safwah
Adviceful
Thought pattern
Proposalist
Her wish!
Wedding bell!
Break away!
Chapter 2:Thriller

New decision

82 10 0
By REAL-SMASHER

💠💠💠💠💠
©®AS-2023.


*Bᴀsᴇᴅ ᴏɴ ᴀ ᴛʀᴜᴇ sᴛᴏʀʏ*


                     *♡WAZEER¸.•💥*
                   (A Tᴡɪsᴛ Oғ Fᴀᴛᴇ)


Bʏ.
   *HAWWA__B__KUMO.*
       (Rᴇᴀʟ Sᴍᴀꜱʜᴇʀ).💕
*WATTPAD:REAL-SMASHER.*
*AREWABOOKS:REALSMASHER.*
••••••••••

*It's all about:#Love one another,#Twist,#Betrayal,#Friends,#Fate,#Romance,#Hated, & #Lost..*


                               04

#New decision

                   Zazzaro idanunta Hoor tayi tana dafe ƙirji tace "na shiga uku.. Hamood please don't do this to me.. Ka tsaya ka bani yarona" wani matsiyacin kallo ya sakar mata ya rufe motar ya tayar zai tafi,da gudu Hoor ta isa gefen da Abuu Turab yake yana kallonta idanunsa na ciccikowa da ƙwalla ya kasa magana,kana kallonsa za ka san ba ya son tafiya ko'ina tare da mahaifinsa,amma kuma bazai iya fitowa ya faɗa ba,tsoron yai magana yake a gaban Hamood,bai so yai masa faɗa yai masa irin ihun da yake yiwa Mimi,Hoor ta buɗe motar hawaye na zuba idonta tace "Hamood please ka tsaya ka bani yarona.. Ina za ka kaishi? I've my right over him,zan iya riƙeshi na bashi tarbiyya a matsayin mahaifiyarsa,kada kace za ka rabani da ɗana by force" ƙoƙarin jan motar ya dunga yi,ita kuma ta riƙe murfin motar tana son ɗaukan ɗanta,a zuciye yace "Hooriyah get out of my way,kada kija nabi ta kanki na wuce" cikin ihun itama tace "kabi ta kan nawa ka wuce Hamood,shi ne zan san ka tsaneni ba ka son sake ganina,ka kasheni kawai ka huta.. Ai babu me maka komai tunda ku kuke da garin Kano,ba taƙamarka kai jinin sarauta ba? Ka kasheni nace maka,amma wallahi babu inda za kaje min da yaro.. Saboda selfishness irin naka na rasa ƴata 6 days yau,sannan yanzu kazo za ka rabani da wanda nake gani naji sanyi.. Shin kai kaɗai ka rasa ƴarka ne? Ai nima ƴata ce kamar yanda take taka" yanda take kuka haka Abuu Turab yake kuka yana kallonta,a hankali cikin tsoro ya kalli Hamood yace "Dad ni a gurin Mimi zan zauna,ba zan bika ba ka ƙyaleni naje gurinta,she's crying because of me" gigitaccen tsawa Hamood yai masa cikin ihu yace "Wazeer! Keep ur mouth shut kafin na mammareka.. Baza ka zauna gurinta ba,yau ɗin nan za mu tafi ni da kai,bazan taɓa barinka a gurinta ba,muguwa ce ita,tana da son kanta,me kisan kai ce,mutane take kashewa,idan na barka a gurinta za ta kasheka kamar yanda ta kashe Lil Mysha.." Abuu Turab na kuka yace "Dad ba ta kashe mutane,ni na fi son Mimi,a gurinta zan zauna" cikin faɗa idanun Hamood sun rufe tsabar ɓacin rai ya fizgi motar,sauran kaɗan ya taka mata ƙafa da mota,Allah ya kawo Yaa Umar da ya fito parlour amsa waya,jiyo kamar hayaniya da ihunsu ne yasa ya fasa ɗaukan wayar,ƙwalawa su Yaa Abuye kira yayi yana cewa "ku fito ina ga rigima suke" da hanzarinsa kafin su fito tuni har ya rigasu isa waje,yanda yaga Hamood ya fizgi motar yasa da wani irin ƙarfi ya fizgo ƙanwarsa ta faɗa jikinsa,wani irin kuka me cin rai Hoor ta fashe da shi,tana ƙoƙarin ƙwacewa tabi motar Hamood da gudu,Yaa Abuye da suka fito gidan yai mata tsawa yana faɗin "what's happening? Meke damunki Hoor? Kukan me kike?" Cikin gushewar hankali tace "Yaa Abuye ya tafi min da ɗana,ya rabani da Abuu Turab ɗina" Yaa Abuye ya dunga kallonta yana faɗin "kamar yaya ya tafi da shi? Ina zai kaishi?" Yaa Umar yace "Allah dai ya rufa asiri na fito,amma da tuni ya bigeta da mota" Yaa Abuye yace "hauka yake zai bigeta? Kou shaye² ya fara?" Yaa Umar ya taɓe baki yace "tou Yaya wallahi nima dai na kasa gane komai,kou maganar da Abbansa yai masa ne yasa yazo ya ɗauke shi?" Yaa Abuye yana kallon can titi da zuwa lokacin babu alamar motar Hamood ya ɓace tuni yace "Umar kamota ku shigo cikin gida" da sauri ya juya zuwa ciki Yaa Umar na riƙe da ita suka bi bayansa,banda kuka babu Hoor take tana waige² kou za taga Hamood ya dawo mata da ɗanta,amma har suka shiga gidan kou ƙurarsa basu gani ba bare shi kou me kama da shi,suna shigowa cikin parlour Mama da Yaa Mansoor suka bisu da kallo,da gudu Hoor ta ƙwace jikinta ta tafi ta faɗa jikin Mama ta sake rushewa da sabon kuka,hankalin Mama a tashe tana kallon Yaa Abuye tace "tou wai dama zuwan nasa na ya karɓe ɗansa ne? Ba tafiya yazo yai dasu kamar yanda kace Abban nasa ya ce muku ba?" Yaa Abuye yace "tou nima dai Mama na yi zaton haka,amma ban san me haka yake nufi ba kuma" kamar gidan da akai mutuwa haka duka sukai shiru kowa da tunanin da yake,sai kuma kukan Hoor da ya cika gurin,Yaa Abuye yana girgiza kanshi yace "Mama ina ganin mu bar maganar nan iya mu kaɗai,mu bashi lokaci muga kou zai dawo da kansa ya nemi ta dawo,i think yana kan dokin fushi yanzu,bazai saurari kowa ba tunda har ya kasa sauraron iyayensa.. Hoor kiyi haƙuri,in sha Allah zai dawo miki da ɗanki,ki bar kukan haka nan kada damuwa yasa wani ciwon ya kamaki" Mama na sauke ajiyar zuciya tace "maganarka haka ne Abuye.. Mu bashi lokacin,Allah ya ganar da shi gaskiya" Yaa Mansoor da ya kasa cewa komai yace "ameen.." Yaa Umar dai ba haka yaso ba,dan shi kaɗai yaga abunda ya gani sanda ya fita,ba don Allah ya kaishi ba da yanzu wani maganar ake yifa ba wannan ba,amma ganin Mama tace a bashi lokaci yasa kawai yai shiru,tunda shi ne ƙarami a ciki bazai so ya kawo nashi maganar ba,kou kiran can gidan babu wanda Mama tasa yayi,duka sukai shiru da niyyar su zuba ido suga kou wani zai biyo ba'asi idan an kwana biyu.

