ALMAJIRA ✔

By DielaIbrahim

1.2K 70 5

Story of a girl living a miserable life as the agony of her life is too painful for them to survive, She find... More

Prologue
1
02
03
04
05
06
07
08
09
10
11
12
13
14
15
16
17
AL'ADARMU
19
20
SOFIA

18

34 2 0
By DielaIbrahim

ALMAJIRA Sabon Salo

PAID BOOK

*NOBLE WRITERS ASSOCIATIONS✍🏼*

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
'''Gidan karamci, rubutu don ci gaban al'umma, mu gudu tare mu tsira tare, alƙalaminmu ƴancinmu.'''
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

*https://www.facebook.com/106494781436168/*


ALMAJIRA
PAGE 18

______________________________________

Yayi relaxing a kan kujeran dakalin ya zauna very confortable ya mikar da kafafuwan sa, sannan ya nannaɗe hannayen sa akan kirjin sa ya lumshe idanuwan sa yana tunani.

Ina gefe duk ina kallon sa sai naga ya birge ni karo na farko kenan a rayuwa ta da naga wani ɗa namiji ya birge ni, na zuba ma kwantaccen sajen sa ido da lallausan bakin gashin kan sa tamkar na lararabawa tsabar laushi da taushi da kyalli da komai ma, kamannin Anna ne sak a fuskar sa, ban san lokacin da nace," Amma kasan kuna yanayi da Anna ko?

Ko gizau kuma bai ko buɗe ido ba balle ya kalle ni, idanuwan sa suna a rufe sai naji sautin murmushin shi mai sanyaya zuciyar mai sauraro, sai Ya ce,"Na sani khadija, amma kin san wani lokacin dama kana haɗuwa da mai kama da kai kuma sai kiga ma babu abin da kuka haɗa da shi" ya faɗa daidai lokacin yana kokarin tashi don zuwa yin sallar magriba, ina kallon sa yayi alwala a famfo ya dawo waje na ya ce,"Khadija, bari naje masallaci na dawo, ke ma ki tashi kiyi naki sallan"

Na gyaɗa kai nima na tashi na nufi wajan fanfo, na gama alwala na dawo wajan na shimfiɗa kallabi na, na fara sallah.

Ina zaune a wajan har ya dawo ya iske ni ina addu'a zama yayi yana mai ɗaga hannu shima ina tofawa shima ya tofa yana cewa,"Amin ya rabbi Allah ya karɓa addu'a"

Murmushi nayi kawai na ɗan kalle shi a sace...Kamar almara sai naji ya ce,"Kallon ya isa haka *ƴar buzuwa na* "

Ya faɗi sunan da ya sani saurin kallon sa da mamaki a fuska ta, sai ya tuna min da mahaifiya ta, duk dama da wasa ya faɗi hakan amma sai naji wani iri a zuciya ta ina tunanin ko wani hali take yanzu oho sai Allah, wata kil ma ta rasu tun da jima wa...Hawaye ne suka sauko ɗigo ɗaya na sa hannu na share gefen kumatu na.

Na buɗe ido sai na sauke su tangaran a fuskar sa babu yabo babu fallasa yana kallo na, idanuwa na suna kasa sai naji tattausan hannayen sa suna share min hawayen fuska ta.

"Ki dena kuka kinji, ba kina da Anna ba?

Na gyada kai kamar wata ƴar yarinya hawayen na kara sauka a idanuwa na.

Ya sake ya ce,"Ba kuma kina da Baffah ba?

Na sake gyaɗa kai na sa hannu ina share guntun hawayen ina sauraran sa.

Ya sake sunkuyo wa daf da fuska ta idanuwa na suna kallon idanuwan sa, ina jin numfashin sa na fita ta siririn hancin sa, Ya ce,"Sai wa kuma?

A daburce na ce, "Sai Sofia"

Ya sake marairaice fuska Ya ce," Sai wa kuma"

Wannan karan shiru nayi dukkan jiki na kyarma ya ɗauka, ni kam ya fara bani tsoro, miye kuma haka yake yi?

Ni kam ta shi nayi da sauri zan bar wajan sai naji ya rike min hannu ya taso ya dawo ya tsaya in da nake, na runtse ido na shi kuma yana kallon fuska ta,

Ya ce,"Kin fara tsoro na ko?

