BIBIYATA YAKEYI ( WAYE SHI?)

Від zeeyybawa

2.3K 172 19

BIBIYARTA YAKEYI WAYE SHI? A'ina yake? Meyasa yake Bibiyarta? Більше

BABI NA DAYA
BABI NA UKU
BABI NA HUDU
BABI NA BIYAR
BABI NA SHIDA
BABI NA BAKWAI
ADVERT
Advert
Advert
Advert
BABI NA TAKWAS
BABI NA TARA
BABI NA GOMA
20
BIBIYATA YAKEYI

BABI NA BIYU

125 13 1
Від zeeyybawa


*BIBIYATA YAKEYI*
_(WAYE SHI?)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


  BY
     ZAYNAB BAWA

Assalamu alaikum
Ina kuke manyan mata?

Matanda suka san kansu, Suka amsa sunansu Mata, Amarya, Uwar gida shin kin taba using kayan *ROYAL EXQUISITE* kuwa??? Idan kin taba to barkanki danna tabbata kin fita daban da sauran mata, idan Baki taba ba kuwa lallai an barki a baya kuma kin dade kina cutar kanki da mijinki, Domin samun kayanmu masu kyau da inganci zaku iya tuntubarmu domin munada Kayan mata masu kyau da inganchi Kamar su
Virgin again
Tightening pills
Turaren ban mamaki
Sweetness agents
Wetness agents
Infection set da sauransu
Domin ƙarin bayani ku tuntubemu ta wannan numbern
08030644073

Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
*Y'AR FARI*
*YARIMA FAYAD* paid 200
*ƘADDARAR RAYUWA*

*Assalamu alaikum barkanmu da warhaka*

INA MASOYANA WANDA SUKA KARANTA LITTAFIN BIBIYATA AKEYI 🤝 WANNAN SALON SHEKARAR 2017 NE, YA KUKAJIN LABARIN? NASAN DA YAWANKU BAKU MANTASHI BA!

TO MASOYA GANI NAN NA KAWO MUKU WANI ZAZZAFAN LABARI MAI CIKE DA SALO KALA KALA!!! WANNAN SABON LABARI SHINE BIBIYATA YAKEYI(WAYESHI).

WANNAN SALON 2023 NE! SABON LABARI SABON SALON LITTAFI DABAN YAKE DANA BAYA BIBIYATA AKEYI!

BIBIYATA YAKEYI(WAYESHI) PAID BOOK NE BA FREE BA.🤝



PAGE 2

     Bayan fitarmu daga ɗakin gabaki ɗaya, Mama ta dubi Anty ganin yanda jikinta yayi sanyi duk sai taji babu dadi, cikin karfafa guiwa Mama tace.

"Kiyi hakuri idan wannan abun ne yaci ace yanzu ya zame miki jiki ya daina damunki gabaki ɗaya. Kuma ina da tabbacin wata rana zai shude ya zama labari kamar hakanma bai taba faruwa ba."

Saida Anty tayi murmushi mai ciwo sannan tace.

"Mama dole na damu domin ba yanzu bane lokacin damuwar, lokacin da abun zai zama wani iri nakeji, ina matukar tausayawa yarana dan sune kananu acikin gidan nan. Kuma sune wanda basu da farin jini, inaji ajikina ba zasu taba son yaran da na haifa ba. Yau idan akace babu ni yarana basu da makama tunda sune manya sune danginsu kadai kuma basa son su, gara ke koda yaranki basu tasa sosai ba amma kina da dangi wanda zasu iya rike miki yaranki kuma basajin haushin naki kamar yanda suke jin haushin nawa yaran, ni ba uwa ko uba gareni ba bare nayi tunanin ko babu ni nabar wanda zasu kulamin dasu." Mama ta katseta da fadin.

"Haba Habiba wai me yasa kike haka ne? Duk me ya kawo wannan zancen? In Allah yayarda Allah zai barmu akan yaran mu har zuwa girman su." Anty ta share kwallar data zubo mata tace,

"Shikenan na daina yanzu kishiga ki fadawa babansu jikin Hussainin danni idan na shiga sai ya zama wani abun daban."

Mama ta mike ta fice daga dakin. Ganin takalma a kofar dakin Baba ya sanya ta tsagaita kamar bazata shigaba sai kuma tayi sallama ta shiga. Dukkan su wanda suke palourn suka amsa mata sallamar,

Kujerar dake kusa da ta Baba ta karasa ta zauna tana karewa yan mata guda biyu dake zaune kasa kan carfet kallo fuskarta dauke da fara'a tace.