*HAMOOD*

       Yanda ya fizgi motar ya matuƙar tadawa Abuu Turab hankali,a tsorace ya runtse idanunsa numfashinsa na fita heavily,can bayan wani lokaci ya fashe da azababben kuka me ƙarfi,har shiɗewa numfashinsa yake yana dawowa,bakinsa na ɓari muryarsa na trembling yana kiran sunan "Mi.. Mim.. Miiiii!" Dole ka kalleshi ya baka tausayi duk taurin zuciyarka,Hamood da zuciyarsa ke wani tuƙuƙi,yana barin ƙofar gidan ya ɗaga kanshi ya kalli mirror,yana hango yanda Yaa Umar ya fizgo Hoor ya sauke ajiyar zuciya tare da ƙarawa motarshi wuta ya bar link ɗin,dama bai da niyyar yai mata komai,just ya tsoratar da ita yasa taji shakkarsa da shayin kuma bin hanyarsa. Daga Jambulo kou gidansu bai nufa ba saboda yanda ranshi yake ɓace,yawo yai tayi a titi daga nan zuwa can ya rasa takamaiman abun yi,yana jin yanda ɗansa yake kuka yana kiran sunan Miminsa amma bai kulashi ba,duk yanda yake jin zai iya yi masa shiru har zuwa sanda zai gaji yai shiru,lokacin da kukansa ya dameshi dan kansa yai parking gefen titi,a hankali ya juyo yana kallonsa idanusa a rine da ɓacin rai yace "come my dear" ya buɗe masa hannu,girgiza masa kai Abuu Turab yayi da muryar kuka yana komawa cikin kujerar motar yace "ni.. Ni.. Gurin Mi.. Mim.. Miiiii na zan.. Jeee" yai maganar a kakkatse har sannan numfashi ya ƙi dai²ta,Hamood ya dunga kallonsa for about 2 minutes ya kasa cewa komai,can ya kauda kanshi yana sauke numfashi da calming kanshi,a hankali ya juyo ya tsare ɗan nasa da idanu yace "Wazeer!" Kasa amsawa Abuu Turab yayi saboda kuka,Hamood yace "ka fi son Mimi akan Dad?" Saurin gyaɗa kanshi Abuu Turab yayi,Hamood ya dunga kallonsa kafin ya gyaɗa kansa shima,yana sauke wani numfashin ɓacin rai yace "ka fi son zama da ita akan ni?" Nan ma ya sake gyaɗa masa kai da sauri,Hamood yai murmushin takaici kafin ya ɗauke kanshi ya tada motar suka ci gaba da zagaye gari,zuciyarshi na saƙa masa abubuwa da yawa,akan ya bar ɗanshi hannun Hoor gara koma meye ya aikata,sallah kawai yake iya tsaiwa yayi sai abincin da ya siya masa,dake ya galabaita saboda kuka bai iya yai musu ba yaci,yana gamawa babu ɓata lokaci ya fara hamma,Hamood bai nufo gida ba sai dare lokacin da ya tabbatar bacci me nauyi ya ɗaukeshi,a hankali yana kallon yanda yake sauke numfashi da ajiyar zuciya a bacci yace "let's see idan na bar ƙasar da kai waye zai kirani yace sai na dawo da kai.. I promise u that baza ka sake ganin kowa ba,ur Mom and kowa ma,sai na tabbatar na cire maka tunanin komai daga ranka,sai nai wining zuciyarka,sai na sa ka manta da kowa,except ni mahaifinka.." Daga haka ya tada motar ya nufi Tudun wuzirci,Hamood na yin parking ya sauko tare da zagayawa ya buɗe gefen da yake ya ɗaukoshi yasa a kafaɗarsa,abunka da farin mutum tsabar kukan da yayi yau idanunsa sun kumbura,haka ma fuskarsa tai jaa,banda sauke ajiyar zuciya babu abunda yake akai²,kai tsaye cikin gida ya wuce da shi,ya yi sa'a yauma Abba ba ya