Da sauri na buɗe ido na sauke su akan na sa kamar zan yi kuka, ya karanci zuciya ta, na daure na ce,"Don Allah Yaya..........ban kai ga karasa wa ba sai naji hannun sa akan baki na yana girgiza kai yana cewa,"Zan dena kinji" 
Na ɗaga kai na kalle sa sai naga yana ɓalle boturan hannun rigan sa shirt ne dama da wandon jeans, ya sanya tun da safe da yayi wanka....Ina kallon nasa sai naji ya kuma cewa,"Amma sai dai idan zaki raka ni wani waje yanzun nan"

Na ce,"Ina kuma? na faɗa fuska ta cike da damuwa kuka ne kaɗai ya rage nayi saboda idanuwa na sun riga da sun yi ja tsabar na kagu na koma wajan su Anna.

Na wai ga na ce,"Ba su Anna suna ciki ba, ina zan raka ka dare fa yayi"

Na ɗaga hankali ne kasancewar nasani tabbas na sake da shi duk da bamu wani jima ba, amma na rasa ya a kayi na saba da shi a cikin kwanaki kalilan, ban fa san ko shi waye ba, amma dai zan iya bada shedar mutumin kirki ne tun da ban taɓa ganin sa yana chutar da wani ba.....ina tsaka da wannan tunanin naji Ya ce

"Idan kin gama tunanin ki zo muje dai" ya faɗa yayi gaba abin sa, sai na tsinci kai na da bin bayan sa har muka isa in da motar sa take, ya buɗe min na shiga ya zagaya shima ya shiga.....Zuciya ta na ta min kashedi idan ya min wani abu fa, zuciyar tawa fal da tsoro hakan ya sa nayi shiru ko kyakkyawan zama ban yi ba a kujerar.

Muna ta tafiya babu mai yiwa kowa magana, a daidai wajan masu sai da fruit a bakin hanya irin fresh ɗin nan, ma su kyau, muka tsaya ya fita ya siyo Tuffah, Abarba, Ayaba, Lemo da sauran kayan marmari, ya jido su da yawa kamar hauka, nayi niyan zuwa na taimaka masa sai naji yace min,"No need ke sarauniya ce ƴar buzuwa na" ya faɗa da zolaya ya cigaba da kwaso kayan har suka gama ya tuka motar....Ni dai ban kula sa ba ina zaune kamar gun ki.

Muka sake zuwa wani Super market nan ma yace min na zauna kawai ya kunna min karatun alkur'ani, ina ta saurara har na fara gyangyaɗi ma cen naji ana ta loda kaya a motar na buɗe ido sai naga yana shigowa yana ce musu sai da safe, ban ce mishi kala ba, Amma na lura da yanda ake ta faman kiran wayan sa an masa miss call ya kai sau goma ko ma fiye da haka kuma bai ɗaga kiran ba...

Muka koma asibiti na fito ma ban tsaya taya sa kwashe kayan ba saboda ban san ko na su waye bane.

Ahmad ya gane Khadija na tsoron sa yanzu tun da har taki yi masa magana yana kallon ta ta wuce ta shiga ɗakin da aka kwantar da Anna, rabuwa yayi da ita kuma dama bai isa ya sanya ta kwashe kayan nan ba saboda suna da nauyi...dole ta sa ya nemo wasu sojoji ya nuna musu ɗakin sukai ta shigar da kayan.

Shi kuma yana tsaye jikin motar sa, yana kokarin ɗaga kira an sake kira kenan a karo sau ba a dadi.

*************
Ina shiga na iske Anna zaune tana hira da Baffah, Sofia kuma na zaune daram a cinyar Anna tayi bacci.

Murmushi nayi na faɗa jikin Anna da sauri na rungume ta ina cewa "Lahhh Alhamdulillahiii Anna na ta samu lafiya"

Baffah ya ce,"Ina kika shiga ne tun ɗazu Hadiza? abin ka da mahaifi kenan dole ya tambaya ina ta shiga

Na ce,"Baffah ina waje ni da Yaya Ahmad, na jira shi yaje masallaci ya dawo shi ne na shigo yanzu"

"Ohhhooo, ina yake?

Baffah ya tambaya a daidai lokacin da naga sojoji suna ta shigowa da kaya niki niki a hannun su, manya manyan ledoji bakake, zasu kai goma ko ma fiye da haka, na yamutsa baki cikin rai na ina cewa ko miye waɗannan kuma ohoooo

Na ce wa Baffah ,"Yana waje na bar sa" na faɗa ina wai gawa kofar shigowa in ga ko ya shigo, ai kuwa ya shigo yana tsaye yana kare min kallo hannyen sa na saman kirjin sa ya nannaɗe su.