"Ikon Allah wa nake gani kamar Fadeelah da Ayusha? Lallai sun girama masha Allah shekaru da yawa ba'a hadu ba." Baba yace.

"Sune kuwa, shekaru dayawa kam, yanzu nake niyyar na aika a kirawoku gabaki daya domin yayansu yazo min da wani zance." Mama tace.

"Toh ai gamu bari nakira Habiban tana tare da Hussaini yanzu Mamee ta dawo dashi daga makaranta zazzabi ya rufe shi."

"Allah ya sauwake." Shine abunda Baba ya fada sannan ya dubi Fadeela da Aysha yace.

"bakuga Mamanku bane ba? Ba zaku gaidata ba?" Fadeela ce tafara faɗin.

"Ina wuni?" Mama ta amsa fuska a sake sai Aysha ma tabi bayanta suka gaisheta. Mikewa tayi ta fita ta kirawo Aunty, Minti biyu gabaki dayansu suka shigo tare,

Itama sai da Baba yayi magana kafin suka gaida ta hakanma murya adakile kamar wanda bakin su ke ciwo. Bata batawa kanta lokaci wajan amsawa ba dan yanayin yanda sukayi mata gaisuwa gabaki daya babu da'a a ciki. Baba ya jijjiga kai kawai yanajin babu dadi bai san yaushe al'amarin gidansa zai gyaru ba, yana fata Allah ya kawo masa mafita a wannan lamari kafin mutuwarsa idan ba haka ba zai mutu da bakin ciki da fargabar tarwatsewar ahalinsa.

Ya ɗauki lokaci a haka saida gabaki daya wajan suka fahimci abunda ya faru bai yi masa dadi ba. Anty sai taji babu dadi data san halin da zai shiga kenan data amsa gaisuwar ko a yaya suka yi ta,

Yadauki lokaci ahaka sannan yayi gyaran murya gabaki ɗayan su suka fuskance shi sai da yai nisa sannan yace,

"Hajiya Indo (Mama) Habiba (Aunty) ga Fadeela da Aysha daga yau in sha Allahu sun dawo gidannan da zama gabaki ɗaya, anan zasu ci gaba da karatunsu har Allah ya fito musu da miji suyi aure. Na baku amanar su ina so kuji ajikinku kamar ƴaƴan da kuka haifa ne duk da cewa banda shakku akanku zaku kula dasu yanda ya dace kawai tunasarwa ce nayi. Idan laifi suka yi kamar yanda kuke yiwa kanwarsu Mamee hukunci haka suma zaku yi musu." Mama tace,

"Insha Allahu ai abunda yayi Mamee shi yayi su Fadeela Allah ya bamu ikon rike amana."

"Amin" Baba ya amsa bai jira yaji maganar Aunty ba dan yasan idan Mama ta amince itama ta amince. Anty cikin ranta ji takeyi kamar tafito ta gaya masa bazata iya rike wannan amanar ba dan ga dukkan alamu yaran dan ita sukazo aransu, amma bazata iya ba saboda bata san halin da zai shiga ba har indai ta fadi hakan. Ita ta fara mikewa tace,

"Zan koma wajan Hussaini na barshi shi daya." Baba yace.

"Toh  nima yanzu zan shigo na duba jikin nasa." Ya dubi Mama yace,

"Kuje ki nuna musu yanda zasu zauna idan kin nuna musu ki dawo." Amsawa tayi ta tashi tayi waje, bayan tafita Baba ya dube su yace,

"Ku dauki kayanku kuje wajan Hajiya Indo  zata nuna muku daki sannan dan Allah bana son tashin hankali, ku girmama su gabaki ɗayan su mahaifanku ne." Suka amsa da.

"Toh." Sannan suka fice. Yaya Ahmad wanda yake zaune a wajan tunda aka fara bai yi magana ba sai bayan sun fita ya yi masa sallam ya fita."

——————

Ina zaune a aji amma gabaki daya na kosa lokacin tashi yayi na dawo gida dan son sanin halin da Hussaini yake ciki ga kuma tambayoyin da suke raina fall inaji yau gabaki daya sai na sauke su akan Aunty, kuma ina addu'ar kowacce tambaya idan nayi tabani amsar ta.