zaure,da alama ya fita babu jimawa,sai mutanenshi kawai suna ta hira,part ɗinsa Hamood ya wuce ya buɗe ya shiga,a parlour bayan ya rufe ƙofar da key ya kwantar da Abuu Turab ya nufi hanyar bedroom ɗin ɗan nasa,kayanshi ya shiga haɗawa cikin luggage da sauri²,yana yi yana kallon agogon dake ɗaure wrist ɗinsa,yana gama packing up kayan ya tashi ya fita da su parlour,sannan ya koma master bedroom ɗinsa yai wanka ya shirya cikin farin long sleeve da black trouser,kou da ya fito yaga har sannan yana bacci,a hankali ya ƙarasa ya ɗaukeshi,ɗayan hannunshi kuma luggage ɗin kayansa,ya tsaya bakin ƙofa ya rufe gidan then ya nufi ɓangaren Daada,dai² zai shiga ɓangaren ya haɗu da Salisu,ya kalleshi a hankali yana ɗan tsayawa,Salisu ya ɗan rusuna yana faɗin "barka da fitowa ranka shi daɗe,kawo jakar na riƙe maka" Hamood na kallonsa fuskarsa ɗaure yace "yawwa Salisu,Isiyaku fa?" Salisu yace "yana waje ranka shi daɗe,a kira maka shi ne?" Hamood ya ajiye luggage ɗin hannunsa yace "no! Karɓi Wazeer ka kai masa shi,kace ya jirani ina nan fitowa yanzu" da sauri Salisu ya karɓi Abuu Turab da Hamood yake miƙa masa,yace "ranka shi daɗe kawo akwatin" Hamood yace "no jeka kawai,bari na shiga gurin Daada na fito" Salisu yace "tou ranka shi daɗe,a fito lafiya" daga haka ya tafi da Abuu Turab dake ta bacci,a gaggauce Hamood ya shiga da sallama,Daada dake tare da hadimanta suka amsa suna yi masa barka da shigowa then suka tashi suka basu guri,ya ƙarasa ya zauna fuskarshi babu walwala sosai suka gaisa,a hankali yana kallon Daada yace "Daada i'm leaving now" Daada ta ɗago tana kallonsa tace "zuwa ina?" Yace "zan koma America" kallonsa ta dunga yi kamar bata gane me yake cewa ba kafin tace "toh ka yima Abbanku sallama?" Yace "a'a" tace "toh sai ka jira har ya dawo ai ba nisa yayi ba" girgiza kanshi yayi yace "zan kirashi in sha Allah,ai na ga baya nan kuma few minutes ya rage jirginmu ya ɗaga" Daada tana gyaɗa kanta tace "toh shi kenan.. Allah ya tsare ya saukeku lafiya" ya amsa kafin ya tashi yana sake kallon agogon dake ɗaure wrist ɗinsa,ya ƙarasa gabanta yace "na barku lafiya" ta amsa tana dafa kanshi tace "Allah yayi muku albarka" ya amsa tare da ajiye mata kuɗi masu ɗan dama sannan ya miƙe ya nufi ƙofa cikin ɗan sauri,Daada ta bishi da addu'ah tana cewa "idan ka sauka ka kiramu kaji kou?" Yace "in sha Allah" daga haka ya fice ya bar gidan. A ƙofar gida ya samu Isiyaku da Salisu tsaye suna hira,ganinsa yasa da sauri Isiyaku ya taho ya karɓi akwatin hannunsa ya koma ya buɗe booth ya saka sannan ya buɗe masa motar,dai² lokacin Hamood ya karɓi Abuu Turab daga hannun Salisu yana faɗin "thanks" sannan ya shiga mota,sai da ya sallami Salisu sannan Isiyaku ya rufe,ya koma ya shiga mazauninsa ya tada motar yana tambayar Hamood dake rungume da ɗansa yace "yallaɓai ina muka nufa?" Hamood dake ta kallon ɗansa yace "take us to airport" Isiyaku ya amsa ya tada mota suka ɗauki hanya.