Da kyar ya iya karasowa in da muke, babu kuzari a tattare da shi, fuskar sa babu annuri ya karaso yana cewa ,"Baffah ga komai da komai da zaku bukata, ga kuma kuɗi" ya mika wa Baffah bandir ɗin ƴan dubu ɗaya, yana cewa "Dubu ɗari uku ne Baffah duk abin da kuke bukata ku cire a ciki kuyi anfani da shi, don Allah bana son baran nan"

Baffah kamar yana kallon Ahmad abin ya ba shi mamaki, Ya ce ,"Ɗan nan mun gode da ɗawainiya sosai Allah yayi ma rayuwar ka Albarka, amma kuɗin nan sun yi yawa ka rage su dan Allah"

Anna ta ce,"Yaro mun gode sosai wannan ma da kai mana ya isa wallahi muna godiya, ka bar kuɗin ka kaji, kar ɗawainiyar yayi yawa"

Ya sunkuya har kasa, muryar sa kasa kasa, fuskar sa dai babu wani fara'a Ya ce," Baffah kuna mai da hannun kyau ta baya, Don Allah kuyi hakuri , kuma kun sani babu kyau, kuɗin nan fa zasu muku anfani, ba wai na rai na sana'ar baran dankuke zuwa bane, Anna kawai ina son ku dena zuwa ne kuma ga shi baki da lafiya" ya faɗa yana kara sassauta murya

Da kyar Baffah ya kar ɓa, yana shi mishi albarka yana cewa ,"Yaro kai ɗan wani gari ne tun da kazo bamu samu mun tattauna ba"

"Baffah ni da Iyaye na ma zauna garin abuja ne, kuma a cen nake aiki, sana'a ta zane wato Arc............

Bai karasa ba sai naji Baffah yayi saurin cewa Arctecture?

Ahmad yayi saurin amsa masa da ,"Eh Arctect ne ni da Mahaifi na, Wanda ma muna da campanin zana abubuwa da dama"

Baffah yayi saurin cewa ,"Allah ya taimaka Ahmad, amma kwakwalwata tana son tunano min da wasu abubuwa da nayi a rayuwa ta da jimawa nima ina ji a jikina kamar nayi zane,.........Baffah ya tsagai ta.

Ahmad ya na tsugunne sai da ya ɗago kai da sauri ya kalli Baffah Ya ce,"Da gaske Baffah shin miye sunan ka na asali wai?

"Anna ganin abin na su na yin zurfi sai ta kaste su da cewa "*Baffah*" Baffah shine asalin sunan sa".

Ahmad karar wayar sa ya sashi yin shiru ran shi na daɗa dagule wa, ya duba wayar yaga still Mummy ce, ita in ta fara kiran waya shikenan ta dunga kenan, ita ce dama take ta kiran sa akan lafiya taga yayi kwana biyi bai dawo ba, sannan ta faɗa masa cewa idan har bai dawo yau ba to zai gansu a kaduna gobe, ko a ina suke zasu nemo sa, Dole ta sa yau zai kama hanyar Abuja da daddaren nan.

Ya ce,"Baffah Iyaye na suna son gani na, yan zun nan zan kama hanya, amma bayan kwana biyu zan dawo ko dankuwa an sallame ku zan same ku a gida...ya tsagaita.

______________________________________

ALMAJIRA SABON SALO littafine da ni ke da yakinin duk wani masoyi na idan ya karanta shi ba zai yi dana sanin karantawa ba.

Na san you guys will always patronize me and stand by me saboda duk mai son ka yake kaunar ka kuma yake amfana da kai, Na san ba zai ji kyashin kai ma ka karu da shi ba.

200 naira kacal zaku biya dan samun shiga whatsapp group din da zan rinka posting in Allah ya yarda.

3119736620
Fadila Ibrahim
First bank
Sannan ku turo da shedar biya ta wannan layin

07031086858

Continue Reading

You'll Also Like

8K 591 37
GABA DA GABANTA (Aljani ya taka wuta)😂 don't miss it, akwai cakwakiya
1.5K 123 26
Makahon so, shine lokacin da sashe ɗaya ya makance akan soyayyar ɗaya sashen. Gurgun so, shine son da sashe ɗaya yake mutuwar son ɗaya sashen amma ba...
2.9K 315 67
labari akan yadda rayuwa ta kan sauya wa Dan Adam.yadda abubuwa sukan juya su rikice su firgice har mutum yaga kamar shi kadai aka tsana,ko kuwa ya m...
7.2K 263 25
labarin soyayya mai ciki da darussa iri iri mai masu tsayawa a zuci..masoyane suke nuna ma juna tsana marar adadi rana d'aya lokaci d'aya kiyaiyar ta...