Ana tashi kuwa jikina har bari yake na dauki Qur'ani na nafice na tattara kan kannena sannan muka yi gida. Ina shiga na riski wani labarin daban da murnata na fito daga dakin Mama zuwa dakin da aka sauke su, sun amasani babu yabo babu fallasa amma ko ajikina danni dama zaman kadaici ni kadai agidan ya isheni. Hira nake yi musu suna amsawa sai da aka kira sallar asubahi sannan na fice dan yin Sallah. Dake dakin da aka sauke su ciki ne da falo harda bandaki ya sanya tunda suka shiga basu fito ba sai da Mama ta aikani na kirawo su muci abinci. Naje na sanar dasu suka shaida min na kawo musu shi nan kamar yanda aka yi musu jiya. Mama tace lallai su fito aci dasu naje sanar musu. Sai da suka dauki lokaci kafin suka fito basu wani tsaya sunci abincin ba suka koma ciki yanzu nikam jikina ya fara sanyi yanda suke mu'amalantarmu kamar ba yan uwansu ba. Hakan yasa nima banbi takansu ba dare nayi na shige dakin Aunty.

"Anty waini menene yasa Yaya yake miki haka?" Na jefa mata tambaya,

"Ba Yaya kadai ba dukkan su haka suke min." Ta bani amsa.

"Amma Anty na Yayan yafi yawa shifa ko yaranki baya kulawa."

"Hmm Mamee kenan sarkin tambaya, kwanaki da kika tambayeni bana fada miki dalilin ba?"

"Eh kin fada amma Anty jikina yana bani kamar ba wannan dalilin bane kadai yasa yake miki haka ta iya yiwuwa akwai wani dalilin daban tunda kinga mu yana mana magana amma baya yiwa su Meema."

Sai da ta zuba min idanuwa kamar zatace wani abun saita fasa, afili tace.

"Mamee kenan sarkin wayo, kema bakya jin dadi yanda yake nuna musu koh?" Gyada kai nayi tayi murmushi tace.

"Shikenan tunda shi baya son su ke ai kina sonsu kiyi karatu sosai ki zama gatansu gabaki ɗaya."

Murmushi kawai nayi amma tabbas nasan akwai abunda Anty ke boyewa saboda ga dukkan alamu Yaya ba haushi daya yake nunawa akanta ba. Har zuciyarsa yake jin haushinta da abunda ta haifa.

Sallama nayi mata na shige dakin Mama na samu ta kwanta amma ba bacci na keyi ba. Nabi gadon nima na kwanta.

"Mama!" Na kira sunanta.

"Uhm" Ta amsa.

"Mama wai menene a tsakanin Yaya da Anty yasa yake jin haushinta?" Kamar bazata amsa niba sai can naji  tace,

"Ke ina ruwanki da kike son sani?"

"Mama ni bana jin dadin yanda al'amura suke gudana a gidan nan, idan inada hali dana gyara."

"Allah yabaki halin wata rana ki gyara. Amma kidaina bibiyar abunda ya hada Antynku da yayyunku banaso." Amin nace sannan nadaura da faɗin.

"Kwanaki Anty ta taba fadamin dalilin, Amma ni gani nakeyi kamar wannan dalilin yayi kadan a tsanar da Yaya ya ke yi mata inaji kamar akwai wani abun." Mama tace.

"Menene tace miki dalilin?."

PAID BOOK
Littafin BIBIYATA YAKEYI (WAYE SHI) na kudine ki biya Naira Dari uku 300 Domin kisha karatunki hankaki kwance,
account 0003075326
Zainab  m Bawa JAIZ BANK shaidar biya Ta 08161146563 da zarar kin biya Hankli kwance  zaki samu damar karanta wannan labarin ku shigo daga ciki kar ayi babu ku domin wannan
tafiyace wanda salonta da tsarinta ya bambamta da ko wace irin tafiya karki bari ayi babu ke."
Idan Kuma kina bukatar Aringa tura miki pc kullum Dari hudu 400 kacal zaki biya batareda an Sanyaki cikin group ba zaizo ya sameki har yanda kike." A

✔️ote
Follow
Comment
Share please

To be continued

Zaynab Alabura 💕

*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡

Продовжити читання

Вам також сподобається

Doors open. Від ash

Фанфіки

587K 9K 87
A text story set place in the golden trio era! You are the it girl of Slytherin, the glue holding your deranged friend group together, the girl no...
1.3M 58.1K 104
Maddison Sloan starts her residency at Seattle Grace Hospital and runs into old faces and new friends. "Ugh, men are idiots." OC x OC
792K 29.5K 105
The story is about the little girl who has 7 older brothers, honestly, 7 overprotective brothers!! It's a series by the way!!! 😂💜 my first fanfic...
1.1M 20K 44
What if Aaron Warner's sunshine daughter fell for Kenji Kishimoto's grumpy son? - This fanfic takes place almost 20 years after Believe me. Aaron and...