*HOORIYAH*

        Banda Mama da tai magana ta tausheta da su Yaa Mansoor,da babu abunda zai hana bata rufe kanta tabi Hamood ta karɓo ɗanta ba,tou kawai Mama da su Yaa Abuye sun yi magana,ita kuka ta san darajar iyayenta shi yasa ta bar zancen,amma haka kawai gabanta ke ta faɗuwa tunda ya tafi da shi,addu'ah take Allah yasa ba wani abu ne zai faru ba,Allah yasa ba wai Hamood yana nufin ya rabata da ɗanta ba kenan,gabanta ne ya kuma faɗuwa a fili tace "idan ya tafi dashi kuma fa? Idan ya bar ƙasar da shi fa?" Wata zuciyar tace "haka ma bazai taɓa faruwa ba,Abba baza su barshi ya tafi min da yarona ko'ina ba.." Wannan tunanin yasa tai believing kawai babu inda Hamood ya isa ya tafi da Abuu Turab,yinin ranar haka ta ƙarasa yinshi sukuku,kamar wata mara aikin yi sai na tunani,kou abincin kirki ta kasa ci saboda damuwar data sawa ranta,fatan da take kawai ace Hamood bai kai mata yaro ko'ina ba ya barshi gurin Daada,ta san na kwana biyu Daada baza ta jurewa zama da shi ba saboda rashin sakewar da zai yi,za tasa a kirata kou da bata koma gidan matsayin matar Hamood ba,za tace tazo ta ɗauki ɗanta,a lokacin shi kuma ya bar ƙasar,cikin ruwan sanyi ɗanta zai dawo gareta. Wannan tunanin shi ne yasa ta ɗan sakko har ta dawo cikin hayyacinta,ta sakankance akan faruwar al'amarin cikin ɗan taƙaitaccen lokaci.

*HAMOOD*

      Suna isowa Malam Aminu Kano international airport ya sauka motar ɗauke da Wazeer a shoulder ɗinsa,luggage ɗinsa da Isiyaku ya ciro a booth ya karɓa,yana kallon Isiyaku yace "za ka iya komawa Isiyaku na gode" Isiyaku yace "tou ranka shi daɗe Allah ya tsare ya saukeku lafiya" Hamood ya amsa yana ciro kuɗi aljihunsa ya bashi,Isiyaku ya karɓa yana tai masa godiya tare da addu'o'i kafin ya juya da motar gida,agent ɗin da yai magana da shi ɗazu da safe ya fara kira suka yi magana,yana katse kiran ya kashe wayarshi kafin ya bar gurin yana tafiya da ɗan sauri,a ciki inda sukai zai gashi ya tsaya ya karɓi boarding pass ɗin Wazeer da tickets wanda kafin ya wuce,a mugun ƙagauce yake yayi ya bar Nigeria kafin a samu matsala,dan yanda yake ji yau dole ya bar ƙasar nan da ɗansa,raba Hooriyah da Wazeer shi ne abunda ya rage wanda zai mata ciwo sosai sama da komai,yana so ta ɗanɗana zafin rashin abunda kake so a tare da kai,bazai yiwu tai silar da ya rasa ƴarshi kuma tai tunanin zai bar mata Wazeer a hannunta ba,duk da dai ya saketa ba kuma don ba ya sonta ba,sai don ya koya mata darasin rayuwa,ganin da sauran lokaci kafin jirginsu ya tashi ya tsaya nan toilet ɗin lounge ya kai Wazeer yai fitsari,idanunsa cike da bacci ba wai dan yana magagi ba,Hamood ya gyara masa wandon sannan ya ɗaukeshi ya fito ya zauna yana ta kallon lokaci,guraren 9pm bayan ya gama abunda zai suka shige,jirginsu ya ɗaga daga Nigeria zuwa ƙasar Amurka. Da yake dare ne tunda Hamood ya zauna seat ɗinsa ya kwantar da Wazeer jikinsa,a hankali ya zare suite ɗinsa ya rufeshi,haka kawai ya dunga kallon innocent baby face ɗin ɗansa fuskarsa da murmushin nasara,babu ɓata lokaci jirginsu ya shiga keta giragizai a sararin samaniya,ya ɗaukesu awanni masu dama kafin jirginsu ya sauka Lax (Los Angeles International Airport),hayaniyar passengers da suke ɗaukan kayansu shi ne ya tada Wazeer,a hankali ya shiga buɗe idanunsa masu cike da bacci,haka nan ya shiga bin inda yake da mutanen gurin da kallo,a hankali ya ɗaga kanshi ya kalli Hamood dake kallonsa,fuskarshi da murmushi akai yace "mu tafi gida?" A hankali ya gyaɗa kanshi kafin ya buɗe baki yace "gurin Mimi?" Hamood ya kalli Wazeer kawai,ba tare da ya ce masa komai ba ya saukeshi sannan ya tashi ya ciro luggage na kayansa,a hankali ya kama hannunshi suka bi sahun masu fita suna sauka,Wazeer sai wara idanunsa yake,mamakin ganinsu suna sauka daga stairs na jirgi yasa ya kalli Hamood,da excited voice yace "Dad jirgi muka shiga?" Hamood yai masa murmushi tare da gyaɗa kanshi yace "yes my dear" Wazeer ya juya ya kalli mutane da inda suke cikin LAX yace "Dad where are we now?" Hamood yace "nan muna Los Angeles" Wazeer yai shiru kamar yana tunani,sanda ya fara ganin fararen fata sosai ma'ana turawa a hankali yace "Dad can i ask u?" Hamood duk ya cika da mamakin yanda yake magana da shi yau yace "yes my love,what's it?" A hankali Wazeer dake wara idanuwa yace "ina ne Los Angeles? Me muka zo yi? Ina Mimi? Me yasa bamu zo da ita ba?" Shiru Hamood yai yana kallonsa lokaci ɗaya yace "Wazeer! Ka bari muje gida,ok?" A hankali Wazeer ya gyaɗa kanshi yace "tou!" Daga haka yai shiru,suna fitowa airport Hamood ya tare musu cab ya sanar da mutumin Ave ɗin da zai kaisu can guraren West Hollywood,sanda ya fara shigar da Wazeer sannan ya shiga ya zauna,me cab yaja suka tafi,a hanya Wazeer yai shiru yana kalle²,musamman da yaga gine² ba irin wanda yake gani a Nigeria ba,sai dai bai ce komai ba har suka isa street da gidansu yake,baturen me motar daya ɗaukosu yai parking,Hamood ya buɗe motar ya sauka,yana kallon Wazeer ya miƙa masa hannu yana cewa "get down my dear" saukowa yayi tare da kama hannunshi,me cab ya sauko musu da luggage ɗinsu,Hamood ya bashi kuɗinshi sannan suka wuce apartment ɗinsu,bin Dad ɗinsa kawai Wazeer yake yana kallon gurin da bai sani ba,duk sai yaji ya kasa sakewa da kowa da komai,tunda suka zo baiga wanda ya sani ba sai Dad ɗinsa,shi yasa yake biye da shi sau da ƙafa,key Hamood ya ciro aljihunsa yasa ya buɗe musu ƙofa suka shiga,Wazeer ya karanto addu'ar shiga gida,yanayin tsarin gine²n arean sosai yasa shi cikin tunani,irin wooden gidaje da yake gani a films ɗin turawa ne,apartment ne that contains 3 bedroom,living room sai kitchen,dai² zaman mutum ɗaya da iyalinsa ko'ina a gyare tas²,a hankali ya ɗaga kai yana kallon Dad,kamar wanda maganar yake cinsa yace "Dad wannan gidanmu ne?" Hamood dake ƙoƙarin zaunawa yana fito da sim card da zai saka a wayarshi yace "yes my love" Wazeer ya zauna kusa da shi yana kallon madaidaicin parlonsu da babu shirgi kuma a tsaftace yace "a nan za mu zauna?" Hamood yace "yes my love" a hankali Wazeer ya sake cewa "Mimi za tazo itama?" Strictly Hamood yace "no my dear.. Just me and u za mu zauna nan,zan kaika school kayi karatu ka zama babban business Tycoon,kana so kou?" Shiru yai yana kallon Dad ɗinsa ya kasa cewa komai,can a hankali yace "Dad nan wane ƙasar ne?" Hamood da ya gama saka sim ya kunna wayar yace "America!" Wazeer yace "gurin aikinka muka zo?" Hamood yai murmushi yace "gida muka zo nan,gurin aikina yana can wani guri.. Muje kai wanka muyi sallah,sai mu fita mu siyo abinci kou?" A hankali Wazeer ya gyaɗa kanshi yace "ok!" Ɗaya daga cikin bedroom biyu da bai amfani da su amma komai akwai a gidan suka shiga,Hamood ya ƙarasa wardrobe ya buɗe ya ɗauki towel ya bawa Wazeer yace "go and take shower,nima zanje nayo sai muyi sallah" a hankali ya gyaɗa kanshi yace "da kaina zanyi?" Hamood yace "yes! Do it urself" ɗan murmushi Wazeer yayi yace "Mimi bata barin nayi da kaina" Hamood yace "ok! Muje nayi maka" da sauri yace "no Dad! I will do it myself" Hamood yace "ok! Thought baza ka iya ba" ya girgiza kanshi yace "zanyi.. Ai ita Mimi ba ta barin nayi" Hamood yace "ok! Maza je kayi,zan ajiye maka kayan da za ka sa" cire kayanshi yayi ya ɗaura towel kamar yanda Hoor ke masa a gida,sannan ya tafi ya buɗe toilet,Hamood yace "don't forget to brush up ur teeth" daga haka ya buɗe luggage ya shiga fito da kayan dake ciki ya shiryasu a cikin wardrobe,yana gamawa ya fita ya tafi nashi ɗakin,wanka ya fara yi sannan ya ɗauro alwala ya fito,a gurguje ya shirya cikin t-shirt da trouser black,ka ganshi kyakkyawan bafulatani dake jin izzar sarauta da jin daɗi,kamar ba ɗan Nigeria ba,yana fitowa ya nufo bedroom ɗin Wazeer ya buɗe yana faɗin "Wazeer ka gama?" Wayam yaga ɗakin babu shi,da sauri ya nufo parlour yana kiranshi,Wazeer dake zaune parlour yace "i'm here Dad" wani ajiyar zuciya Hamood ya sauke da ya ganshi,a hankali yace "taso muyi sallah muje eatry" tashi yayi yana sanye da short trouser da t-shirt me bala'in kyau,gashinshi duk yai curly kamar yaron turawa,abunka da jinin shuwa Arab,pray mat Hamood ya ɗauko ya shimfiɗa musu,shi ya jasu sukai sallolin da ake binsu sannan suka fita gidan,nearest eatry suka je suka ci abinci,a hanya suka shiga wani super market Hamood yai musu siyayya,ya sissiya masa chocolates sannan suka fito,grocery dake kusa suka sake shiga ya siya musu fruits sannan daga nan suka hau cab suka tafi gida.

*NIGERIA..*

       A daren bayan Hamood ya tafi,Abba Waziri ya dawo daga gidan Sarki,duka akan maganar sakin da Hamood yaiwa Hoor ne,Abban yaje suyi maganar da ƴan uwansa Sarki Abduljalal da su Galadima,bayan ya sanar da su hukuncin da ya yanke na dawo da Hoor ɗin da yace Hamood yayi,amma ya ga ya nuna baiso,shi ne dalilin da yasa yazo suyi shawara,Sarki Abduljalal yace "babu damuwa mu bashi lokaci,yanzu ya hau dokin fushi da zuciya,in sha Allah idan ya sakko sai ayi maganar,amma yanzu Waziri kayi shiru da maganar,kada ma sake cewa kowa komai" duka su Galadima suma abunda suka ce kenan,Abba Waziri yace "shi kenan" haka ya dawo gida har ranshi baiso ba da su Mai martaba suka ce a bari,yaso su goya masa baya a maidata kawai by force,saboda su suka haifi Hamood ba shi ya haifesu ba,sai dai me? Yana dawowa gida Daada take sanar masa batun tafiyar Hamood a daren,Abba ya dunga kallonta ranshi a ɓace yace "wato yaron nan so yake ya nunama duniya bamu isa da shi ba,shi yasa zai kama hanya ya bar ƙasa ana tsakiyar magana? Me yake nufi? Bazai ji maganar mu ba kenan? Bazai bi abunda muke so ba?" Daada tace "tou nima dai lamarin nasa ya fara bani tsoro,na so ya kiraka kou da bai jiraka ba,amma sai cewa yayi sun kirashi ne daga can,kuma dama basu bashi hutu me tsayi ba" Abba ya dunga gyaɗa kanshi babu ƙaƙƙautawa,yace "ya kyauta.. Yaje Allah ya bada sa'a,tunda haka ya zaɓa na zare hannuna a lamarinsa,suma su Yayan zanje na sanar musu halin da ake ciki.." Daga haka ya tashi ya wuce part ɗinsa.

*HOORIYAH*

      Kamar wasa tunda Hamood ya ɗauke Wazeer ya tafi,kou a waya bata sake jin wani ya yi magana da ita ba,al'amarin sosai ya ɗaure mata kai,tun tana lissafi da saka rai Daada za ta kirata tace mata tazo,kou ta aiko a dawo mata da Wazeer,sai taji shiru babu wanda ya tuntuɓeta,shirun nan kuwa sosai yasa ta shiga damuwa,kullum ba ta da sukuni,damuwarta ta san halin da ɗanta yake ciki,idan ta zauna bata da aiki sai dai taita kallon wayarta tana jiran kiran Daada kou wani daga family'n Hamood,Mama data karanceta tas ta ga yanda take cikin damuwa,tun tana mata shiru har ta dawo tana bata haƙuri da tausarta,wasa² haka kwanaki suka shiga turawa. Ita kanta Mama ta yi mamakin da taji shiru daga gurinsu Abba Waziri,jin babu wani labari yasa ta kira Yaa Abuye tace masa ya kamata a san abun yi akan lamarin Hoor,tunda har Allah ya sa Hamood ya riga ya bata takardarta kuma ya karɓe ɗansa,abunda yake nufi sun rabu shi da ita,da Hoor taita zaman haka nan babu tsiyar da take a gida,sai zaman banza da tunane² marasa amfani da fa'ida,da su zuba mata ido suna kallonta a wannan halin,ƙarshe wani abu yazo ya faru mara daɗi,abunda take nufi shi ne a nemar mata Admission ta koma makaranta,yin hakan in sha Allah kou da bai cireta daga damuwar da take ciki ba zai ragu,Yaa Abuye yai na'am yace "in sha Allah Mama,yanzu ɗalibai suna first semester,idan lokacin sake ɗaukan sababbi yayi sai a nemar mata" Mama tace "tou shi kenan,Allah ya taimaka yayi jagora" Yaa Abuye ya amsa da "ameen.."

          #Afwaan! Yau na ɗan shiga uzuri shi yasa banyi muku post da wuri ba,ai min haƙuri please...

*AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE*

   _Jama'a kada ku bari wannan garabasa ta wuce ku,muna da nau'in magungunan gargajiya masu kyau da inganci_
   _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176  domin karin bayani,  maganin ya samu lambar yabo saboda inganci da sahihancinsa,  yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai-dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka   fara amfani da   maganin zaki ga sauyi,  domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari  2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu 'batawa kai lokaci🙏🏻_

*Infection*
    _Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye!  infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu'amula mussaman ga ma'aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za'a dace *SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI💯*_

    _Muna sayar da supplement gangariya  irin wadanda ba su da matsala sai da su gyara garkuwar jiki da inganta lafiya, muna bayar da sari duk wani supplement muna da shi, kuma muna sayar da daya muna bada sari akan farashi mai sauki, muna tura kayanmu ko wane gari domin neman karin bayani a tuntunbi wannan lambobinmu dake kasa._
*08089965176*
*07084653262*

#Follow
#Comment
#Vote
#Share fisabilillah!
#ASLI-SMASHER.

Continue Reading

You'll Also Like

361K 22.4K 117
Unbreakable Bonds A boy who was least interested in love and a girl who was broken because of her mother and sister's hatred. What will happen when...
69.6K 11.3K 74
~BOOK 3 IN THE DESIRES SERIES~ STARTED. ON 20-JANUARY-2021 FINISHED. ON 15-OCTOBER-2021 #1 in mothers. On. 7-08-2021 #1 in introvert...
1.4K 4 19
You are a boy that gets betrayed by your team. Cause You can't use your sacred gear and they try to kill you. But you get reincarnated as a devil. To...
BETRAYAL By Uniy

Mystery / Thriller

6.2K 264 28
Have you ever had someone you loved more than anything betray you? Inseparable, triplets from different mothers, that's what they were. They grew up...